• English
  • Business News
Saturday, May 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Shirya Wa Gwamna Inuwa Kasaitaccen Bikin Raye-rayen Al’adun Gargajiya Gabanin Rantsar Da Shi 

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
An Shirya Wa Gwamna Inuwa Kasaitaccen Bikin Raye-rayen Al’adun Gargajiya Gabanin Rantsar Da Shi 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A shirye-shiryen sake rantsar da gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya a matsayin gwamnan Jihar Gombe karo na biyu, tawagogin raye-raye da bushe-bushen al’adu daban-daban suka hallara a gdain Gwamnatin jihar domin nuna bajintarsu kan al’adu.

 

Kungiyoyin al’adun daban-daban sanye da kaya kala-kala sun baje kolin basirarsu, dake nuna bambance-bambancen al’adu da zaman lafiya a Jihar Gombe, tare da nuna goyon bayansu ga Gwamna Inuwa Yahaya da al’ummar Jihar Gombe kan bikin rantsarwar dake tafe a ranar Litinin.

  • Jirgin Sama Samfurin C919 Kirar Kasar Sin Ya Fara Jigilar Fasinjoji

Wasu daga cikin kungiyoyin al’adun da suka cashe a dandalin, sun hada da Laku daga Kaltungo, da Babu Nare daga Kwami, da Ngorda daga Yamaltu/Deba, da masu rawan al’adu na Waja daga Balanga, da Bitbit daga Billiri, da Fulani daga tawagar raya al’adu ta Jihar Gombe, da Dankwairon Gwamna da kuma masu kiɗdan al’adu na Yarbawa.

 

Labarai Masu Nasaba

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Sauran mawakan zamani na gida da suka nishadantar a taron sun hada da Sale El-square, da S-Niggar Gombe, da Kubura Sarkin Fulani, da Abbati Gombe da dai sauransu.

 

A takaitaccen jawabin da ya gabatar, Gwamna Inuwa ya gode wa wadanda suka shirya taron, da wadanda suka nishaɗdantar da kuma wadanda suka halarci gagarumin bikin.

 

Game da nasararsa ta kwanan nan na zama Shugaban kungiyar Gwamnonin Arewa, Gwamna Inuwa ya bayyana nasarar a matsayin wata dama ta kara hidimtawa jama’a, inda ya sadaukar da matsayin ga dokacin al’ummar Jihar Gombe.

 

Ya ce, “Wannan matsayi ba nawa ni kadai ba ne, na dokacin al’ummar Jihar Gombe ne,” yana mai ba da tabbacin cewa ba zai ci amanar al’ummar jihar dama na Arewa ba.

 

Gwamnan ya yi amfani da damar wajen sabunta kira ga ‘yan siyasa musamman wadanda suka sha kaye a zabe, da su ajiye muradun su a gefe, su bada gudummawa don gina kasa.

 

Tun farko a jawabinsa na maraba, Farfesa Ibrahim Abubakar Ndodi wanda shi ne shugaban kwamitin tsare-tsaren sake rantsar da gwamnan, ya ce wannan dare na shagulgulan al’adu yana daga cikin shirye-shiryen rantsarwar wanda za a karkare gobe Litinin 29 ga wannan watan na Mayu, inda za a rantsar da Gwamna Inuwa Yahaya a karo na biyu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Minista Sadiya Ta Mika Ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinkai Ga Babban Sakatare

Next Post

Jihar Kano Ta Ayyana Masu Kwacen Waya A Matsayin ‘Yan Fashi Da Makami

Related

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta
Ra'ayi Riga

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

14 hours ago
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci
Labarai

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

16 hours ago
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma
Noma Da Kiwo

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

17 hours ago
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje
Labarai

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

18 hours ago
GORON JUMA’A 09/05/2025
Labarai

GORON JUMA’A 09/05/2025

19 hours ago
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 
Labarai

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

20 hours ago
Next Post
Jihar Kano Ta Ayyana Masu Kwacen Waya A Matsayin ‘Yan Fashi Da Makami

Jihar Kano Ta Ayyana Masu Kwacen Waya A Matsayin 'Yan Fashi Da Makami

LABARAI MASU NASABA

Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo

Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo

May 9, 2025
Babban Bankin Sin Zai Inganta Hidimomin Kudi Don Habaka Amfani Da Shi

Babban Bankin Sin Zai Inganta Hidimomin Kudi Don Habaka Amfani Da Shi

May 9, 2025
Sin Da Rasha Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Zurfafa Dangantakar Abokantaka Ta Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-tsare A Sabon Zamani

Sin Da Rasha Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Zurfafa Dangantakar Abokantaka Ta Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-tsare A Sabon Zamani

May 9, 2025
Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha

Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha

May 9, 2025
Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

May 9, 2025
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

May 9, 2025
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.