ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, September 12, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Wayar Da Kan Iyaye A Jihar Kaduna Kan Alfanun Shirin Bunkasa Ilimin ‘Ya’Ya Mata Na AGILE

by Abubakar Abba
1 year ago
AGILE

An gudanar da taron gangamin wayar da kan al’ummar da ke a garin Rigachikun a karamar hukumar Igabi a jihar Kaduna, musamman iyaye kan alfanun tura ‘ya’yansu mata makarantar sakandare, domin su ci gajiyar shirin bunkasa ilimin ‘ya’ya mata na AGILE.

A hirarta da manema labarai jim kadan bayan kammala taron, Ko’idinatar shirin na Jihar Kaduna, Maryam Sani dangaji ta ce, makasudin taron shi ne, domin wayar wa iyayen da ke a garin Rigachikun da kewaye kai kan mahimmancin su tura ‘ya’yansu mata zuwa makarantar sakandare da kuma tallafin kudin karatu, da Bankin Duniya ke turawa kai tsaye zuwa ga asusun bankin na daliban mata.

  • Aikin Bututun Gas Na Nijeriya – Morocco Na Ƙara Samun Ci Gaba
  • Abubuwa 5 da Ya Kamata Ku Sani Game da Wasan Ƙarshe Tsakanin Chelsea Da PSG

Maryam ta ce, shirin ya faro ne daga matakin makarantar firamare zuwa na sakandare, musamman domin su ci gajiyar shirin.

ADVERTISEMENT

Ta ce, wannan wayar da kan shi ne karo na uku, inda ta ce, muhimmancin wayar da kan shi ne, yawanci wasu iyayen ba su da masaniya kan shirin, wanda kuma shi ne, Bankin Duniya ya ga ya kamata a zo yankin domin a kara wayar da kan iyaye kan alfanun Shirin.

Maryam ta yi nuni da cewa, tallace-tallace, musamman a tsakanin ‘ya’ya mata bai da wani alfanu, amma samun ilimin zamani na da babban tasiri ga rayuwar mata da kuma al’umma.

LABARAI MASU NASABA

Mene Ne Ra’ayinku Kan Dawo Da Tallafin Man Fetur Ko Barin Sa?

Sin Tana Son Cin Moriya Tare Da Sassan Duniya A Fannin Kirkire-kirkire

Ko’odinitar ta ce a baya a karkashin shirin, ana bayar da tallafin naira 5,000, wanda ya koma koma naira 15,000, kuma a yanzu ya koma naira 25,000.

Mayarma ta kara da cewa irin wannan tallafin zai taimaka wa iyayen daliban mata wajen saya musu abubuwa irinsu takalmin zuwa makaranta, ko takardun karatu ko Biro da sauran kayan karatu.

Ita ma daya daga cikin ma’aikatan Bankin Duniya, Dakta Basir Rufa’I ta ce, an wayar da kan ‘ya’ya matan kan yadda za su rajista a karkashin shirin.

Ta ce, akwai kuma ka’ida da aka gindiya ga wadanda su ci gajiyar shirin, wanda ta ce, shi ne na zuwa makaranta da suka samu maki kaso saba’in a cikin dari a cikin rajistarsu ta zuwa makaranta, wanda ta haka ne za su iya samun cin gajiyar tallafin.

Wasu daga cikin iyayen da ‘ya’yansu mata suka ci gajiyar shirin, Fatima Abubakar da Alh. Idris Maiwada, sun yaba da shirin tare da gode wa gwamnatin Kaduna kan goyon bayan da take ci gaba da bai wa shirin.

AGILE
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

MASU ALAKA

NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN
Labarai

Mene Ne Ra’ayinku Kan Dawo Da Tallafin Man Fetur Ko Barin Sa?

September 12, 2026
Sin Tana Son Cin Moriya Tare Da Sassan Duniya A Fannin Kirkire-kirkire
Labarai

Sin Tana Son Cin Moriya Tare Da Sassan Duniya A Fannin Kirkire-kirkire

September 11, 2026
Sin Da Indiya Na Shirye-shiryen Ganawar Xi Da Modi
Labarai

Sin Da Indiya Na Shirye-shiryen Ganawar Xi Da Modi

September 11, 2026
Next Post
Wasu Ma’aikatan Fadar Kano Sun Maka Sarki Sanusi Gaban Kotu

Wasu Ma'aikatan Fadar Kano Sun Maka Sarki Sanusi Gaban Kotu

LABARAI MASU NASABA

NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Mene Ne Ra’ayinku Kan Dawo Da Tallafin Man Fetur Ko Barin Sa?

September 12, 2026
Sin Ta Nuna Rashin Jin Dadinta Ga Italiya Da Tarayyar Turai Kan Ziyarar Jami’ar DPP

Sin Ta Nuna Rashin Jin Dadinta Ga Italiya Da Tarayyar Turai Kan Ziyarar Jami’ar DPP

September 11, 2026
Sin Tana Son Cin Moriya Tare Da Sassan Duniya A Fannin Kirkire-kirkire

Sin Tana Son Cin Moriya Tare Da Sassan Duniya A Fannin Kirkire-kirkire

September 11, 2026
Sin Da Indiya Na Shirye-shiryen Ganawar Xi Da Modi

Sin Da Indiya Na Shirye-shiryen Ganawar Xi Da Modi

September 11, 2026
Hadin Gwiwar Hada-Hadar Ba Da Hidima Tsakanin Sin Da Afirka Na Karfafa Karfin Afirka

Hadin Gwiwar Hada-Hadar Ba Da Hidima Tsakanin Sin Da Afirka Na Karfafa Karfin Afirka

September 11, 2026
Zaben 2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Bayyana Shirinsu Yayin Da INEC Ta Fitar Da Jawalin Zabe

Dalilan Da Ya Sa Jam’iyyun Siyasa Suka Jinkirta Ƙaddamar Da Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen

September 11, 2026
Nazarin CGTN: Kungiyar BRICS Tana Kara Taka Rawar Gani A Harkokin Duniya

Nazarin CGTN: Kungiyar BRICS Tana Kara Taka Rawar Gani A Harkokin Duniya

September 11, 2026
Za A Ci ’Yan Siyasa Masu Kalaman Ɓatanci Tarar Miliyan 10 Da Ɗaurin Watanni 12 — INEC

2027: A Karon Farko INEC Za Ta Ƙaddamar Da Na’urar Bibiyar Zaɓen Nijeriya

September 11, 2026
Me Ya Sa Kamfanonin Amurka Ke Kyautata Zato Ga Sabuwar Damar Sin?

Me Ya Sa Kamfanonin Amurka Ke Kyautata Zato Ga Sabuwar Damar Sin?

September 11, 2026
Gwarzuwar Ma’aikaciyar Gwamnati Ta Shekarar 2026  Mrs Zubaida Umar

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Gwamnati Ta Shekarar 2026 Mrs Zubaida Umar

September 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.