ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kafa Jam’iyyar Adawa: Atiku Da Wasu Sanatoci Sun Sake Sabon Yunkuri

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Atiku

‘Yan adawa na shirin kafa sabuwar jam’iyyar domin kwace mulki daga hannun jam’iyyar APC a 2027.

Gabanin 2027, majiyoyi sun bayyana cewa dan takarar shugaban kasa na PDP a zaben da ya gabata, Alhaji Atiku Abubakar, ya hada kai da wasu ‘yan majalisa domin kafa sabuwar jam’iyya.

  • Uwargidan Shugaban Kasa Ta Bude Makaranta Ga Matan Da Aka Kora A  Manyan Makarantu A Bauchi
  • Kayayyakin Wasanni Kirar Kasar Sin Sun Samu Yabo A Gasar Wasannin Afirka Ta 13

Sun kara da cewa Atiku ya kaddamar da tawaga mai karfi domin jagorantar kafa sabuwar jam’iyyar adawa da za ta fara aiki kafin zaben 2027, inda yake tunanin cewa jam’iyyar za ta iya kwace mulki daga wurin APC.

ADVERTISEMENT

Majiyoyin sun ce tsohon mataimakin shugaban kasan ya hada kai da tsohon gwamnan Zamfara, Abdulaziz Yari, wanda ya nemi shugabancin majalisan dattawa bai samu ba.

Haka kuma shugaban kungiyar sanatocin arewa (NSF), Abdul Ningi, zai shiga cikin wannan tawaga domin ya kasance sojon gona a zauren majalisa wajen tabbatar da sabuwar jam’iyyar.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

A cewar masu sharhi kan al’amurar siyasa, wannan lamari na iya mammaita abun da ya faru a 2013, inda wasu gwamnoni da ‘yan majalisa suka yi wa PDP tawaye tare da yin aiki tare wajen kafa jam’iyyar APC wanda ta kwace mulki.

An dai kafa APC ne a watan Fabrairun 2013, sakamakon kwawancen jam’iyyu da suka hada da CAN, CPC, ANPP, APGA da kuma wani bangare na sabuwar PDP.

Atiku yana daga cikin wadanda suka jagoranci kafa jam’iyyar APC, inda ya tsaya takarar shugaban kasa a 2014, sai dai Muhammadu Buhari ya kayar da shi tun a zaben fitar da gwani.

Ya dai sake dawowa PDP, inda ya tsaya takara a 2019, sai dai kuma ya sha kaye a hannun Buhari. Sannan a zaben bara kuma, Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya kayar da shi.

Majiyoyin sun ce Atiku da sauran abokanansa suna kokarin maimaita abun da ya faru a 2013 na kafa sabuwar jam’iyyar kuma har da kwace mulki.

Ya ce, “Mun yi nisa kan wannan yarjejeniya. Mun tabbatar da cewa kasar nan tana cikin mummunan hali fiye da na 2014 lokacin mulkin Goodluck Ebele Jonathan, shi ya sa muka yi wannan shiri na kafa sabuwar jam’iyyar domin kwace mulki daga wurin Tinubu.”

Wani sanata daga kudu ya ce mafi yawancin abokansa suna sane da yin shiri domin mulki ya dawo arewa idan har suka samu nasarar raunata gwamnatin Tinubu a 2027.

Ya ce, “Mun san irin shirin da ake yi. Muna kallon su ne kwai. Suna ta yin siyasa wajen kawo rudani a jam’iyyarmu wanda za a ruruta wutar fada a tsakaninmu da bangaren shugaban kasa wajen tafiyar da harkokin gwamnati.

Ningi, wanda yake wakiltar Bauchi ta tsakiya a majalisar dattawa ya shaida wa sashin Hausa na BBC cewa sanatocin arewa za su yaki shugaban kasa.

Ya ce, “Lallai ba za su yaki gwamnati ba kamar yadda ‘yan adawa ke yi ba. Amma dai wannan irin sakamako ne ya dace da gwamnatin da muke da ita. Wadannan shugabannin da suke gallaza mana ba su muka zaba ba.

“Mun kawo bambance-bambancen addini da kabilanci wajen gudanar da sha’anin gwamnati. Sun kawo farfagandar cewa ba za a amince a kara bai wa Bahaushe ko Fulani shugabanci ba, saboda ba a samun zaman lafiya.

“Idan aka duba da idon basira za a ga cewa mafi yawan ‘yan adawa sun fito ne daga yankin arewa maso gabas da kuma arewa maso yamma. Amma an ki amincewa mu zama shugabannin ‘yan adawa a zauren majalisar dattawa ba.

“Wannan shi ne daya daga cikin dalilan da muka ce za mu duba mu gani kan abubuwan da ke faruwa a karkashin kungiyar sanatocin arewa, wanda nake shugabanci a yanzu haka,” in ji shi.

Atiku
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
Tambarin Dimokuradiyya

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 11, 2026
Next Post
Kabilu Biyar Mafiya Tsadar Aure A Nijeriya

Kabilu Biyar Mafiya Tsadar Aure A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.