Mutane da dama sun rasa rayukansu a wata ambaliyar ruwa da ta mamaye garin Mokwa, hedikwatar karamar hukumar Mokwa a jihar Neja.
Mazauna yankin sun bayyana cewa, titin da ya hada yankunan arewaci da kudancin Nijeriya a Mokwa ya dulmiye sakamakon ambaliyar.
- AU Ta Jinjinawa Goyon Bayan Sin Ga Ci Gaban Nahiyar Afrika
- MDD Ta Gudanar Da Bikin Ranar Tunawa Da Dakarun Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Duniya Ta 2025
Wasu gidaje da kadarori na miliyoyin naira sun nutse a cikin ruwa. Wasu kuma sun ce adadin wadanda suka mutu zai iya zarce 50, saboda har yanzu ba a ga wasu mazauna yankin ba da suka hada da mata da kananan yara.
Ambaliyar dai, ta afku ne sakamakon mamakon ruwan sama da aka shafe sa’o’i da dama yana sauka a daren Laraba.
Wani mazaunin garin, Mohammed Usman ya ce tuni aka fara tsamo gawarwaki da dama a cikin ruwan, amma wasu da dama ba a iya ganin su ba musamman a wuraren da gidaje suka nutse.
Daraktan yada labarai da ayyuka na musamman a Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Neja, Dakta Ibrahim Audu Hussaini, ya tabbatar da faruwar lamarin.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp