ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, November 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Shirya Wa Gwamna Inuwa Kasaitaccen Bikin Raye-rayen Al’adun Gargajiya Gabanin Rantsar Da Shi 

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Gwamna Inuwa

A shirye-shiryen sake rantsar da gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya a matsayin gwamnan Jihar Gombe karo na biyu, tawagogin raye-raye da bushe-bushen al’adu daban-daban suka hallara a gdain Gwamnatin jihar domin nuna bajintarsu kan al’adu.

 

Kungiyoyin al’adun daban-daban sanye da kaya kala-kala sun baje kolin basirarsu, dake nuna bambance-bambancen al’adu da zaman lafiya a Jihar Gombe, tare da nuna goyon bayansu ga Gwamna Inuwa Yahaya da al’ummar Jihar Gombe kan bikin rantsarwar dake tafe a ranar Litinin.

ADVERTISEMENT
  • Jirgin Sama Samfurin C919 Kirar Kasar Sin Ya Fara Jigilar Fasinjoji

Wasu daga cikin kungiyoyin al’adun da suka cashe a dandalin, sun hada da Laku daga Kaltungo, da Babu Nare daga Kwami, da Ngorda daga Yamaltu/Deba, da masu rawan al’adu na Waja daga Balanga, da Bitbit daga Billiri, da Fulani daga tawagar raya al’adu ta Jihar Gombe, da Dankwairon Gwamna da kuma masu kiɗdan al’adu na Yarbawa.

 

LABARAI MASU NASABA

Bayan Ganawa Da Tinubu, COAS Ya Tabbatar Wa ‘Yan Nijeriya Samun Ingantaccen Tsaro

Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal

Sauran mawakan zamani na gida da suka nishadantar a taron sun hada da Sale El-square, da S-Niggar Gombe, da Kubura Sarkin Fulani, da Abbati Gombe da dai sauransu.

 

A takaitaccen jawabin da ya gabatar, Gwamna Inuwa ya gode wa wadanda suka shirya taron, da wadanda suka nishaɗdantar da kuma wadanda suka halarci gagarumin bikin.

 

Game da nasararsa ta kwanan nan na zama Shugaban kungiyar Gwamnonin Arewa, Gwamna Inuwa ya bayyana nasarar a matsayin wata dama ta kara hidimtawa jama’a, inda ya sadaukar da matsayin ga dokacin al’ummar Jihar Gombe.

 

Ya ce, “Wannan matsayi ba nawa ni kadai ba ne, na dokacin al’ummar Jihar Gombe ne,” yana mai ba da tabbacin cewa ba zai ci amanar al’ummar jihar dama na Arewa ba.

 

Gwamnan ya yi amfani da damar wajen sabunta kira ga ‘yan siyasa musamman wadanda suka sha kaye a zabe, da su ajiye muradun su a gefe, su bada gudummawa don gina kasa.

 

Tun farko a jawabinsa na maraba, Farfesa Ibrahim Abubakar Ndodi wanda shi ne shugaban kwamitin tsare-tsaren sake rantsar da gwamnan, ya ce wannan dare na shagulgulan al’adu yana daga cikin shirye-shiryen rantsarwar wanda za a karkare gobe Litinin 29 ga wannan watan na Mayu, inda za a rantsar da Gwamna Inuwa Yahaya a karo na biyu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Coas
Manyan Labarai

Bayan Ganawa Da Tinubu, COAS Ya Tabbatar Wa ‘Yan Nijeriya Samun Ingantaccen Tsaro

November 11, 2025
Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal
Labarai

Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal

November 11, 2025
‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3 A Nasarawa
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3 A Nasarawa

November 11, 2025
Next Post
Jihar Kano Ta Ayyana Masu Kwacen Waya A Matsayin ‘Yan Fashi Da Makami

Jihar Kano Ta Ayyana Masu Kwacen Waya A Matsayin 'Yan Fashi Da Makami

LABARAI MASU NASABA

Coas

Bayan Ganawa Da Tinubu, COAS Ya Tabbatar Wa ‘Yan Nijeriya Samun Ingantaccen Tsaro

November 11, 2025
Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam

Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam

November 11, 2025
Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa

Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa

November 11, 2025
Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal

Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal

November 11, 2025
CIIE Ya Kasance Gadar Sada Tattalin Arzikin Kasar Sin Da Na Duniya

CIIE Ya Kasance Gadar Sada Tattalin Arzikin Kasar Sin Da Na Duniya

November 11, 2025
CMG Ya Gabatar Da Sabbin Manhajoji 10 Da Ya Kirkiro Don Watsa Gasar Wasannin Motsa Jiki Ta Kasar Sin Karo Na 15

CMG Ya Gabatar Da Sabbin Manhajoji 10 Da Ya Kirkiro Don Watsa Gasar Wasannin Motsa Jiki Ta Kasar Sin Karo Na 15

November 11, 2025
‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3 A Nasarawa

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3 A Nasarawa

November 11, 2025
Cikin Wata Ɗaya, ‘Yansanda Sun Kama Mutane 200 Da Ake Zargi Da Laifuka A Katsina

Cikin Wata Ɗaya, ‘Yansanda Sun Kama Mutane 200 Da Ake Zargi Da Laifuka A Katsina

November 11, 2025
CIIE Ya Ba ‘Yan Kasuwar Afirka Damar Habaka Cinikinsu Da Sin 

CIIE Ya Ba ‘Yan Kasuwar Afirka Damar Habaka Cinikinsu Da Sin 

November 11, 2025
Me Sabon Tarihin Da Aka Kafa A Baje Kolin CIIE Ke Nunawa?

Me Sabon Tarihin Da Aka Kafa A Baje Kolin CIIE Ke Nunawa?

November 11, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.