ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, September 18, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Shirya Wa Gwamna Inuwa Kasaitaccen Bikin Raye-rayen Al’adun Gargajiya Gabanin Rantsar Da Shi 

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Gwamna Inuwa

A shirye-shiryen sake rantsar da gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya a matsayin gwamnan Jihar Gombe karo na biyu, tawagogin raye-raye da bushe-bushen al’adu daban-daban suka hallara a gdain Gwamnatin jihar domin nuna bajintarsu kan al’adu.

 

Kungiyoyin al’adun daban-daban sanye da kaya kala-kala sun baje kolin basirarsu, dake nuna bambance-bambancen al’adu da zaman lafiya a Jihar Gombe, tare da nuna goyon bayansu ga Gwamna Inuwa Yahaya da al’ummar Jihar Gombe kan bikin rantsarwar dake tafe a ranar Litinin.

ADVERTISEMENT
  • Jirgin Sama Samfurin C919 Kirar Kasar Sin Ya Fara Jigilar Fasinjoji

Wasu daga cikin kungiyoyin al’adun da suka cashe a dandalin, sun hada da Laku daga Kaltungo, da Babu Nare daga Kwami, da Ngorda daga Yamaltu/Deba, da masu rawan al’adu na Waja daga Balanga, da Bitbit daga Billiri, da Fulani daga tawagar raya al’adu ta Jihar Gombe, da Dankwairon Gwamna da kuma masu kiɗdan al’adu na Yarbawa.

 

LABARAI MASU NASABA

Saudiyya Ta Yi Biris Da Bukatar Nijeriya Ta Ƙarin Kujerun Hajjin 2027

Dalilanmu Na Neman NDLEA Ta Binciki Bello El-Rufai Kan Zargin Amfani Da Hodar Iblis

Sauran mawakan zamani na gida da suka nishadantar a taron sun hada da Sale El-square, da S-Niggar Gombe, da Kubura Sarkin Fulani, da Abbati Gombe da dai sauransu.

 

A takaitaccen jawabin da ya gabatar, Gwamna Inuwa ya gode wa wadanda suka shirya taron, da wadanda suka nishaɗdantar da kuma wadanda suka halarci gagarumin bikin.

 

Game da nasararsa ta kwanan nan na zama Shugaban kungiyar Gwamnonin Arewa, Gwamna Inuwa ya bayyana nasarar a matsayin wata dama ta kara hidimtawa jama’a, inda ya sadaukar da matsayin ga dokacin al’ummar Jihar Gombe.

 

Ya ce, “Wannan matsayi ba nawa ni kadai ba ne, na dokacin al’ummar Jihar Gombe ne,” yana mai ba da tabbacin cewa ba zai ci amanar al’ummar jihar dama na Arewa ba.

 

Gwamnan ya yi amfani da damar wajen sabunta kira ga ‘yan siyasa musamman wadanda suka sha kaye a zabe, da su ajiye muradun su a gefe, su bada gudummawa don gina kasa.

 

Tun farko a jawabinsa na maraba, Farfesa Ibrahim Abubakar Ndodi wanda shi ne shugaban kwamitin tsare-tsaren sake rantsar da gwamnan, ya ce wannan dare na shagulgulan al’adu yana daga cikin shirye-shiryen rantsarwar wanda za a karkare gobe Litinin 29 ga wannan watan na Mayu, inda za a rantsar da Gwamna Inuwa Yahaya a karo na biyu.

Gwamna Inuwa
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora

MASU ALAKA

Saudiyya Ta Yi Biris Da Bukatar Nijeriya Ta Ƙarin Kujerun Hajjin 2027
Labarai

Saudiyya Ta Yi Biris Da Bukatar Nijeriya Ta Ƙarin Kujerun Hajjin 2027

September 18, 2026
Dalilanmu Na Neman NDLEA Ta Binciki Bello El-Rufai Kan Zargin Amfani Da Hodar Iblis
Labarai

Dalilanmu Na Neman NDLEA Ta Binciki Bello El-Rufai Kan Zargin Amfani Da Hodar Iblis

September 18, 2026
Shettima Ya Yi Karin Haske Kan Maganar Gwamnonin Arewa 6
Labarai

Shettima Ya Yi Karin Haske Kan Maganar Gwamnonin Arewa 6

September 18, 2026
Next Post
Jihar Kano Ta Ayyana Masu Kwacen Waya A Matsayin ‘Yan Fashi Da Makami

Jihar Kano Ta Ayyana Masu Kwacen Waya A Matsayin 'Yan Fashi Da Makami

LABARAI MASU NASABA

Saudiyya Ta Yi Biris Da Bukatar Nijeriya Ta Ƙarin Kujerun Hajjin 2027

Saudiyya Ta Yi Biris Da Bukatar Nijeriya Ta Ƙarin Kujerun Hajjin 2027

September 18, 2026
Dalilanmu Na Neman NDLEA Ta Binciki Bello El-Rufai Kan Zargin Amfani Da Hodar Iblis

Dalilanmu Na Neman NDLEA Ta Binciki Bello El-Rufai Kan Zargin Amfani Da Hodar Iblis

September 18, 2026
Shettima Ya Yi Karin Haske Kan Maganar Gwamnonin Arewa 6

Shettima Ya Yi Karin Haske Kan Maganar Gwamnonin Arewa 6

September 18, 2026
Cinikin Shige Da Fice Mai Dorewa Ba Tare Da Gurbatta Muhalli Ba Na Kasar Sin Yana Sahun Gaba A Duniya

Cinikin Shige Da Fice Mai Dorewa Ba Tare Da Gurbatta Muhalli Ba Na Kasar Sin Yana Sahun Gaba A Duniya

September 17, 2026
U-20: Nijeriya Ta Doke Ingila Da Ci 3-0, Ta Kai Zagayen Kwata-fainal

U-20: Nijeriya Ta Doke Ingila Da Ci 3-0, Ta Kai Zagayen Kwata-fainal

September 17, 2026
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Zaman Lafiya Da Tsaro Na Sin Da Afirka Karo Na Hudu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Zaman Lafiya Da Tsaro Na Sin Da Afirka Karo Na Hudu

September 17, 2026
Yadda Hadin Gwiwar BRICS Ke Ingiza Ci Gaban Kasashe Masu Tasowa

Yadda Hadin Gwiwar BRICS Ke Ingiza Ci Gaban Kasashe Masu Tasowa

September 17, 2026
Nazarin CGTN: Baje Koli Na Sin Da ASEAN Ya Nuna Kudurin Sin Na Bunkasa Bude Kofa

Nazarin CGTN: Baje Koli Na Sin Da ASEAN Ya Nuna Kudurin Sin Na Bunkasa Bude Kofa

September 17, 2026
An Kammala Taro Na 13 Na Dandalin Tattauna Tsaro Na Xiangshan A Beijing

An Kammala Taro Na 13 Na Dandalin Tattauna Tsaro Na Xiangshan A Beijing

September 18, 2026
Ka Da Ku Siyar Da Gidajenku Don Sayen Hannun Jarin Matatar Dangote – Sanusi II

Ka Da Ku Siyar Da Gidajenku Don Sayen Hannun Jarin Matatar Dangote – Sanusi II

September 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.