• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Samun Sakamako Mai Kyau A Hadin Gwiwar Dake Tsakanin Sin Da Afirka

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Ana Samun Sakamako Mai Kyau A Hadin Gwiwar Dake Tsakanin Sin Da Afirka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An gudanar da taron manyan wakilai game da nazarin matakan aiwatar da sakamakon taron ministoci karo na 8 na dandalin tattaunawar hadin gwiwar kasar Sin da kasashen Afirka (FOCAC) ta yanar gizo a ranar 18 ga wannan wata, inda bangarori daban daban suka cimma daidaito kan yadda za a gaggauta gina al’ummar Sin da Afirka mai kyakkyawar makoma a sabon zamani, da inganta hadin gwiwar abokantaka a tsakanin kasashe masu tasowa, da kuma kiyaye amfanin dandalin tattaunawar na FOCAC.

A shekarun baya-baya nan, bisa tsarin dandaloli irin su bikin baje kolin kayayyakin da ake shigowa da su cikin kasar Sin, da bikin baje kolin tattalin arziki da cinikayya na kasar Sin da kasashen Afirka, da bikin sayar da kayayyakin Afirka ta intanet, karin kayayyakin Afirka sun shiga kasuwar kasar Sin.

Alkaluman kididdiga na nuna cewa, tun bayan taron kolin dandalin tattaunawar hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka da aka yi a nan birnin Beijing a shekarar 2018, an ba da izinin shigar da kayayyakin amfanin gona da kayayyakin abinci iri 25 daga kasashen Afirka 14 da suka hada da kasashen Kenya, da Afirka ta Kudu, da Benin, da Masar zuwa kasar Sin. Kasar Sin ta kasance kasa ta biyu a duniya wajen sayen kayayyakin amfanin gonan kasashen Afirka.

A shekarar 2021, yawan kudin kayayyakin amfanin gona da kasashen Afirka suka sayar wa kasar Sin ya karu da kashi 18.2 cikin dari bisa na makamancin lokacin shekarar 2020.

Ban da wannan kuma, tun bayan da aka kafa dandalin tattaunawar na FOCAC, tsawon hanyoyin jiragen kasa da kamfanonin Sin suka gina ko gyara a kasashen Afirka ya zarce kilomita dubu 10, tsawon hanyoyin motoci ya kai kimanin kilomita dubu 100, yawan gadoji ya kai kusan dubu daya, yayin da yawan tasoshin jiragen ruwa, ya kai kusan dari daya, da asibitoci da makarantu da dama, da samar da ayyukan yi fiye da miliyan 4 da dubu 500 a kasashen Afirka.

Labarai Masu Nasaba

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Jama’ar kasashen Afirka sun yaba matuka da wadannan nasarori. (Zainab)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Shiga Alhinin Kisan Gillar Da Aka Yi Wa Sheikh Goni Aisami Gashuwa, A Yobe

Next Post

Saboda Girman Haihuwar Annabi (SAW) Aka Rabe Farkon Shekarar Musulunci Da Watan Haihuwarsa

Related

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

8 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

8 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

10 hours ago
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

13 hours ago
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

14 hours ago
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

15 hours ago
Next Post
Saboda Girman Haihuwar Annabi (SAW) Aka Rabe Farkon Shekarar Musulunci Da Watan Haihuwarsa

Saboda Girman Haihuwar Annabi (SAW) Aka Rabe Farkon Shekarar Musulunci Da Watan Haihuwarsa

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.