ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kafa Jam’iyyar Adawa: Atiku Da Wasu Sanatoci Sun Sake Sabon Yunkuri

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Atiku

‘Yan adawa na shirin kafa sabuwar jam’iyyar domin kwace mulki daga hannun jam’iyyar APC a 2027.

Gabanin 2027, majiyoyi sun bayyana cewa dan takarar shugaban kasa na PDP a zaben da ya gabata, Alhaji Atiku Abubakar, ya hada kai da wasu ‘yan majalisa domin kafa sabuwar jam’iyya.

  • Uwargidan Shugaban Kasa Ta Bude Makaranta Ga Matan Da Aka Kora A  Manyan Makarantu A Bauchi
  • Kayayyakin Wasanni Kirar Kasar Sin Sun Samu Yabo A Gasar Wasannin Afirka Ta 13

Sun kara da cewa Atiku ya kaddamar da tawaga mai karfi domin jagorantar kafa sabuwar jam’iyyar adawa da za ta fara aiki kafin zaben 2027, inda yake tunanin cewa jam’iyyar za ta iya kwace mulki daga wurin APC.

ADVERTISEMENT

Majiyoyin sun ce tsohon mataimakin shugaban kasan ya hada kai da tsohon gwamnan Zamfara, Abdulaziz Yari, wanda ya nemi shugabancin majalisan dattawa bai samu ba.

Haka kuma shugaban kungiyar sanatocin arewa (NSF), Abdul Ningi, zai shiga cikin wannan tawaga domin ya kasance sojon gona a zauren majalisa wajen tabbatar da sabuwar jam’iyyar.

LABARAI MASU NASABA

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

A cewar masu sharhi kan al’amurar siyasa, wannan lamari na iya mammaita abun da ya faru a 2013, inda wasu gwamnoni da ‘yan majalisa suka yi wa PDP tawaye tare da yin aiki tare wajen kafa jam’iyyar APC wanda ta kwace mulki.

An dai kafa APC ne a watan Fabrairun 2013, sakamakon kwawancen jam’iyyu da suka hada da CAN, CPC, ANPP, APGA da kuma wani bangare na sabuwar PDP.

Atiku yana daga cikin wadanda suka jagoranci kafa jam’iyyar APC, inda ya tsaya takarar shugaban kasa a 2014, sai dai Muhammadu Buhari ya kayar da shi tun a zaben fitar da gwani.

Ya dai sake dawowa PDP, inda ya tsaya takara a 2019, sai dai kuma ya sha kaye a hannun Buhari. Sannan a zaben bara kuma, Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya kayar da shi.

Majiyoyin sun ce Atiku da sauran abokanansa suna kokarin maimaita abun da ya faru a 2013 na kafa sabuwar jam’iyyar kuma har da kwace mulki.

Ya ce, “Mun yi nisa kan wannan yarjejeniya. Mun tabbatar da cewa kasar nan tana cikin mummunan hali fiye da na 2014 lokacin mulkin Goodluck Ebele Jonathan, shi ya sa muka yi wannan shiri na kafa sabuwar jam’iyyar domin kwace mulki daga wurin Tinubu.”

Wani sanata daga kudu ya ce mafi yawancin abokansa suna sane da yin shiri domin mulki ya dawo arewa idan har suka samu nasarar raunata gwamnatin Tinubu a 2027.

Ya ce, “Mun san irin shirin da ake yi. Muna kallon su ne kwai. Suna ta yin siyasa wajen kawo rudani a jam’iyyarmu wanda za a ruruta wutar fada a tsakaninmu da bangaren shugaban kasa wajen tafiyar da harkokin gwamnati.

Ningi, wanda yake wakiltar Bauchi ta tsakiya a majalisar dattawa ya shaida wa sashin Hausa na BBC cewa sanatocin arewa za su yaki shugaban kasa.

Ya ce, “Lallai ba za su yaki gwamnati ba kamar yadda ‘yan adawa ke yi ba. Amma dai wannan irin sakamako ne ya dace da gwamnatin da muke da ita. Wadannan shugabannin da suke gallaza mana ba su muka zaba ba.

“Mun kawo bambance-bambancen addini da kabilanci wajen gudanar da sha’anin gwamnati. Sun kawo farfagandar cewa ba za a amince a kara bai wa Bahaushe ko Fulani shugabanci ba, saboda ba a samun zaman lafiya.

“Idan aka duba da idon basira za a ga cewa mafi yawan ‘yan adawa sun fito ne daga yankin arewa maso gabas da kuma arewa maso yamma. Amma an ki amincewa mu zama shugabannin ‘yan adawa a zauren majalisar dattawa ba.

“Wannan shi ne daya daga cikin dalilan da muka ce za mu duba mu gani kan abubuwan da ke faruwa a karkashin kungiyar sanatocin arewa, wanda nake shugabanci a yanzu haka,” in ji shi.

Atiku
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

May 15, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Hadakar ‘Yan Adawa Ta Rushe Yayin Da Tikitin Takarar Shugaban Kasa Ya Raba Kan Shugabannin ADC

May 9, 2026
Next Post
Kabilu Biyar Mafiya Tsadar Aure A Nijeriya

Kabilu Biyar Mafiya Tsadar Aure A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.