• English
  • Business News
Monday, November 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Yaye Dalibai 15,139 Masu Digirin NCE A Adamawa

by Muh'd Shafi'u Saleh
12 months ago
Dalibai

Bikin yaye ɗaliban kwalejin ilimi ta tarayya da ke Yola FCE wanda da shi ne karo 15, ɗaya ne daga cikin ɓangarori uku na taron da suka haɗa bikin cikar Kwalejin shekaru 50 da aka ƙaddamar a lokacin gudanar da taron.

Da ya ke jawabi a taron shugaban kwalejin, Mohammad Usman Degereji, ya bayyana cewa tun da aka kafa ta, makarantar ta samu ci gaba a dukkan fannonin da suka shafi kwalejin.

  • Batun ‘Yan Mata Masu Yanga Wajen Tsallaka Titi
  • Mun Shirya Ƙirkiro Sabbin Masarautu A Adamawa – Fintiri

Shugaban ya lissafo wasu daga cikin manyan nasarorin da kwalejin ta samu da suka haɗar da kafa cibiyar ɗalibai don sauƙin samun bayanan sakamako, da bayar da shaidar karatun ilimi a fannonin ilimi daban-daban.

Wasu daga manyan nasarorin da ta samu sun haɗa da samar da motocin bas bas dake ɗaukar ma’aikata da dalibai kyauta na tsawon watanni uku, sakamakon cire tallafin man fetur, da rarraba kayan abinci ga ɗalibai domin sauƙaƙa wahalhalun da ake ciki sakamakon cire tallafin, da gyaran asibitin kwalejin da kuma samar masa kayan aiki, da magunguna hadi da kwararren likita daga FMC Yola.

Shugaban ya kuma godewa gwamnatin tarayya, da gwamnatin jihar Adamawa da kuma hukumar TETFUND, da ma’aikatan Kwalejin da kuma ɗalibai bisa goyon baya da fahimtar da suka bayar na cimma nasarorin da kwalejin ta samu.

LABARAI MASU NASABA

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

A nasa jawabin, ministan Ilimi Tunji Alausa, wanda ya sami wakilcin Dakta Yusuf Sa’eed, ya taya shugaban Kwalejin da hukumar gudanarwa murnar samun ci gaba ya kuma yi alƙawarin gabatar da buƙatar Kwalejin na ingantawa a gaban ministan ilimin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

gombe
Ilimi

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025
Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma
Ilimi

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

October 18, 2025
ASUU
Ilimi

Cikin Wata 9 Farfesoshi 309 Sun Bar Aiki A Jami’o’in Gwamnati, In Ji ASUU

October 18, 2025
Next Post
Gwamnatin Kasar Sin Ta Tallafawa Malawi Da Abinci

Gwamnatin Kasar Sin Ta Tallafawa Malawi Da Abinci

LABARAI MASU NASABA

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

November 2, 2025
Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

November 2, 2025
Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

November 2, 2025
Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

November 2, 2025
Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

November 2, 2025
Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

November 2, 2025
Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

November 2, 2025
Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

November 2, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su

November 2, 2025
Gidauniyar IRM Da KADCHMA Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna

Gidauniyar IRM Da KADCHMA Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna

November 2, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.