Ofishin kula da harkokin siyasa na kwamitin kolin JKS, ya gudanar da taro domin tattaunawa kan daftarorin da za a gabatar domin nazarinsu yayin zama na 7 na kwamitin kolin JKS na 19.
Taron na jiya, wanda Xi Jinping, sakatare janar na kwamitin kolin JKS ya jagoranta, ya tattauna kan daftarin rahoto na kwamitin kolin na 19 da za a mika ga babban taron wakilan JKS karo na 20, da daftarin yi wa kundin tsarin JKS garambawul da daftarin rahoton aiki na hukumar kolin JKS mai sa ido kan da’a, wanda za a mika ga babban taron wakilan JKS karo na 20.
Har ila yau, ofishin kula da harkokin siyasa na kwamitin kolin na 19, ya tattauna kan rahoton aiwatar da wasu matakai 8 na inganta jam’iyyar da ayyukan gwamnati, da kuma rahoton aiki na gano wasu dabaru marasa amfani da rage matsi kan kananan hukumomi, tun bayan babban taron wakilan JKS karo na 19. (Fa’iza Mustapha)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp