• English
  • Business News
Monday, November 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Samu Hauhawar Farashi Mafi Muni A Nijeriya

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Farashi

LABARAI MASU NASABA

Mayar Da Martani Kan Barazanar Amurka Ga Nijeriya: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yaba Wa Kwankwaso 

NARD Ta Yi Fatali Da Iƙirarin Gwamnatin Tarayya Na Ba Ta ₦43bn, Kuma Yajin Aiki Na Nan

Hauhawan farashin kayan masarufi na ci gaba da karuwa fiye da kima, inda ya haura zuwa kashi 28.92 a watan Disamban 2023, wanda hakan na nuni da cewa a sama da shekaru 24 Nijeriya ba ta taba fuskantar irin wannan hauhuwar farashin ba.

A cikin rahoton da hukumar kiddigga ta kasa (NBS) ta fitar a makon nan, ta ce zuwa watan Disamban shekarar da ta gabata, hauhawar farashi ya karu zuwa kashi 28.92 daga kashi 28.20 a watan Nuwamba 2023.

  • Hadin Abincin Kajin Gidan Gona Masu Saurin Girma
  • Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Gana Da Tawagar Amurka Ta Rukunin Ayyukan Hada-hadar Kudi Na Sin Da Amurka 

Rahoton ta ce, hakan ya nuna an samu karuwa hauhawar farashi da tazarar 0.72 daga watan Nuwamban kawai.

Hukumar kididdiga ta ce hakan ta faru ne sanadin tsadar farashin abinci, lamarin da kuma ya ta’azzara tsadar rayuwa da karin matsin lamba kan babban bankin Nijeriya da ya yi wajen kara kudin ruwa.

Hukumar ta ce idan aka duba kididdigar hauhawa a Disamban 2022 da ya kai zuwa 21.24 kuma aka kwatanta da na shekarar 2023, za a iya cewa duk shekara Nijeriya na samun karuwar hauhawar farashi.

 Hukumar ta ci gaba da cewa hauhawar farashin abinci zuwa Disamban 2023 ya kai kaso 33.93 cikin 100 a shekara guda, kaso 10.18 na hauhawa idan aka kwatantanta da na Disamban shekarar 2022 mai kashi 23.75 cikin dari.

Ta ce, hauhawar farashin ya faru ne sakamakon tsadar kayan abinci irin su buredi, man fetur da man girki, dankali, doya, kayan hatsi, kifi, nama, kayan marmari, madara, kwai da dai sauran kayan abincin da ake amfani da su a Nijeriya.

LEADERSHIP Hausa ta labarto cewa al’ummar Nijeriya na ci gaba da nuna damuwarsu kan yadda kayan masarufi ke tashin gwauron zabi, lamarin dai ya kara jefa jama’an kasar cikin matsatsi da kuncin rayuwa. Duk da cewa gwamnatin Bola Ahmad Tinubu na ikirarin nemo hanyoyin fita daga matsatsin da ake ciki musamman na tattalin arziki da sauransu.

Masharhanta irinsu, Dabid Omojomolo na cibiyar ‘Caital Economics’ sun yi hasashen cewa hauhawar farashi a Nijeriya za ta iya kai wa har kashi 30 nan da karshen wata uku na farko wannan shekara.

 A cikin watan Mayu ne Shugaba Tunubu ya bijiro da gyare-gyare mafi karfin hali a cikin shekaru gomma bayan ya yi watsi da manufar cire tallafin man fetur, darajar kudin Nijeriya kuma ta karye a kokin farfado da bunkasar tattalin arziki.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa
Manyan Labarai

Mayar Da Martani Kan Barazanar Amurka Ga Nijeriya: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yaba Wa Kwankwaso 

November 3, 2025
Likitoci
Labarai

NARD Ta Yi Fatali Da Iƙirarin Gwamnatin Tarayya Na Ba Ta ₦43bn, Kuma Yajin Aiki Na Nan

November 3, 2025
Kano
Manyan Labarai

Kano Ta Amince Da Naira Biliyan 8.2 Don Ayyukan ilimi, Samar Da Ruwa, Da Makamashi

November 3, 2025
Next Post
‘Yansanda Sun Kubutar Da Mutum 3 Daga Harin ‘Yan Fashin Daji A Jihar Kaduna

'Yan sanda Sun Cafke Waɗanda Ake Zargi Da Satar Mutane A Abuja

LABARAI MASU NASABA

2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa

Mayar Da Martani Kan Barazanar Amurka Ga Nijeriya: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yaba Wa Kwankwaso 

November 3, 2025
Likitoci

NARD Ta Yi Fatali Da Iƙirarin Gwamnatin Tarayya Na Ba Ta ₦43bn, Kuma Yajin Aiki Na Nan

November 3, 2025
Kano

Kano Ta Amince Da Naira Biliyan 8.2 Don Ayyukan ilimi, Samar Da Ruwa, Da Makamashi

November 3, 2025
Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

November 2, 2025
Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

November 2, 2025
Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

November 2, 2025
Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

November 2, 2025
Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

November 2, 2025
Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

November 2, 2025
Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

November 2, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.