• English
  • Business News
Saturday, October 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Wayar Da Kan Iyaye A Jihar Kaduna Kan Alfanun Shirin Bunkasa Ilimin ‘Ya’Ya Mata Na AGILE

by Abubakar Abba
3 months ago
AGILE

An gudanar da taron gangamin wayar da kan al’ummar da ke a garin Rigachikun a karamar hukumar Igabi a jihar Kaduna, musamman iyaye kan alfanun tura ‘ya’yansu mata makarantar sakandare, domin su ci gajiyar shirin bunkasa ilimin ‘ya’ya mata na AGILE.

A hirarta da manema labarai jim kadan bayan kammala taron, Ko’idinatar shirin na Jihar Kaduna, Maryam Sani dangaji ta ce, makasudin taron shi ne, domin wayar wa iyayen da ke a garin Rigachikun da kewaye kai kan mahimmancin su tura ‘ya’yansu mata zuwa makarantar sakandare da kuma tallafin kudin karatu, da Bankin Duniya ke turawa kai tsaye zuwa ga asusun bankin na daliban mata.

  • Aikin Bututun Gas Na Nijeriya – Morocco Na Ƙara Samun Ci Gaba
  • Abubuwa 5 da Ya Kamata Ku Sani Game da Wasan Ƙarshe Tsakanin Chelsea Da PSG

Maryam ta ce, shirin ya faro ne daga matakin makarantar firamare zuwa na sakandare, musamman domin su ci gajiyar shirin.

Ta ce, wannan wayar da kan shi ne karo na uku, inda ta ce, muhimmancin wayar da kan shi ne, yawanci wasu iyayen ba su da masaniya kan shirin, wanda kuma shi ne, Bankin Duniya ya ga ya kamata a zo yankin domin a kara wayar da kan iyaye kan alfanun Shirin.

Maryam ta yi nuni da cewa, tallace-tallace, musamman a tsakanin ‘ya’ya mata bai da wani alfanu, amma samun ilimin zamani na da babban tasiri ga rayuwar mata da kuma al’umma.

LABARAI MASU NASABA

Jami’ar ABU Ta Ƙaryata Zargin Ƙera Makamin Nukiliya A Asirce

Hukumar Kare Ƴancin Masu Amfani Da Kaya (FCCPC): Tabbatar Da Adalci A Kasuwa

Ko’odinitar ta ce a baya a karkashin shirin, ana bayar da tallafin naira 5,000, wanda ya koma koma naira 15,000, kuma a yanzu ya koma naira 25,000.

Mayarma ta kara da cewa irin wannan tallafin zai taimaka wa iyayen daliban mata wajen saya musu abubuwa irinsu takalmin zuwa makaranta, ko takardun karatu ko Biro da sauran kayan karatu.

Ita ma daya daga cikin ma’aikatan Bankin Duniya, Dakta Basir Rufa’I ta ce, an wayar da kan ‘ya’ya matan kan yadda za su rajista a karkashin shirin.

Ta ce, akwai kuma ka’ida da aka gindiya ga wadanda su ci gajiyar shirin, wanda ta ce, shi ne na zuwa makaranta da suka samu maki kaso saba’in a cikin dari a cikin rajistarsu ta zuwa makaranta, wanda ta haka ne za su iya samun cin gajiyar tallafin.

Wasu daga cikin iyayen da ‘ya’yansu mata suka ci gajiyar shirin, Fatima Abubakar da Alh. Idris Maiwada, sun yaba da shirin tare da gode wa gwamnatin Kaduna kan goyon bayan da take ci gaba da bai wa shirin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’ar ABU Ta Ƙaryata Zargin Ƙera Makamin Nukiliya A Asirce
Manyan Labarai

Jami’ar ABU Ta Ƙaryata Zargin Ƙera Makamin Nukiliya A Asirce

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji
Labarai

Hukumar Kare Ƴancin Masu Amfani Da Kaya (FCCPC): Tabbatar Da Adalci A Kasuwa

October 25, 2025
Fiye da Janarori 50 Za Su Yi Ritaya Bayan Sabbin Naɗe-Naɗen Tinubu
Manyan Labarai

Fiye da Janarori 50 Za Su Yi Ritaya Bayan Sabbin Naɗe-Naɗen Tinubu

October 25, 2025
Next Post
Wasu Ma’aikatan Fadar Kano Sun Maka Sarki Sanusi Gaban Kotu

Wasu Ma'aikatan Fadar Kano Sun Maka Sarki Sanusi Gaban Kotu

LABARAI MASU NASABA

Jami’ar ABU Ta Ƙaryata Zargin Ƙera Makamin Nukiliya A Asirce

Jami’ar ABU Ta Ƙaryata Zargin Ƙera Makamin Nukiliya A Asirce

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Hukumar Kare Ƴancin Masu Amfani Da Kaya (FCCPC): Tabbatar Da Adalci A Kasuwa

October 25, 2025
Fiye da Janarori 50 Za Su Yi Ritaya Bayan Sabbin Naɗe-Naɗen Tinubu

Fiye da Janarori 50 Za Su Yi Ritaya Bayan Sabbin Naɗe-Naɗen Tinubu

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Ma’aikacin Banki Na Shekarar 2025 Dakta Tony Okpanachi

October 25, 2025
Muna Duba Ƙudirin Ƙirƙiro Jihohi 55 – Barau Jibrin

Muna Duba Ƙudirin Ƙirƙiro Jihohi 55 – Barau Jibrin

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Shugaban Kamfani Na Shekarar 2025 Gbenga Olu Komolafe

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Thomas Etuh: Gwarzon Ɗan Kasuwa Na 2025

October 25, 2025
Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma (3)

Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma (3)

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Babban Sarki Oweizide Ekpemupolo (Tompolo): Hiddimta Wa Al’umma Ba Tare Da Gajiyawa Ba

October 25, 2025
Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

October 24, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.