• English
  • Business News
Saturday, October 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Ci Gaba Da Alhinin Rasuwar Ghali Na’Aabba

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Ghali

Al’ummar Nijeriya daga sassa daban-daban na ci gaba da alhinin rasuwar tsohon shugaban majalisar wakilai, Hon. Ghali Umar Na’Abba wanda ya riga mu gidan gaskiya a tsakiyar makon nan.

An gudanar da jana’izarsa a Jihar Kano kamar yadda addinin Musulunci ya tanada.

  • Dalilai 20 Da Ke Sa Dalibai Faduwa Jarrabawa (1)
  • Majalisar NPC Za Ta Fara Zaman Taron Shekara-shekara A Ranar 5 Ga Watan Maris

Na’Abba ya kasance shi ne shugaban majalisar wakilai na hudu, ya rasu yana da shekaru 65 a duniya bayan ya yi fama da rashin lafiya. Tsohon shugaban majalisar ya kasance dan asalin Jihar Kano wanda aka zabe shi a matsayin dan majalisa mai wakiltar Kano ta tsakiya daga 1999 zuwa 2003.

Ya zama shugaban majalisar ne ‘yan watanni bayan kaddamar da majalisar ta hudu biyo bayan murabus din shugaban majalisar na wancan lokaci, Salisu Buhari daga Jihar Kano, kan badakalar jabun takardun makaranta.

Ya taka muhimmiyar rawar a lokacin da ya zama shugaban majalisar wakilai wajen tabbatar da ‘yancin majalisar a tsakanin bangaren gwamnati, wanda hakan ya haddasa rikici tsakaninsa da tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo.

LABARAI MASU NASABA

An Fara Yi Wa Yara Miliyan 1.6 Rigakafi A Taraba

Ƴansanda Sun Kama Gungun Masu Sojan Gona Suna Aikata Laifuka A Kano

Duk da kasancewarsu ‘ya’yan jam’iyya daya tsakanin Na’Abba da Obasanjo, amma bai hana shi yin gwagwarmaya ba wajen tabbatar da ‘yancin majalisa. Ana ganin cewa rikicinsa da Obasanjo ne ya hana shi ya sake dawowa zauren majalisa.

Kwanan nan ya sauya sheka daga jam’iyyar APC, ya koma babbar jam’iyyar adawa ta PDP.

Tarihinsa ya nuna cewa ya halarci Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya a Jihar Kaduna, inda ya karanta kimiyyar siyasa, kuma ya kammala a shekarar 1979.

Kafin rasuwarsa, Na’Abba ya yi fama da rashin lafiya mai tsanani har sai da ta kai an fitar da shi kasar waje domin nema lafiyarsa, kuma ya dawo Nijeriya bayan ya murmure daga cutar da ba a bayyana ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Fara Yi Wa Yara Miliyan 1.6 Rigakafi A Taraba
Labarai

An Fara Yi Wa Yara Miliyan 1.6 Rigakafi A Taraba

October 18, 2025
Ƴansanda Sun Kama Gungun Masu Sojan Gona Suna Aikata Laifuka A Kano
Labarai

Ƴansanda Sun Kama Gungun Masu Sojan Gona Suna Aikata Laifuka A Kano

October 18, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

October 18, 2025
Next Post
MDD Ta Yi Maganar Rayuka 190 Da Aka Kashe A Filato

MDD Ta Yi Maganar Rayuka 190 Da Aka Kashe A Filato

LABARAI MASU NASABA

An Fara Yi Wa Yara Miliyan 1.6 Rigakafi A Taraba

An Fara Yi Wa Yara Miliyan 1.6 Rigakafi A Taraba

October 18, 2025
Lewandowski Ba Zai Buga Wasan El Classico Ba

Lewandowski Ba Zai Buga Wasan El Classico Ba

October 18, 2025
Ƴansanda Sun Kama Gungun Masu Sojan Gona Suna Aikata Laifuka A Kano

Ƴansanda Sun Kama Gungun Masu Sojan Gona Suna Aikata Laifuka A Kano

October 18, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

October 18, 2025
Radda

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Al’umma Su Hada Hannu Da Gwamnati Wajen Kawar Da Matsalar Tsaro

October 18, 2025
Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi

Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi

October 18, 2025
IMF

Fitar Da Kudi Ta Haramtacciyar Hanya Na Kara Dagula Matsalar Tattalin Arziki – IMF

October 18, 2025
majalisar kasa

Majalisar Wakilai Ta Gayyaci CBN Da Bankuna Kan Cire Wa Kwastomomi Kudi Ba Dalili

October 18, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Matashi Ya Kashe Ɗan Acaɓa Don Neman Kuɗin Auren Mace Ta Uku A Bauchi

October 17, 2025
katsina

Tawagar Bankin Duniya Ta Gana Da Gwamnan Katsina Kan Mayar Da ‘Yan Gudun Hijira Muhallinsu

October 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.