ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana-wata-ga-wata: Tinubu Ya Bukaci A Gaggauta Cafke Atiku Abubakar Kan Zargin Rashawa

by Abubakar Abba and Khalid Idris Doya
3 years ago
Tinubu

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Alhaji Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, ya yi kira da a gaggauta cafkewa da gurfanar da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar kan zargin baya-bayan da ake yi masa na hada kai da tsohon Shugaban Kasa, Olusegun Obasanjo wajen wawushe dukiyar al’umma a lokacin da suke kan mulki. 

 

LEADERSHIP ta yi tilawar cewa, wani mutum Michael Achimugu, da ya kira kansa tsohon hadimin Atiku, ya sake wani faifan bidiyo inda ke bada cikakken bayanin yadda ya zargi Atiku da yin amfani da kamfanonin da ake kira ‘Special Purpose Vehicles’ (SPVs) wajen amsar cin hanci tare da karkatar da dukiyar jama’a a lokacin da yake matsayin mataimakin shugaban kasa a karkashin mulkin Obasanjo.

ADVERTISEMENT
  • Wasu Jiga-jigan APC Da Ba A Jin Duriyarsu A Yakin Neman Zaben Tinubu

A cikin bidiyon da ya yadu a kafafen sadarwar zamani, Achimugu ya gargadi ‘yan Nijeriya da kada su zabi Atiku bisa zarge-zargen rashawa. Ya kuma yada sautin murya na muhawararsa da Atiku da wasu shaidu da duk yake son tabbatar wa jama’a zargin da yake yi.

 

LABARAI MASU NASABA

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

Da ya ke bayyana ra’ayinsa kan bayanin na Achimugu a ranar Litinin a Abuja ta bakin kwamitin yakin zaben APC a wani taron manema labarai da suka kira, Tinubu ya hakikance kan cewar a kama Atiku kawai, ya ce, tsohon mataimakin shugaban kasan bai cancanci samun kariya kawai don yana takarar shugaban kasa ba.

 

Babban mai magana da yawun kwamitin yakin zaben Tinubu, Festus Keyamo (SAN) ya ce, dole ne Atiku ya nemi gafara kuma ya yi watsi da muradinsa na neman Shugaban kasa.

 

Keyamo, ya kara da cewa, bai kamata jami’an tsaro su yi wata-wata wajen ganin cafke Atiku, ya ce kada su tsaya tunanin don yana takarar ba za a tuhumeshi ba.

 

Keyamo na cewa, “Sama da mako guda ke nan, ‘yan Nijeriya sun tsunduma cikin mamaki kan bayanin da Mr. Michael Achimugu ya fitar kan hujjojin da ya fitar da ke zarginsa da sama da fadi da dukiyar al’umma ta hanyar amfani da “Special Purpose Vehicles” (SPVs).

 

“Wadannan kamfanonin SPVs da Atiku ya musu rijista lokacin da ya zama mataimakin shugaban kasa tare da amincewar (Shugaban kasa Olusegun Obasanjo) tare da yin amfani da abokansa da makusantansa a matsayin masu hannun jari da daraktocin kamfanin. Kawai sun yi hakan ne da manufar karkatar da duniyar gwamnati ta hanyar amfani da wadannan kamfanonin.

 

“Dukkaninmu za mu iya tunawa lokacin da suke mulki, Shugaban kasa Olusegun Obasanjo da Atiku Abubakar sun gina jami’ar Bells da jami’ar American University bi da bi. Yanzu, mun fahimci inda kudin ya fito.

 

“Mun samu kwararan shaidu daga wajen Mr. Michael Achimugu, kafin mu yi kiran a kama Atiku.”

Tinubu
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 
Tinubu
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai Na Aikin Hajjin Bana Na Bauchi Ya Rasu A Saudiyya
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Na Bar Harƙoƙin Siyasa Gaba Ɗaya – Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi, Air Marshal Saddique Baba

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM
Siyasa

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

June 3, 2026
Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
Siyasa

Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada

June 1, 2026
Next Post
Xie Feng: Sin Ta Sha Alwashin Kara Bude Kofa Da Samar Da Damammakin Zurfafa Hadin Gwiwar Cimma Moriyar Juna

Xie Feng: Sin Ta Sha Alwashin Kara Bude Kofa Da Samar Da Damammakin Zurfafa Hadin Gwiwar Cimma Moriyar Juna

LABARAI MASU NASABA

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.