• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Samu Hauhawar Farashi Mafi Muni A Nijeriya

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
An Samu Hauhawar Farashi Mafi Muni A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hauhawan farashin kayan masarufi na ci gaba da karuwa fiye da kima, inda ya haura zuwa kashi 28.92 a watan Disamban 2023, wanda hakan na nuni da cewa a sama da shekaru 24 Nijeriya ba ta taba fuskantar irin wannan hauhuwar farashin ba.

A cikin rahoton da hukumar kiddigga ta kasa (NBS) ta fitar a makon nan, ta ce zuwa watan Disamban shekarar da ta gabata, hauhawar farashi ya karu zuwa kashi 28.92 daga kashi 28.20 a watan Nuwamba 2023.

  • Hadin Abincin Kajin Gidan Gona Masu Saurin Girma
  • Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Gana Da Tawagar Amurka Ta Rukunin Ayyukan Hada-hadar Kudi Na Sin Da Amurka 

Rahoton ta ce, hakan ya nuna an samu karuwa hauhawar farashi da tazarar 0.72 daga watan Nuwamban kawai.

Hukumar kididdiga ta ce hakan ta faru ne sanadin tsadar farashin abinci, lamarin da kuma ya ta’azzara tsadar rayuwa da karin matsin lamba kan babban bankin Nijeriya da ya yi wajen kara kudin ruwa.

Hukumar ta ce idan aka duba kididdigar hauhawa a Disamban 2022 da ya kai zuwa 21.24 kuma aka kwatanta da na shekarar 2023, za a iya cewa duk shekara Nijeriya na samun karuwar hauhawar farashi.

 Hukumar ta ci gaba da cewa hauhawar farashin abinci zuwa Disamban 2023 ya kai kaso 33.93 cikin 100 a shekara guda, kaso 10.18 na hauhawa idan aka kwatantanta da na Disamban shekarar 2022 mai kashi 23.75 cikin dari.

Ta ce, hauhawar farashin ya faru ne sakamakon tsadar kayan abinci irin su buredi, man fetur da man girki, dankali, doya, kayan hatsi, kifi, nama, kayan marmari, madara, kwai da dai sauran kayan abincin da ake amfani da su a Nijeriya.

LEADERSHIP Hausa ta labarto cewa al’ummar Nijeriya na ci gaba da nuna damuwarsu kan yadda kayan masarufi ke tashin gwauron zabi, lamarin dai ya kara jefa jama’an kasar cikin matsatsi da kuncin rayuwa. Duk da cewa gwamnatin Bola Ahmad Tinubu na ikirarin nemo hanyoyin fita daga matsatsin da ake ciki musamman na tattalin arziki da sauransu.

Masharhanta irinsu, Dabid Omojomolo na cibiyar ‘Caital Economics’ sun yi hasashen cewa hauhawar farashi a Nijeriya za ta iya kai wa har kashi 30 nan da karshen wata uku na farko wannan shekara.

 A cikin watan Mayu ne Shugaba Tunubu ya bijiro da gyare-gyare mafi karfin hali a cikin shekaru gomma bayan ya yi watsi da manufar cire tallafin man fetur, darajar kudin Nijeriya kuma ta karye a kokin farfado da bunkasar tattalin arziki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Wani Jariri Ya Ɓata A Asibitin Waziri Gidado Da Ke Kano

Next Post

‘Yan sanda Sun Cafke Waɗanda Ake Zargi Da Satar Mutane A Abuja

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

9 hours ago
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

10 hours ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

11 hours ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

15 hours ago
Farashi
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

16 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

17 hours ago
Next Post
‘Yansanda Sun Kubutar Da Mutum 3 Daga Harin ‘Yan Fashin Daji A Jihar Kaduna

'Yan sanda Sun Cafke Waɗanda Ake Zargi Da Satar Mutane A Abuja

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.