• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana-wata-ga-wata: Tinubu Ya Bukaci A Gaggauta Cafke Atiku Abubakar Kan Zargin Rashawa

by Abubakar Abba and Khalid Idris Doya
3 years ago
in Siyasa
0
Ana-wata-ga-wata: Tinubu Ya Bukaci A Gaggauta Cafke Atiku Abubakar Kan Zargin Rashawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Alhaji Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, ya yi kira da a gaggauta cafkewa da gurfanar da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar kan zargin baya-bayan da ake yi masa na hada kai da tsohon Shugaban Kasa, Olusegun Obasanjo wajen wawushe dukiyar al’umma a lokacin da suke kan mulki. 

 

LEADERSHIP ta yi tilawar cewa, wani mutum Michael Achimugu, da ya kira kansa tsohon hadimin Atiku, ya sake wani faifan bidiyo inda ke bada cikakken bayanin yadda ya zargi Atiku da yin amfani da kamfanonin da ake kira ‘Special Purpose Vehicles’ (SPVs) wajen amsar cin hanci tare da karkatar da dukiyar jama’a a lokacin da yake matsayin mataimakin shugaban kasa a karkashin mulkin Obasanjo.

  • Wasu Jiga-jigan APC Da Ba A Jin Duriyarsu A Yakin Neman Zaben Tinubu

A cikin bidiyon da ya yadu a kafafen sadarwar zamani, Achimugu ya gargadi ‘yan Nijeriya da kada su zabi Atiku bisa zarge-zargen rashawa. Ya kuma yada sautin murya na muhawararsa da Atiku da wasu shaidu da duk yake son tabbatar wa jama’a zargin da yake yi.

 

Labarai Masu Nasaba

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

Da ya ke bayyana ra’ayinsa kan bayanin na Achimugu a ranar Litinin a Abuja ta bakin kwamitin yakin zaben APC a wani taron manema labarai da suka kira, Tinubu ya hakikance kan cewar a kama Atiku kawai, ya ce, tsohon mataimakin shugaban kasan bai cancanci samun kariya kawai don yana takarar shugaban kasa ba.

 

Babban mai magana da yawun kwamitin yakin zaben Tinubu, Festus Keyamo (SAN) ya ce, dole ne Atiku ya nemi gafara kuma ya yi watsi da muradinsa na neman Shugaban kasa.

 

Keyamo, ya kara da cewa, bai kamata jami’an tsaro su yi wata-wata wajen ganin cafke Atiku, ya ce kada su tsaya tunanin don yana takarar ba za a tuhumeshi ba.

 

Keyamo na cewa, “Sama da mako guda ke nan, ‘yan Nijeriya sun tsunduma cikin mamaki kan bayanin da Mr. Michael Achimugu ya fitar kan hujjojin da ya fitar da ke zarginsa da sama da fadi da dukiyar al’umma ta hanyar amfani da “Special Purpose Vehicles” (SPVs).

 

“Wadannan kamfanonin SPVs da Atiku ya musu rijista lokacin da ya zama mataimakin shugaban kasa tare da amincewar (Shugaban kasa Olusegun Obasanjo) tare da yin amfani da abokansa da makusantansa a matsayin masu hannun jari da daraktocin kamfanin. Kawai sun yi hakan ne da manufar karkatar da duniyar gwamnati ta hanyar amfani da wadannan kamfanonin.

 

“Dukkaninmu za mu iya tunawa lokacin da suke mulki, Shugaban kasa Olusegun Obasanjo da Atiku Abubakar sun gina jami’ar Bells da jami’ar American University bi da bi. Yanzu, mun fahimci inda kudin ya fito.

 

“Mun samu kwararan shaidu daga wajen Mr. Michael Achimugu, kafin mu yi kiran a kama Atiku.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Qin Gang Da Babban Sakataren AL Sun Yi Kira Da A Gaggauta Aiwatar Da Sakamakon Taron Sin Da Kasashen Larabawa

Next Post

Xie Feng: Sin Ta Sha Alwashin Kara Bude Kofa Da Samar Da Damammakin Zurfafa Hadin Gwiwar Cimma Moriyar Juna

Related

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago
Siyasa

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

2 days ago
Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)
Siyasa

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

3 days ago
APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC
Siyasa

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

4 days ago
PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya
Siyasa

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

4 days ago
INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC
Manyan Labarai

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

1 week ago
APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami
Manyan Labarai

APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami

1 week ago
Next Post
Xie Feng: Sin Ta Sha Alwashin Kara Bude Kofa Da Samar Da Damammakin Zurfafa Hadin Gwiwar Cimma Moriyar Juna

Xie Feng: Sin Ta Sha Alwashin Kara Bude Kofa Da Samar Da Damammakin Zurfafa Hadin Gwiwar Cimma Moriyar Juna

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

September 17, 2025
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

September 17, 2025
Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

September 17, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

September 17, 2025
Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

September 17, 2025
An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

September 17, 2025
‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

September 17, 2025
Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

September 17, 2025
Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

September 17, 2025
Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya

Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.