• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Wayar Da Kan Iyaye A Jihar Kaduna Kan Alfanun Shirin Bunkasa Ilimin ‘Ya’Ya Mata Na AGILE

by Abubakar Abba
1 month ago
in Labarai
0
An Wayar Da Kan Iyaye A Jihar Kaduna Kan Alfanun Shirin Bunkasa Ilimin ‘Ya’Ya Mata Na AGILE
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An gudanar da taron gangamin wayar da kan al’ummar da ke a garin Rigachikun a karamar hukumar Igabi a jihar Kaduna, musamman iyaye kan alfanun tura ‘ya’yansu mata makarantar sakandare, domin su ci gajiyar shirin bunkasa ilimin ‘ya’ya mata na AGILE.

A hirarta da manema labarai jim kadan bayan kammala taron, Ko’idinatar shirin na Jihar Kaduna, Maryam Sani dangaji ta ce, makasudin taron shi ne, domin wayar wa iyayen da ke a garin Rigachikun da kewaye kai kan mahimmancin su tura ‘ya’yansu mata zuwa makarantar sakandare da kuma tallafin kudin karatu, da Bankin Duniya ke turawa kai tsaye zuwa ga asusun bankin na daliban mata.

  • Aikin Bututun Gas Na Nijeriya – Morocco Na Ƙara Samun Ci Gaba
  • Abubuwa 5 da Ya Kamata Ku Sani Game da Wasan Ƙarshe Tsakanin Chelsea Da PSG

Maryam ta ce, shirin ya faro ne daga matakin makarantar firamare zuwa na sakandare, musamman domin su ci gajiyar shirin.

Ta ce, wannan wayar da kan shi ne karo na uku, inda ta ce, muhimmancin wayar da kan shi ne, yawanci wasu iyayen ba su da masaniya kan shirin, wanda kuma shi ne, Bankin Duniya ya ga ya kamata a zo yankin domin a kara wayar da kan iyaye kan alfanun Shirin.

Maryam ta yi nuni da cewa, tallace-tallace, musamman a tsakanin ‘ya’ya mata bai da wani alfanu, amma samun ilimin zamani na da babban tasiri ga rayuwar mata da kuma al’umma.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

Ko’odinitar ta ce a baya a karkashin shirin, ana bayar da tallafin naira 5,000, wanda ya koma koma naira 15,000, kuma a yanzu ya koma naira 25,000.

Mayarma ta kara da cewa irin wannan tallafin zai taimaka wa iyayen daliban mata wajen saya musu abubuwa irinsu takalmin zuwa makaranta, ko takardun karatu ko Biro da sauran kayan karatu.

Ita ma daya daga cikin ma’aikatan Bankin Duniya, Dakta Basir Rufa’I ta ce, an wayar da kan ‘ya’ya matan kan yadda za su rajista a karkashin shirin.

Ta ce, akwai kuma ka’ida da aka gindiya ga wadanda su ci gajiyar shirin, wanda ta ce, shi ne na zuwa makaranta da suka samu maki kaso saba’in a cikin dari a cikin rajistarsu ta zuwa makaranta, wanda ta haka ne za su iya samun cin gajiyar tallafin.

Wasu daga cikin iyayen da ‘ya’yansu mata suka ci gajiyar shirin, Fatima Abubakar da Alh. Idris Maiwada, sun yaba da shirin tare da gode wa gwamnatin Kaduna kan goyon bayan da take ci gaba da bai wa shirin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AGILEƊalibaiIlimiKadunaShiri
ShareTweetSendShare
Previous Post

Cote d’Iboire Ta Amince Da Kafa Bankin Makamashi Na Afirka

Next Post

Wasu Ma’aikatan Fadar Kano Sun Maka Sarki Sanusi Gaban Kotu

Related

An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa
Labarai

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

2 minutes ago
Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP
Manyan Labarai

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

3 hours ago
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru
Manyan Labarai

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

14 hours ago
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

20 hours ago
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?
Labarai

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

21 hours ago
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da Ɗansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

22 hours ago
Next Post
Wasu Ma’aikatan Fadar Kano Sun Maka Sarki Sanusi Gaban Kotu

Wasu Ma'aikatan Fadar Kano Sun Maka Sarki Sanusi Gaban Kotu

LABARAI MASU NASABA

An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

August 24, 2025
Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

August 24, 2025
Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

August 24, 2025
Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

August 24, 2025
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

August 24, 2025
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.