• English
  • Business News
Wednesday, October 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana-wata-ga-wata: Tinubu Ya Bukaci A Gaggauta Cafke Atiku Abubakar Kan Zargin Rashawa

by Abubakar Abba and Khalid Idris Doya
3 years ago
Tinubu

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Alhaji Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, ya yi kira da a gaggauta cafkewa da gurfanar da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar kan zargin baya-bayan da ake yi masa na hada kai da tsohon Shugaban Kasa, Olusegun Obasanjo wajen wawushe dukiyar al’umma a lokacin da suke kan mulki. 

 

LEADERSHIP ta yi tilawar cewa, wani mutum Michael Achimugu, da ya kira kansa tsohon hadimin Atiku, ya sake wani faifan bidiyo inda ke bada cikakken bayanin yadda ya zargi Atiku da yin amfani da kamfanonin da ake kira ‘Special Purpose Vehicles’ (SPVs) wajen amsar cin hanci tare da karkatar da dukiyar jama’a a lokacin da yake matsayin mataimakin shugaban kasa a karkashin mulkin Obasanjo.

  • Wasu Jiga-jigan APC Da Ba A Jin Duriyarsu A Yakin Neman Zaben Tinubu

A cikin bidiyon da ya yadu a kafafen sadarwar zamani, Achimugu ya gargadi ‘yan Nijeriya da kada su zabi Atiku bisa zarge-zargen rashawa. Ya kuma yada sautin murya na muhawararsa da Atiku da wasu shaidu da duk yake son tabbatar wa jama’a zargin da yake yi.

 

LABARAI MASU NASABA

Babu Rikici A Jam’iyyar APC A Nasarawa — Shugaban Jam’iyya

Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

Da ya ke bayyana ra’ayinsa kan bayanin na Achimugu a ranar Litinin a Abuja ta bakin kwamitin yakin zaben APC a wani taron manema labarai da suka kira, Tinubu ya hakikance kan cewar a kama Atiku kawai, ya ce, tsohon mataimakin shugaban kasan bai cancanci samun kariya kawai don yana takarar shugaban kasa ba.

 

Babban mai magana da yawun kwamitin yakin zaben Tinubu, Festus Keyamo (SAN) ya ce, dole ne Atiku ya nemi gafara kuma ya yi watsi da muradinsa na neman Shugaban kasa.

 

Keyamo, ya kara da cewa, bai kamata jami’an tsaro su yi wata-wata wajen ganin cafke Atiku, ya ce kada su tsaya tunanin don yana takarar ba za a tuhumeshi ba.

 

Keyamo na cewa, “Sama da mako guda ke nan, ‘yan Nijeriya sun tsunduma cikin mamaki kan bayanin da Mr. Michael Achimugu ya fitar kan hujjojin da ya fitar da ke zarginsa da sama da fadi da dukiyar al’umma ta hanyar amfani da “Special Purpose Vehicles” (SPVs).

 

“Wadannan kamfanonin SPVs da Atiku ya musu rijista lokacin da ya zama mataimakin shugaban kasa tare da amincewar (Shugaban kasa Olusegun Obasanjo) tare da yin amfani da abokansa da makusantansa a matsayin masu hannun jari da daraktocin kamfanin. Kawai sun yi hakan ne da manufar karkatar da duniyar gwamnati ta hanyar amfani da wadannan kamfanonin.

 

“Dukkaninmu za mu iya tunawa lokacin da suke mulki, Shugaban kasa Olusegun Obasanjo da Atiku Abubakar sun gina jami’ar Bells da jami’ar American University bi da bi. Yanzu, mun fahimci inda kudin ya fito.

 

“Mun samu kwararan shaidu daga wajen Mr. Michael Achimugu, kafin mu yi kiran a kama Atiku.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Babu Rikici A Jam’iyyar APC A Nasarawa — Shugaban Jam’iyya
Siyasa

Babu Rikici A Jam’iyyar APC A Nasarawa — Shugaban Jam’iyya

October 21, 2025
Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu
Siyasa

Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

October 20, 2025
Tsohon Ɗan Majalisar Bayelsa Ya Shawarci Jonathan Ya Guji Neman Takara A 2027
Siyasa

Tsohon Ɗan Majalisar Bayelsa Ya Shawarci Jonathan Ya Guji Neman Takara A 2027

October 17, 2025
Next Post
Xie Feng: Sin Ta Sha Alwashin Kara Bude Kofa Da Samar Da Damammakin Zurfafa Hadin Gwiwar Cimma Moriyar Juna

Xie Feng: Sin Ta Sha Alwashin Kara Bude Kofa Da Samar Da Damammakin Zurfafa Hadin Gwiwar Cimma Moriyar Juna

LABARAI MASU NASABA

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

October 21, 2025
Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

October 21, 2025
Aikin Jinya Kyauta: Gwamnatin Zamfara Ta Kammala Zagaye Na 10 Na Kula Da Marasa Lafiya 3,447

Aikin Jinya Kyauta: Gwamnatin Zamfara Ta Kammala Zagaye Na 10 Na Kula Da Marasa Lafiya 3,447

October 21, 2025
Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba

Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba

October 21, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Gwamna Yusuf Ya Buƙaci Hukumar NBC Da Ta Sa Ido Kan Gidajen Rediyo Da Talabijin Na Yanar Gizo

October 21, 2025
Me Aka Gano Kan Makomar Tattalin Arzikin Kasar Sin Daga Karuwar 5.2% Na Tattalin Arzikinta?

Me Aka Gano Kan Makomar Tattalin Arzikin Kasar Sin Daga Karuwar 5.2% Na Tattalin Arzikinta?

October 21, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Tabbatar Da Yusuf A Matsayin Sabon Shugaban NPC, Wasu 2 A Matsayin Kwamishinoni

October 21, 2025
Jirgin Kasa Mafi Saurin Gudu A Duniya Ya Fara Zirga-Zirgar Gwaji A Sin

Jirgin Kasa Mafi Saurin Gudu A Duniya Ya Fara Zirga-Zirgar Gwaji A Sin

October 21, 2025
Uba Sani Ya Amince Da Biyan Naira Biliyan ₦2.3 Ga Tsofaffin Ma’aikata Da Iyalansu

Ma’aikatan Manyan Makarantu Na Kaduna Sun Dakatar Da Yajin Aiki Yayin Da Gwamna Sani Ya Amince Da Sabon Tsarin Albashi

October 21, 2025
Jami’an Kasashen Afrika Na Koyon Dabarar Yaki Da Talauci Ta Sin A Jihar Ningxia

Jami’an Kasashen Afrika Na Koyon Dabarar Yaki Da Talauci Ta Sin A Jihar Ningxia

October 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.