• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Shirya Wa Gwamna Inuwa Kasaitaccen Bikin Raye-rayen Al’adun Gargajiya Gabanin Rantsar Da Shi 

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
An Shirya Wa Gwamna Inuwa Kasaitaccen Bikin Raye-rayen Al’adun Gargajiya Gabanin Rantsar Da Shi 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A shirye-shiryen sake rantsar da gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya a matsayin gwamnan Jihar Gombe karo na biyu, tawagogin raye-raye da bushe-bushen al’adu daban-daban suka hallara a gdain Gwamnatin jihar domin nuna bajintarsu kan al’adu.

 

Kungiyoyin al’adun daban-daban sanye da kaya kala-kala sun baje kolin basirarsu, dake nuna bambance-bambancen al’adu da zaman lafiya a Jihar Gombe, tare da nuna goyon bayansu ga Gwamna Inuwa Yahaya da al’ummar Jihar Gombe kan bikin rantsarwar dake tafe a ranar Litinin.

  • Jirgin Sama Samfurin C919 Kirar Kasar Sin Ya Fara Jigilar Fasinjoji

Wasu daga cikin kungiyoyin al’adun da suka cashe a dandalin, sun hada da Laku daga Kaltungo, da Babu Nare daga Kwami, da Ngorda daga Yamaltu/Deba, da masu rawan al’adu na Waja daga Balanga, da Bitbit daga Billiri, da Fulani daga tawagar raya al’adu ta Jihar Gombe, da Dankwairon Gwamna da kuma masu kiɗdan al’adu na Yarbawa.

 

Labarai Masu Nasaba

Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Sauran mawakan zamani na gida da suka nishadantar a taron sun hada da Sale El-square, da S-Niggar Gombe, da Kubura Sarkin Fulani, da Abbati Gombe da dai sauransu.

 

A takaitaccen jawabin da ya gabatar, Gwamna Inuwa ya gode wa wadanda suka shirya taron, da wadanda suka nishaɗdantar da kuma wadanda suka halarci gagarumin bikin.

 

Game da nasararsa ta kwanan nan na zama Shugaban kungiyar Gwamnonin Arewa, Gwamna Inuwa ya bayyana nasarar a matsayin wata dama ta kara hidimtawa jama’a, inda ya sadaukar da matsayin ga dokacin al’ummar Jihar Gombe.

 

Ya ce, “Wannan matsayi ba nawa ni kadai ba ne, na dokacin al’ummar Jihar Gombe ne,” yana mai ba da tabbacin cewa ba zai ci amanar al’ummar jihar dama na Arewa ba.

 

Gwamnan ya yi amfani da damar wajen sabunta kira ga ‘yan siyasa musamman wadanda suka sha kaye a zabe, da su ajiye muradun su a gefe, su bada gudummawa don gina kasa.

 

Tun farko a jawabinsa na maraba, Farfesa Ibrahim Abubakar Ndodi wanda shi ne shugaban kwamitin tsare-tsaren sake rantsar da gwamnan, ya ce wannan dare na shagulgulan al’adu yana daga cikin shirye-shiryen rantsarwar wanda za a karkare gobe Litinin 29 ga wannan watan na Mayu, inda za a rantsar da Gwamna Inuwa Yahaya a karo na biyu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Minista Sadiya Ta Mika Ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinkai Ga Babban Sakatare

Next Post

Jihar Kano Ta Ayyana Masu Kwacen Waya A Matsayin ‘Yan Fashi Da Makami

Related

Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi
Manyan Labarai

Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

28 minutes ago
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita
Labarai

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

10 hours ago
NNPP
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

12 hours ago
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Manyan Labarai

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

15 hours ago
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

15 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Labarai

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

17 hours ago
Next Post
Jihar Kano Ta Ayyana Masu Kwacen Waya A Matsayin ‘Yan Fashi Da Makami

Jihar Kano Ta Ayyana Masu Kwacen Waya A Matsayin 'Yan Fashi Da Makami

LABARAI MASU NASABA

Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

September 19, 2025
An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

September 18, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.