ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, November 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Maka Shi Gaban Kotu Bisa Satar Karafan Naira Miliyan 5

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Kotu

LABARAI MASU NASABA

An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

ADVERTISEMENT

An gurfanar da wani mutum mai suna Okwudili Orji mai shekaru 42 a gaban kotu bisa zargin satar sandunan karafa da kudinsu ya kai Naira miliyan 5 a yankin Ejigbo da ke Jihar Legas.

An gurfanar da Orji ne a kan tuhume-tuhume biyu da suka shafi sata a gaban babban alkalin kotun majistare Patrick Nwaka a kotun Majistare ta Yaba.

  • Sin Ta Bukaci Japan Da Kada Ta Yi Yunkurin Amfani Da Rahoton IAEA A Matsayin Izinin Zubar Da Dagwalon Ruwan Nukiliya A Cikin Teku
  • Ina Son Kara Aure, Ko Me Yake Kawo Matsaloli Tsakanin Kishiyoyi Da Yadda Za A Magance?

Dan sanda mai shigar da kara, Cyril Ejiofor, ya shaida wa kotun cewa laifukan da Orji ya aikata sun saba wa sashe na 314 da 287 na dokar laifuka ta Jihar Legas a shekarar 2015.

A wani bangare na tuhume-tuhumen, ya kara da cewa, “Kai Okwudili Orji, a cikin watan Satumba 2022, da misalin karfe 9 na safe, a mahadar Bucknor, Ejigbo, Jihar Legas, a gundumar Majistare ta Legas, ka yi damfara da sandunan karfe da kudinsu ya kai Naira miliyan 5, daga wani mutum Uzoma Patrick, da ya zama shi ne wakilinku, bayan ka san damfara ce, don haka laifin da ka aikata zai kai ga hukunka shi a karkashin sashe na 314 na dokar laifuka ta Jihar Legas na shekarar 2015.”

Lauyan da yake kare wanda ake kara, N.C. Okparauwa, ya roki kotun da ta amince da wanda yake karewa a ba da belinsa a mafi saukin yanayi domin ya samu sukunin kara bincke.

A cewarsa bai ga wata hujja a kan karar da masu gabatar da kara suka gabatar ba, alkalin kotun ya amince wanda ake kara ya bayar da belinsa a kan kudi Naira 1 tare da mutum biyu da za su tsaya masa.

Ya ba da umarnin cewa wadanda za su tsaya masa dole su zama ma’aikata ne masu daraja a Jihar Legas ba masu sana’o’in dogaro da kai ba, sannan kuma dole ne su gabatar da takardar shaidar biyan haraji na shekaru uku da kotu za ta iya tantancewa.

Mai shari’a Nwaka ya dage sauraron karar har zuwa ranar 28 ga Agusta, 2023, domin ci gaba sauraro.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa
Kotu Da Ɗansanda

An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

November 8, 2025
An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi
Kotu Da Ɗansanda

An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

November 8, 2025
Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi
Kotu Da Ɗansanda

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

October 4, 2025
Next Post
Gwamnatin Gombe Ta Bukaci Jami’an Lafiya Da Su Kara Kwazo Wajen Yaki Da Cutar Sida

Gwamnatin Gombe Ta Bukaci Jami'an Lafiya Da Su Kara Kwazo Wajen Yaki Da Cutar Sida

LABARAI MASU NASABA

Ronaldo Na Fuskantar Dakatarwar Wasanni Biyu Bayan Samun Jan Kati

Ronaldo Na Fuskantar Dakatarwar Wasanni Biyu Bayan Samun Jan Kati

November 14, 2025
Editoci Sun Yi Gargadi Kan Rushewar Kafofin Yada Labarai Sakamakon Matsin Tattalin Arziki

Editoci Sun Yi Gargadi Kan Rushewar Kafofin Yada Labarai Sakamakon Matsin Tattalin Arziki

November 14, 2025
Kotu Ta Yanke Wa Mutum 4 Hukuncin Kisa Kan Kashe Wani Makanike A Kano

Kotu Ta Yanke Wa Mutum 4 Hukuncin Kisa Kan Kashe Wani Makanike A Kano

November 14, 2025
Abin Da Ya Sa NPA Ta Yi Hadaka Da ‘Snake Island Port’ -Dakta Dantsoho

Abin Da Ya Sa NPA Ta Yi Hadaka Da ‘Snake Island Port’ -Dakta Dantsoho

November 14, 2025
Shugaban NPA Ya Bukaci A Yi Hadaka Domin Cin Gajiyar Albarkatun Fannin Sufurin Afirka

Shugaban NPA Ya Bukaci A Yi Hadaka Domin Cin Gajiyar Albarkatun Fannin Sufurin Afirka

November 14, 2025
Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci

Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci

November 14, 2025
Jan Aikin Da Ke Gaban Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya

Jan Aikin Da Ke Gaban Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya

November 14, 2025
Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

November 13, 2025
Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

November 13, 2025
Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

November 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.