• English
  • Business News
Sunday, May 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Yi Garkuwa Da Sama Da ‘Yan Nijeriya 971 A Watan Oktoban 2024 – Rahoto

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
6 months ago
in Labarai
0
Da Dumi-duminsa: ‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Basarake A Ondo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani rahoto ya bayyana cewa ‘yan Nijeriya sama da 971 aka yi garkuwa da su a sassa daban-daban na kasar a watan Oktoban 2024.

 

Wannan fallasa na zuwa ne a daidai lokacin da wata sabuwar kungiyar ta’addanci ta kunno kai mai suna ‘Lakurawa’ a yankin arewa maso yammacin kasar.

  • A Karon Farko Adadin Motoci Masu Aiki Da Sabon Makamashi Da Kasar Sin Ke Kerawa Duk Shekara Ya Zarce Miliyan 10
  • Kawu Sumaila Ya Yi Barazanar Maka Shugaban NNPP Na Kano A Kotu

Bayanan na kunshe ne a cikin rahoton tsaron Nijeriya na Oktoban 2024, wanda wani kamfani mai kula da hadarin tsaro da kuma kamfanin tuntubar bayanan sirri suka gabatar a ranar Talata.

 

Labarai Masu Nasaba

Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

Rahoton ya ce ana samun tabarbarewar matakan tsaro na al’amura da suka hada da garkuwa da mutane da kuma asarar rayuka a kasar nan, yana mai gargadin cewa karuwar adadin ya nuna cewa shekarar 2024 za ta kasance shekara mafi muni a ayyukan rashin tsaro cikin shekaru goma.

 

Ya yi bayanin cewa watan da ake bitar an gudanar da shi ne ta amfani da al’amuran da ke da alaka da tashe-tashen hankula, da suka hada da kashe-kashe da yin garkuwa da mutane domin neman kudin fansa musamman daga kungiyoyi masu aikata laifuka, kungiyoyin asiri, da kungiyoyin sa kai na kabilanci, da tashe-tashen hankula a cikin al’umma.

 

Kamfanin tsaron ya bayyana cewa, bayanan da aka tattara sun nuna cewa kasar ta samu karuwar mace-mace da kashi 51 da kuma karuwar satar mutane da kashi 24.42.

 

Binciken ya nuna cewa Nijeriya ta samu matsalar tsaro 861, inda kashi 64.92 aka alakanta su da barazanar tsaro, kashi 24.79 sun kunshi ayyukan jami’an tsaro, sannan 4.99 an danganta su da tsaron abubuwan da suka faru daga Oktoban 2024.

 

A cikin watan da aka yi bitar, kasar ta kuma sami asarar rayuka 1545, inda kashi 67.70 ke da nasaba da mutuwar fararen hula, kashi 25.89 ga masu aikata laifuka, sannan kashi 6.40 kuma an danganta su ga jami’an tsaro da kuma mutane 971 da aka sace.

 

Dangane rahoton a sassan fadin kasar nan, yankunan arewa maso gabas da arewa maso yamma ne suka fi fama da matsalar tsaro, wanda ya kai kashi 52.03 na al’amuran da suka faru, yayin da yankin kudu maso gabas ya bayar da rahoton mafi karancin abubuwan da suka faru a kashi 7.78.

 

Haka kuma binciken nuna cewa adadin mutanen da aka kashe ya karu daga 1,022 a watan Satumba na 2024 zuwa 1,545 a watan Oktoban 2024, wanda ke nuna karuwar kashi 51.17.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Bankin Duniya Da Hukumar Lamuni Ke Yi Wa Tsarin Ilimin Nijeriya Zagon-kasa – ASUU

Next Post

Binciken CGTN Ya Nuna Amincewa Da Kokarin Kasar Sin Dangane Da Aiwatar Da Matakan Dakile Sauyin Yanayi

Related

Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)
Labarai

Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

19 minutes ago
Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari
Labarai

Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

1 hour ago
Labarai

Kungiyar Malaman Jami’o’i Ta Ba Dalibai 164 Tallafin Karatu

13 hours ago
Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)
Labarai

Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)

14 hours ago
Ra’ayin Al’umma Game Da Iyaye Masu Furta Muggan Kalamai A Kan ‘Ya’yansu
Labarai

Ra’ayin Al’umma Game Da Iyaye Masu Furta Muggan Kalamai A Kan ‘Ya’yansu

16 hours ago
Wayar Salula Na Dab Da Kai Mu Wutar Jahannama
Labarai

Wayar Salula Na Dab Da Kai Mu Wutar Jahannama

17 hours ago
Next Post
Binciken CGTN Ya Nuna Amincewa Da Kokarin Kasar Sin Dangane Da Aiwatar Da Matakan Dakile Sauyin Yanayi

Binciken CGTN Ya Nuna Amincewa Da Kokarin Kasar Sin Dangane Da Aiwatar Da Matakan Dakile Sauyin Yanayi

LABARAI MASU NASABA

Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

May 11, 2025
Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

May 11, 2025
Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

May 10, 2025
An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva

An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva

May 10, 2025
Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu

Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu

May 10, 2025

Kungiyar Malaman Jami’o’i Ta Ba Dalibai 164 Tallafin Karatu

May 10, 2025
Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)

Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)

May 10, 2025
Sin Ta Nemi Indiya Da Pakistan Su Muhimmanta Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali

Sin Ta Nemi Indiya Da Pakistan Su Muhimmanta Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali

May 10, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Shugabannin Kasashe Daban-Daban A Moscow

Xi Jinping Ya Gana Da Shugabannin Kasashe Daban-Daban A Moscow

May 10, 2025
Ra’ayin Al’umma Game Da Iyaye Masu Furta Muggan Kalamai A Kan ‘Ya’yansu

Ra’ayin Al’umma Game Da Iyaye Masu Furta Muggan Kalamai A Kan ‘Ya’yansu

May 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.