• English
  • Business News
Wednesday, June 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Zargin Dan Majalisar Wakilai Na Gaya/Ajingi/Albasu Da Amfani Da Takardun Karatu Na Bogi

by Muhammad
2 years ago
in Siyasa
0
Ana Zargin Dan Majalisar Wakilai Na Gaya/Ajingi/Albasu Da Amfani Da Takardun Karatu Na Bogi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata kungiya mai suna ‘Gamayyar matasan Gaya’, a karshen makon nan, ta bayyana yadda ta bankado wani dan majalisar wakilai mai wakiltar Gaya/Ajinji/ Albasu a jam’iyyar APC, Abdullahi Mahmud Gaya, yake amfani da takardun shaidar karatu na bogi.

Jaridar Daily Times ta rawaito cewa, Kungiyar ta bayyana haka a cikin wata sanarwa da suka rabawa manema labarai, tare da sa hannun ‘Yan kungiyar baki-daya.

  • ‘Yansanda Sun Cafke Mutane 5 Da Ake Zargi Da Hannu A Kisan Dan Sanata Gaya 
  • Zaben APC: Yanzu Haka ‘Yan Takara Uku Sun Janye Wa Osinbajo —Sanata Gaya

Sanarwar ta ce: “A wani lamari mai ban mamaki da al’ajabi, an gano wani dan siyasa a Kano da yin amfani da takardun karatu na bogi.”

“Dan siyasar wanda ya rike mukami a gwamnatin jiha, yanzu kuma dan majalisa ne mai ci mai wakiltar mazabar Gaya, Ajingi da Albasu, ya yi ikirarin cewa ya samu takardar shaidar kammala karatun ‘Advance Diploma’ a Jami’ar Abuja.

Kungiyar ta yi ikirarin cewa bayan binciken da aka yi an gano cewa ba a bi doka ba wajen kammala karatun kuma takardun shaidar karatun sun nuna yadda dan majalisar ya fadi wani kwas bai gyara jarrabawar ba, amma ba’a san dalilin da ya sa hukumar jami’ar ta kawar da kai ta bayar da sakamakon ba tare da bin tsarin da ya dace ba a shekarar 2001.

Labarai Masu Nasaba

Dalilin Mara Wa Tinubu Baya Ba Tare da Ambaton Shettima Ba – Shugaban APC Na Arewa Maso Gabas

APCn Kaduna Ta Mara Wa Tinubu, Uba Sani Da Kakakin Majalisa Abbas Baya Don Wa’adi Na Biyu

Kungiyar ta ce wasu gungun ‘yan jarida ne da suka gudanar da bincike kan dan siyasar suka gano hakan, inda suka tuntubi jami’ar da tambayoyi domin tabbatar da sahihancin takardar da ya haifar da rudani.

Wakilin LEADERSHIP HAUSA ya tuntubi mai taimaka wa dan majalisar a bangaren yada labarai, Malam Abba Dukawa, ya ce sam maganar zargin da ake wa dan majalisar ba shi da tushe bare makama, kuma su bama su san da wata kungiya mai wannan sunan ba.

Sai dai kuma Jaridar ta Daily Times ta ci gaba da cewa binchiken na duba sahihancin takardun an gano hakan ne biyo bayan gano takardun da dan majalisar ya mika wa hukumar INEC na shaidar kammala makarantar firamare wacce ke dauke da sunan wani daban da nasa sunan, daga takardun da ya mika a fom dinsa mai suna CF001 wadda ita ce takardar rantsuwa da shaida wadda ita Hukumar zaben take amfani da ita wajen tantance ‘yan takara, an gano cewa a nan ma ya mika takardar shaidar kammala karatun firamare ta bogi mai dauke da sunan Abdullahi Mohd yayin da sauran takardunsa ke dauke da sunan Mahmud Abdullahi Gaya.

Kungiyar ta ce bata san dalilin da yasa ya cire takardar shaidar ‘Advance Difloma’ daga wannan fom din na CF001 da ya cike domin yin takara a zaben 2023 ba, wadda ya saka ta yayin da yayi takara a zaben 2019.

Kungiyar ta ce mutane da yawa sun nuna shakku kan aminncewar INEC idan har za a iya amfani da wannan kwamachala akan idonta, wannan kuma ya kawo ayar tambaya game ingancin ilmin da dan siyasar ya yi a baya.

Idan za a iya tunawa an taba samun makamancin irin wannan zargin kan, Salisu Buhari, wanda shi ma ya ahiga zabe ya kuma yi nasara da jabun takardun karatu kamar yadda zargin ya nuna a wancan lokacin kuma lokacin da ya nemi wakilcin majalisar tarayya a karamar hukumar Nasarawa ta Jihar Kano.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Abdullahi Mahmud GayaAlhajin GayaAPCTakardun BogiZargi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Atiku Ya Gana Da Masu Ruwa Da Tsaki Na Jam’iyyar PDP Na Jihar Ribas A Abuja

Next Post

Sharhi:Yadda Amurka Ke Wasa Da Hankalin Al’umma

Related

Sirikin Buhari Ya Fice Daga Jam’iyyar APC A Kaduna
Manyan Labarai

Dalilin Mara Wa Tinubu Baya Ba Tare da Ambaton Shettima Ba – Shugaban APC Na Arewa Maso Gabas

1 day ago
APCn Kaduna Ta Mara Wa Tinubu, Uba Sani Da Kakakin Majalisa Abbas Baya Don Wa’adi Na Biyu
Siyasa

APCn Kaduna Ta Mara Wa Tinubu, Uba Sani Da Kakakin Majalisa Abbas Baya Don Wa’adi Na Biyu

3 days ago
Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6
Labarai

Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6

5 days ago
Zamfara: APC Za Ta Maka PDP A Kotu Kan Zargin Matawalle Da Hannu A Satar Mutane
Manyan Labarai

Zamfara: APC Za Ta Maka PDP A Kotu Kan Zargin Matawalle Da Hannu A Satar Mutane

6 days ago
A Bai Wa Kudu Tikitin Takara A 2027 Ko PDP Ta Ruguje – Wani Jigo A PDP
Siyasa

A Bai Wa Kudu Tikitin Takara A 2027 Ko PDP Ta Ruguje – Wani Jigo A PDP

7 days ago
Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki
Manyan Labarai

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

2 weeks ago
Next Post
Sharhi:Yadda Amurka Ke Wasa Da Hankalin Al’umma

Sharhi:Yadda Amurka Ke Wasa Da Hankalin Al’umma

LABARAI MASU NASABA

PDP Ta Yi Satar Amsa Daga Manufofin Buhari – Tinubu

Gwamnatin Tarayya Za Ta Kwaso ‘Yan Nijeriya Da Suka Maƙale A Isra’ila Da Iran

June 18, 2025
An Ɗaure Wani Mutum Wata 6 Kan Satar Takalma A Masallaci A Kaduna

An Ɗaure Wani Mutum Wata 6 Kan Satar Takalma A Masallaci A Kaduna

June 18, 2025
‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Ƙauyen Kebbi, Sun Kashe Mutane Da Dama

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Ƙauyen Kebbi, Sun Kashe Mutane Da Dama

June 18, 2025
Wani Matashi Ya Ƙone Kansa A Kano Saboda Yana Son Zuwa Aljanna 

Wani Matashi Ya Ƙone Kansa A Kano Saboda Yana Son Zuwa Aljanna 

June 18, 2025
Dalilin Da Ya Sa Sin Ta Samu Bunkasar Tattalin Arziki Mai Dorewa Duk Da Kalubalolin Da Ake Fuskanta A Duniya

Dalilin Da Ya Sa Sin Ta Samu Bunkasar Tattalin Arziki Mai Dorewa Duk Da Kalubalolin Da Ake Fuskanta A Duniya

June 17, 2025
An Kama Mutane 26 Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Kogi

An Kama Mutane 26 Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Kogi

June 17, 2025
Xi Da Shugabannin Kasashe 5 Na Tsakiyar Asiya Sun Halarci Bikin Rattaba Hannu

Xi Da Shugabannin Kasashe 5 Na Tsakiyar Asiya Sun Halarci Bikin Rattaba Hannu

June 17, 2025
Sin Ta Cimma Sabuwar Nasarar Bincike Duniyar Wata

Sin Ta Cimma Sabuwar Nasarar Bincike Duniyar Wata

June 17, 2025
Majalisar Wakilai Ta Fara Binciken Yadda Aka Raba Naira Tiriliyan 1.12 Kan Shirin Lamuni Ga Manoma Da Masana’antu

Majalisar Wakilai Ta Fara Binciken Yadda Aka Raba Naira Tiriliyan 1.12 Kan Shirin Lamuni Ga Manoma Da Masana’antu

June 17, 2025
An Gudanar Da Bikin Mu’amalar Jama’a Da Al’adu A Tsakanin Sin Da Tsakiyar Asiya A Astana

An Gudanar Da Bikin Mu’amalar Jama’a Da Al’adu A Tsakanin Sin Da Tsakiyar Asiya A Astana

June 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.