• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Shawarci Al’umma Su Rungumi Zumunci A Tsakaninsu

by Leadership Hausa
3 years ago
in Labarai
0
An Shawarci Al’umma Su Rungumi Zumunci A Tsakaninsu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kungiyar Zumunta da Taimakon Jama’a, ‘’Community Debelopment Association’’ da ke garin Tafa ta karamar hukumar Kagarko a Jihar Kaduna, Alhaji Maikudi Dogo, ya yi kira ga al’ummar garin, da kada su sare wajen cigaba da zumunci da zamantakewar da aka san su dashi shekara da shekaru a tsakaninsu.

Shugaban ya yi wannan kiran ne a lokacin da yake hira da manema labarai yayin gudanar da babban bikinsu na Ajo da suka saba shiryawa akai-akai a harabar ofishin kungiyar da ke garin na Tafa a karshen mako, inda ya yi nuni da cewa, sada zumunci da taimakon juna da al’umma baki daya, sune makasudin kafa kungiyar.

  • Martanin El-Rufa’i: Ko Gawata Ba Za Ta Kusanci PDP Ba
  • “Korar Fulani A Edo: Ina Ake So Wadanda Aka Haifa A Jihar Shekara 50 Su Koma?”

Ya kuma ce, yau shekara sama da 20 kenan da suka kafa kungiyar, a lokacin da membobi 60 kacal, amma yanzu, membobin kungiyar sun haura mutum 200 maza da mata da matasa wadanda suka fito daga jihohi daban-daban na fadin kasar nan, yana mai cewa, ” Alhamdu Lillahi, kungiyar cikin shekarun nan, ta tallafa wa membobin ta da dama ta hanyoyi daban-daban, kamar taimako wajen daurin aure, marasa lafiya, jarin yin kasuwanci da sauran su”.

Alhaji Maikudi sai ya yi kira ga Gwamnatin Jihar Kaduna da ta waiwaye su, ta taimakawa kungiyar da irin tallafin da take baiwa kungiyoyi a jihar, saboda gagarumin taimakon da take yi wa jama’a musamman marasa galihu, da kuma hobbasar da take yi wajen hada kai da jamai’an tsaro don tabbatar da zaman lafiya a Tafa.

A tasu gudunmawar, mataimakin kungiyar, Alhaji Haladu Musa Usman da kakakin kungiyar (PRO) Alhaji Salisu Hassan, duk kira suka yi ga Gwamnati da ta tallafa wa kungiyar saboda taimakon jama’a da take tayi shekara da shekaru.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

Atiku Ya Zargi Tinubu Da Fifita Ziyarar Siyasa A Maimaikon Ta Waɗanda Rashin Tsaro Ya Shafa 

Ita ma Shugabar mata, Hajiya Ladidi Kabuga, kira ta yi ga membobin kungiyar, maza da mata, da suci gaba da bin dokokin kungiyar, su kuma zama masu ladabi da biyayya, har ila yau, su kasance masu Kyakkyawar zamantakewa a tsakanin su.

An dai tashi bikin lami lafiya. Cikin manyan bakin da suka halarci bikin akwai Alhaji Danladi Obajana, Alhaji Baffa na ‘yan Canji, Alhaji Musa mai Shadda, Alhaji Abubakar mai DubuDubu, Alhaji Wawan Sarki, Hakimi Uban Badodo daga Bauchi, da Alhaji Dilan fata daga Gombe. Wasu kuma sune, Hajiya Maimuna kawo daga Kano; Hajiya Maryam Oka.

Jamila Gombe; Hajiya Jummai daga Mokwa, da Hajiya Fati Cestelo daga Mararrabar Jos. Sauran sun hada da Usaina daga Mararrabar Jos, Hajiya Bilki daga Kano, da kuma Hajiya Aisha daga Bauchi


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Addu'aZaman LafiyaZumunci
ShareTweetSendShare
Previous Post

RTEAN Za Ta Jagoranci Samar Da Motoci Masu Amfani Da Iskar Gas A Nijeriya

Next Post

Sardaunan Funtuwa Ya Nemi Al’umma Su Tashi Tsaye Wajen Gudanar Da Addu’o’i

Related

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

22 minutes ago
Ban Bar PDP Ba, Ina Gangamin Hadin Gwiwa Ne Don Tunkarar APC A 2027 – Atiku
Labarai

Atiku Ya Zargi Tinubu Da Fifita Ziyarar Siyasa A Maimaikon Ta Waɗanda Rashin Tsaro Ya Shafa 

1 hour ago
Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 
Labarai

Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

2 hours ago
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

5 hours ago
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Manyan Labarai

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

7 hours ago
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram
Manyan Labarai

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

19 hours ago
Next Post
Sardaunan Funtuwa Ya Nemi Al’umma Su Tashi Tsaye Wajen Gudanar Da Addu’o’i

Sardaunan Funtuwa Ya Nemi Al'umma Su Tashi Tsaye Wajen Gudanar Da Addu’o'i

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

October 5, 2025
Ban Bar PDP Ba, Ina Gangamin Hadin Gwiwa Ne Don Tunkarar APC A 2027 – Atiku

Atiku Ya Zargi Tinubu Da Fifita Ziyarar Siyasa A Maimaikon Ta Waɗanda Rashin Tsaro Ya Shafa 

October 5, 2025
Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

October 5, 2025
Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

October 5, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

October 5, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.