Yau Jumma’a da safe, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya halarci bikin rattaba hannu kan yarjejeniyar kafa hukumar shiga tsakani ta kasa da kasa a yankin Hong Kong na kasar Sin.
Manyan wakilai daga kasashe sama da 60 na nahiyar Asiya da Afirka da Latin Amurka da Turai, da wakilai daga hukumomin kasa da kasa kimanin 20 kamar MDD da sauransu, da kuma wasu tsoffin shugabanni da kwararru na kasa da kasa, sun halarci wannan biki.
- An Gudanar Da Dandalin Kawancen Birane Na Kasa Da Kasa Na Shanghai
- Shekara Biyun Mulki Tinubu: Nasarori Da Matsaloli Da Inda Aka Dosa
A yau da yamma kuma, za a gudanar da taron dandalin tattaunawar ayyukan shiga tsakani, inda za a tattauna kan yadda za a gudanar da aikin shiga tsakani a tsakanin kasa da kasa, da kuma yadda za a gudanar da aikin shiga tsakani kan matsalolin kasuwanci da zuba jari.
A shekarar 2022, kasar Sin tare da wasu kasashe kusan 20 masu ra’ayi iri daya, suka kirkiro shirin na kafa hukumar shiga tsakani ta duniya. Kuma ta hanyar hada hannu, an kammala tattaunawa game da yarjejeniyar kafa hukumar, sannan daukacin kasashen sun amince hedkwatarta ta samu mazauni a yankin Hong Kong na kasar Sin.
Babbar manufar hukumar ita ce warware takaddama ta hanyar tattaunawa, kuma za ta zama hukumar da aka kafa irinta ta farko a hukumance dake mayar da hankali kan warware takaddama. Haka kuma, kafuwarta wani muhimmin mataki ne na daukaka ka’idoji da manufofin MDD. (Mai Fassara: Maryam Yang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp