• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Samun Sakamako Mai Kyau A Hadin Gwiwar Dake Tsakanin Sin Da Afirka

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Ana Samun Sakamako Mai Kyau A Hadin Gwiwar Dake Tsakanin Sin Da Afirka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An gudanar da taron manyan wakilai game da nazarin matakan aiwatar da sakamakon taron ministoci karo na 8 na dandalin tattaunawar hadin gwiwar kasar Sin da kasashen Afirka (FOCAC) ta yanar gizo a ranar 18 ga wannan wata, inda bangarori daban daban suka cimma daidaito kan yadda za a gaggauta gina al’ummar Sin da Afirka mai kyakkyawar makoma a sabon zamani, da inganta hadin gwiwar abokantaka a tsakanin kasashe masu tasowa, da kuma kiyaye amfanin dandalin tattaunawar na FOCAC.

A shekarun baya-baya nan, bisa tsarin dandaloli irin su bikin baje kolin kayayyakin da ake shigowa da su cikin kasar Sin, da bikin baje kolin tattalin arziki da cinikayya na kasar Sin da kasashen Afirka, da bikin sayar da kayayyakin Afirka ta intanet, karin kayayyakin Afirka sun shiga kasuwar kasar Sin.

Alkaluman kididdiga na nuna cewa, tun bayan taron kolin dandalin tattaunawar hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka da aka yi a nan birnin Beijing a shekarar 2018, an ba da izinin shigar da kayayyakin amfanin gona da kayayyakin abinci iri 25 daga kasashen Afirka 14 da suka hada da kasashen Kenya, da Afirka ta Kudu, da Benin, da Masar zuwa kasar Sin. Kasar Sin ta kasance kasa ta biyu a duniya wajen sayen kayayyakin amfanin gonan kasashen Afirka.

A shekarar 2021, yawan kudin kayayyakin amfanin gona da kasashen Afirka suka sayar wa kasar Sin ya karu da kashi 18.2 cikin dari bisa na makamancin lokacin shekarar 2020.

Ban da wannan kuma, tun bayan da aka kafa dandalin tattaunawar na FOCAC, tsawon hanyoyin jiragen kasa da kamfanonin Sin suka gina ko gyara a kasashen Afirka ya zarce kilomita dubu 10, tsawon hanyoyin motoci ya kai kimanin kilomita dubu 100, yawan gadoji ya kai kusan dubu daya, yayin da yawan tasoshin jiragen ruwa, ya kai kusan dari daya, da asibitoci da makarantu da dama, da samar da ayyukan yi fiye da miliyan 4 da dubu 500 a kasashen Afirka.

Labarai Masu Nasaba

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

Jama’ar kasashen Afirka sun yaba matuka da wadannan nasarori. (Zainab)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Shiga Alhinin Kisan Gillar Da Aka Yi Wa Sheikh Goni Aisami Gashuwa, A Yobe

Next Post

Saboda Girman Haihuwar Annabi (SAW) Aka Rabe Farkon Shekarar Musulunci Da Watan Haihuwarsa

Related

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba
Daga Birnin Sin

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

12 minutes ago
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban
Daga Birnin Sin

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

1 hour ago
An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 
Daga Birnin Sin

An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

2 hours ago
Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka
Daga Birnin Sin

Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

4 hours ago
Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya
Daga Birnin Sin

Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya

5 hours ago
Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo
Daga Birnin Sin

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

22 hours ago
Next Post
Saboda Girman Haihuwar Annabi (SAW) Aka Rabe Farkon Shekarar Musulunci Da Watan Haihuwarsa

Saboda Girman Haihuwar Annabi (SAW) Aka Rabe Farkon Shekarar Musulunci Da Watan Haihuwarsa

LABARAI MASU NASABA

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

September 17, 2025
Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

September 17, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

September 17, 2025
Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

September 17, 2025
An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

September 17, 2025
‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

September 17, 2025
Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

September 17, 2025
Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

September 17, 2025
Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya

Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya

September 17, 2025
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.