• English
  • Business News
Friday, October 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Shawarci Al’umma Su Rungumi Zumunci A Tsakaninsu

by Leadership Hausa
3 years ago
Zumunci

Shugaban kungiyar Zumunta da Taimakon Jama’a, ‘’Community Debelopment Association’’ da ke garin Tafa ta karamar hukumar Kagarko a Jihar Kaduna, Alhaji Maikudi Dogo, ya yi kira ga al’ummar garin, da kada su sare wajen cigaba da zumunci da zamantakewar da aka san su dashi shekara da shekaru a tsakaninsu.

Shugaban ya yi wannan kiran ne a lokacin da yake hira da manema labarai yayin gudanar da babban bikinsu na Ajo da suka saba shiryawa akai-akai a harabar ofishin kungiyar da ke garin na Tafa a karshen mako, inda ya yi nuni da cewa, sada zumunci da taimakon juna da al’umma baki daya, sune makasudin kafa kungiyar.

  • Martanin El-Rufa’i: Ko Gawata Ba Za Ta Kusanci PDP Ba
  • “Korar Fulani A Edo: Ina Ake So Wadanda Aka Haifa A Jihar Shekara 50 Su Koma?”

Ya kuma ce, yau shekara sama da 20 kenan da suka kafa kungiyar, a lokacin da membobi 60 kacal, amma yanzu, membobin kungiyar sun haura mutum 200 maza da mata da matasa wadanda suka fito daga jihohi daban-daban na fadin kasar nan, yana mai cewa, ” Alhamdu Lillahi, kungiyar cikin shekarun nan, ta tallafa wa membobin ta da dama ta hanyoyi daban-daban, kamar taimako wajen daurin aure, marasa lafiya, jarin yin kasuwanci da sauran su”.

Alhaji Maikudi sai ya yi kira ga Gwamnatin Jihar Kaduna da ta waiwaye su, ta taimakawa kungiyar da irin tallafin da take baiwa kungiyoyi a jihar, saboda gagarumin taimakon da take yi wa jama’a musamman marasa galihu, da kuma hobbasar da take yi wajen hada kai da jamai’an tsaro don tabbatar da zaman lafiya a Tafa.

A tasu gudunmawar, mataimakin kungiyar, Alhaji Haladu Musa Usman da kakakin kungiyar (PRO) Alhaji Salisu Hassan, duk kira suka yi ga Gwamnati da ta tallafa wa kungiyar saboda taimakon jama’a da take tayi shekara da shekaru.

LABARAI MASU NASABA

An Yi Wa Yara Sama Da Miliyan Biyu Allurar Rigakafin Mashaƙo Da Sankarau A Zamfara

‘Yansanda Sun Ceto Mutum Ɗaya, Sun Kama Mace Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Dajin Kwara 

Ita ma Shugabar mata, Hajiya Ladidi Kabuga, kira ta yi ga membobin kungiyar, maza da mata, da suci gaba da bin dokokin kungiyar, su kuma zama masu ladabi da biyayya, har ila yau, su kasance masu Kyakkyawar zamantakewa a tsakanin su.

An dai tashi bikin lami lafiya. Cikin manyan bakin da suka halarci bikin akwai Alhaji Danladi Obajana, Alhaji Baffa na ‘yan Canji, Alhaji Musa mai Shadda, Alhaji Abubakar mai DubuDubu, Alhaji Wawan Sarki, Hakimi Uban Badodo daga Bauchi, da Alhaji Dilan fata daga Gombe. Wasu kuma sune, Hajiya Maimuna kawo daga Kano; Hajiya Maryam Oka.

Jamila Gombe; Hajiya Jummai daga Mokwa, da Hajiya Fati Cestelo daga Mararrabar Jos. Sauran sun hada da Usaina daga Mararrabar Jos, Hajiya Bilki daga Kano, da kuma Hajiya Aisha daga Bauchi

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Yi Wa Yara Sama Da Miliyan Biyu Allurar Rigakafin Mashaƙo Da Sankarau A Zamfara
Labarai

An Yi Wa Yara Sama Da Miliyan Biyu Allurar Rigakafin Mashaƙo Da Sankarau A Zamfara

October 30, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

‘Yansanda Sun Ceto Mutum Ɗaya, Sun Kama Mace Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Dajin Kwara 

October 30, 2025
Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai
Labarai

Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai

October 30, 2025
Next Post
Sardaunan Funtuwa Ya Nemi Al’umma Su Tashi Tsaye Wajen Gudanar Da Addu’o’i

Sardaunan Funtuwa Ya Nemi Al'umma Su Tashi Tsaye Wajen Gudanar Da Addu’o'i

LABARAI MASU NASABA

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo

October 30, 2025
An Yi Wa Yara Sama Da Miliyan Biyu Allurar Rigakafin Mashaƙo Da Sankarau A Zamfara

An Yi Wa Yara Sama Da Miliyan Biyu Allurar Rigakafin Mashaƙo Da Sankarau A Zamfara

October 30, 2025
Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma 

Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma 

October 30, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Ceto Mutum Ɗaya, Sun Kama Mace Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Dajin Kwara 

October 30, 2025
Babban Daraktan Sakatariyar APEC: Sin Tana Ba Da Gudummawar Ba Da Jagoranci A APEC

Babban Daraktan Sakatariyar APEC: Sin Tana Ba Da Gudummawar Ba Da Jagoranci A APEC

October 30, 2025
Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray

Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray

October 30, 2025
Kasar Sin Ce Ke Da Sama Da Rabin Muhimman Makaloli Na Duniya

Kasar Sin Ce Ke Da Sama Da Rabin Muhimman Makaloli Na Duniya

October 30, 2025
Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai

Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai

October 30, 2025
Bunkasar Fannin Kirkire-Kirkiren Fasahohi Na Sin Alheri Ne Ga Dukkanin Duniya Ba Barazana Ba

Bunkasar Fannin Kirkire-Kirkiren Fasahohi Na Sin Alheri Ne Ga Dukkanin Duniya Ba Barazana Ba

October 30, 2025
Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

October 30, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.