• English
  • Business News
Friday, September 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Samu Manyan Sauye-Sauye Na Zamani A Jihar Xinjiang Cikin Shekaru 70

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 hours ago
in Daga Birnin Sin
0
An Samu Manyan Sauye-Sauye Na Zamani A Jihar Xinjiang Cikin Shekaru 70
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An yi gagarumin bikin murnar cika shekaru 70 da kafa jihar Xinjiang ta Uygur mai cin gashin kai a birnin Urumqi jiya Alhamis 25 ga watan Satumban nan, inda aka nuna wa duniya manyan nasarorin tarihin da jihar ta samu a cikin shekaru 70 da suka gabata, da kuma tabbatar da fifikon tsarin yankunan mabambantan kabilu masu zaman kansu na kasar Sin, gami da sakamako mai gamsarwa wajen aiwatar da manufofin tafiyar da harkokin Xinjiang da jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin ke yi a sabon zamani, tare kuma da shaida babbar niyyar da al’ummun jihar Xinjiang ke da ita a fannin raya jiha mai tsarin gurguzu, kuma irin ta zamani, karkashin jagorancin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin.

Kwarewar gwamnatin kasar Sin wajen tafiyar da harkokin mulki, abu ne da yake a bayyane, al’amarin da ya zama babban dalilin da ya kawo manyan sauye-sauye ga jihar ta Xinjiang. Sakamakon matukar kokarin da aka yi, an cimma nasarori da dama wajen dakile ’yan a-ware na wurin, har ta kai ba a samu wakanar ayyukan ta’addanci a tsawon shekaru da dama a yankin ba, al’amarin da ya tabbatar da kwanciyar hankali, da hadin-kan mabambantan kabilun yankin.

Zaman karko shi ne ke haifar da tabbaci ga ci gaban tattalin arziki. Ci gaba mai inganci da jihar Xinjiang ta samu, zai taimaka gaya ga ci gaban sauran kasashe, tare da samar da damarmakin zamanintar da yankin tsakiyar Asiya gami da sauran shiyyoyi.

A halin yanzu, kasar Sin na himmatuwa wajen zamanintar da kanta bisa salon musamman, yayin da aikin zamanintar da jihar Xinjiang ma ke cikin sabon mafari. Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya kafa alkiblar ci gaban Xinjiang a nan gaba, ciki har da raya sana’o’i na musamman, da bunkasa sabon karfin samar da hajoji da hidimomi masu karko, da raya al’adu da sana’ar yawon shakatawa tare, da inganta aikin kiyayewa, gami da farfado da tsarin muhallin halittu, da gaggauta raya muhimmin yankin tattalin arziki dake kan hanyar siliki da sauransu.

Gagaruman sauye-sauyen da jihar Xinjiang ta samu sun shaida cewa, yadda jama’a ke more rayuwa, hakkin dan Adam ne mafi muhimmanci. Babu shakka, jihar Xinjiang tana fuskantar makoma mai haske. (Murtala Zhang)

Labarai Masu Nasaba

Membobin Tawagar Koli Ta Sin Sun Ziyarci Jami’ai Da Gidajen Al’umma A Yankunan Jihar Xinjiang

Akwai Bukatar Sin Da Amurka Su Lalubo Hanya Mafi Dacewa Ta Tafiya Tare A Sabon Zamani


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Trump Ya Haramta Wa Jami’an Nijeriya Masu Cin Hanci Da Rashawa Shiga Amurka

Next Post

Gwamnati Ta Kafa Kwamitin Bincike A Kan Fashewar Wani Abu A Kaduna

Related

Membobin Tawagar Koli Ta Sin Sun Ziyarci Jami’ai Da Gidajen Al’umma A Yankunan Jihar Xinjiang
Daga Birnin Sin

Membobin Tawagar Koli Ta Sin Sun Ziyarci Jami’ai Da Gidajen Al’umma A Yankunan Jihar Xinjiang

15 minutes ago
Akwai Bukatar Sin Da Amurka Su Lalubo Hanya Mafi Dacewa Ta Tafiya Tare A Sabon Zamani
Daga Birnin Sin

Akwai Bukatar Sin Da Amurka Su Lalubo Hanya Mafi Dacewa Ta Tafiya Tare A Sabon Zamani

1 hour ago
Sin Da Amurka Na Da Damar Cimma Karin Nasarori Tare Muddin Sun Nacewa Alkawuran Da Suke Dauka
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Na Da Damar Cimma Karin Nasarori Tare Muddin Sun Nacewa Alkawuran Da Suke Dauka

22 hours ago
Sin Ta Sha Alwashin Hada Hannu Da MDD Wajen Aiwatar Da Shawarar GGI 
Daga Birnin Sin

Sin Ta Sha Alwashin Hada Hannu Da MDD Wajen Aiwatar Da Shawarar GGI 

23 hours ago
Salon Zamanantarwa Irin Na Kasar Sin: Hanya Ce Mallakar Kasar Sin Wacce Kuma Ta Sada Duniya
Daga Birnin Sin

Salon Zamanantarwa Irin Na Kasar Sin: Hanya Ce Mallakar Kasar Sin Wacce Kuma Ta Sada Duniya

1 day ago
An Yi Bikin Nune-Nunen Hotuna Da Bidiyo Na MDD Da Bikin Kade-Kaden Fina-Finai Masu Alaka Da Zaman Lafiya A Birnin New York
Daga Birnin Sin

An Yi Bikin Nune-Nunen Hotuna Da Bidiyo Na MDD Da Bikin Kade-Kaden Fina-Finai Masu Alaka Da Zaman Lafiya A Birnin New York

1 day ago
Next Post
Mazauna Kuyello A Jihar Kaduna Na Cikin Zullumin Bayyanar ‘Yan Ta’addar Ansaru

Gwamnati Ta Kafa Kwamitin Bincike A Kan Fashewar Wani Abu A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Membobin Tawagar Koli Ta Sin Sun Ziyarci Jami’ai Da Gidajen Al’umma A Yankunan Jihar Xinjiang

Membobin Tawagar Koli Ta Sin Sun Ziyarci Jami’ai Da Gidajen Al’umma A Yankunan Jihar Xinjiang

September 26, 2025
Akwai Bukatar Sin Da Amurka Su Lalubo Hanya Mafi Dacewa Ta Tafiya Tare A Sabon Zamani

Akwai Bukatar Sin Da Amurka Su Lalubo Hanya Mafi Dacewa Ta Tafiya Tare A Sabon Zamani

September 26, 2025
Mazauna Kuyello A Jihar Kaduna Na Cikin Zullumin Bayyanar ‘Yan Ta’addar Ansaru

Gwamnati Ta Kafa Kwamitin Bincike A Kan Fashewar Wani Abu A Kaduna

September 26, 2025
An Samu Manyan Sauye-Sauye Na Zamani A Jihar Xinjiang Cikin Shekaru 70

An Samu Manyan Sauye-Sauye Na Zamani A Jihar Xinjiang Cikin Shekaru 70

September 26, 2025
Trump Ya Haramta Wa Jami’an Nijeriya Masu Cin Hanci Da Rashawa Shiga Amurka

Trump Ya Haramta Wa Jami’an Nijeriya Masu Cin Hanci Da Rashawa Shiga Amurka

September 26, 2025
Gwamnatin Kogi Ta Yi Haɗin Gwuiwa Don Fara Fitar Da Amfanin Gona

Gwamnatin Kogi Ta Yi Haɗin Gwuiwa Don Fara Fitar Da Amfanin Gona

September 26, 2025
Me Ake Nufi Da Ado? 

Me Ake Nufi Da Ado? 

September 26, 2025
Murnar Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (3)

Murnar Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (3)

September 26, 2025
Goron Sallah

GORON JUMA’A

September 26, 2025
NECO 2025: Gwamnan Kano Ya Bayyana Bayanai Ba Daidai Ba

NECO 2025: Gwamnan Kano Ya Bayyana Bayanai Ba Daidai Ba

September 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.