• English
  • Business News
Saturday, October 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Samu Manyan Sauye-Sauye Na Zamani A Jihar Xinjiang Cikin Shekaru 70

by CGTN Hausa and Sulaiman
3 weeks ago
Xinjiang

An yi gagarumin bikin murnar cika shekaru 70 da kafa jihar Xinjiang ta Uygur mai cin gashin kai a birnin Urumqi jiya Alhamis 25 ga watan Satumban nan, inda aka nuna wa duniya manyan nasarorin tarihin da jihar ta samu a cikin shekaru 70 da suka gabata, da kuma tabbatar da fifikon tsarin yankunan mabambantan kabilu masu zaman kansu na kasar Sin, gami da sakamako mai gamsarwa wajen aiwatar da manufofin tafiyar da harkokin Xinjiang da jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin ke yi a sabon zamani, tare kuma da shaida babbar niyyar da al’ummun jihar Xinjiang ke da ita a fannin raya jiha mai tsarin gurguzu, kuma irin ta zamani, karkashin jagorancin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin.

Kwarewar gwamnatin kasar Sin wajen tafiyar da harkokin mulki, abu ne da yake a bayyane, al’amarin da ya zama babban dalilin da ya kawo manyan sauye-sauye ga jihar ta Xinjiang. Sakamakon matukar kokarin da aka yi, an cimma nasarori da dama wajen dakile ’yan a-ware na wurin, har ta kai ba a samu wakanar ayyukan ta’addanci a tsawon shekaru da dama a yankin ba, al’amarin da ya tabbatar da kwanciyar hankali, da hadin-kan mabambantan kabilun yankin.

Zaman karko shi ne ke haifar da tabbaci ga ci gaban tattalin arziki. Ci gaba mai inganci da jihar Xinjiang ta samu, zai taimaka gaya ga ci gaban sauran kasashe, tare da samar da damarmakin zamanintar da yankin tsakiyar Asiya gami da sauran shiyyoyi.

A halin yanzu, kasar Sin na himmatuwa wajen zamanintar da kanta bisa salon musamman, yayin da aikin zamanintar da jihar Xinjiang ma ke cikin sabon mafari. Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya kafa alkiblar ci gaban Xinjiang a nan gaba, ciki har da raya sana’o’i na musamman, da bunkasa sabon karfin samar da hajoji da hidimomi masu karko, da raya al’adu da sana’ar yawon shakatawa tare, da inganta aikin kiyayewa, gami da farfado da tsarin muhallin halittu, da gaggauta raya muhimmin yankin tattalin arziki dake kan hanyar siliki da sauransu.

Gagaruman sauye-sauyen da jihar Xinjiang ta samu sun shaida cewa, yadda jama’a ke more rayuwa, hakkin dan Adam ne mafi muhimmanci. Babu shakka, jihar Xinjiang tana fuskantar makoma mai haske. (Murtala Zhang)

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO
Daga Birnin Sin

Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

October 17, 2025
An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana

October 17, 2025
Tawagar Sin Ta Dindindin A Hukumar Fao Ta Fara Aiki
Daga Birnin Sin

Tawagar Sin Ta Dindindin A Hukumar Fao Ta Fara Aiki

October 17, 2025
Next Post
Mazauna Kuyello A Jihar Kaduna Na Cikin Zullumin Bayyanar ‘Yan Ta’addar Ansaru

Gwamnati Ta Kafa Kwamitin Bincike A Kan Fashewar Wani Abu A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI

Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI

October 18, 2025
An Fara Yi Wa Yara Miliyan 1.6 Rigakafi A Taraba

An Fara Yi Wa Yara Miliyan 1.6 Rigakafi A Taraba

October 18, 2025
Lewandowski Ba Zai Buga Wasan El Classico Ba

Lewandowski Ba Zai Buga Wasan El Classico Ba

October 18, 2025
Ƴansanda Sun Kama Gungun Masu Sojan Gona Suna Aikata Laifuka A Kano

Ƴansanda Sun Kama Gungun Masu Sojan Gona Suna Aikata Laifuka A Kano

October 18, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

October 18, 2025
Radda

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Al’umma Su Hada Hannu Da Gwamnati Wajen Kawar Da Matsalar Tsaro

October 18, 2025
Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi

Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi

October 18, 2025
IMF

Fitar Da Kudi Ta Haramtacciyar Hanya Na Kara Dagula Matsalar Tattalin Arziki – IMF

October 18, 2025
majalisar kasa

Majalisar Wakilai Ta Gayyaci CBN Da Bankuna Kan Cire Wa Kwastomomi Kudi Ba Dalili

October 18, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Matashi Ya Kashe Ɗan Acaɓa Don Neman Kuɗin Auren Mace Ta Uku A Bauchi

October 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.