• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Zargin Dan Majalisar Wakilai Na Gaya/Ajingi/Albasu Da Amfani Da Takardun Karatu Na Bogi

by Muhammad
3 years ago
in Siyasa
0
Ana Zargin Dan Majalisar Wakilai Na Gaya/Ajingi/Albasu Da Amfani Da Takardun Karatu Na Bogi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata kungiya mai suna ‘Gamayyar matasan Gaya’, a karshen makon nan, ta bayyana yadda ta bankado wani dan majalisar wakilai mai wakiltar Gaya/Ajinji/ Albasu a jam’iyyar APC, Abdullahi Mahmud Gaya, yake amfani da takardun shaidar karatu na bogi.

Jaridar Daily Times ta rawaito cewa, Kungiyar ta bayyana haka a cikin wata sanarwa da suka rabawa manema labarai, tare da sa hannun ‘Yan kungiyar baki-daya.

  • ‘Yansanda Sun Cafke Mutane 5 Da Ake Zargi Da Hannu A Kisan Dan Sanata Gaya 
  • Zaben APC: Yanzu Haka ‘Yan Takara Uku Sun Janye Wa Osinbajo —Sanata Gaya

Sanarwar ta ce: “A wani lamari mai ban mamaki da al’ajabi, an gano wani dan siyasa a Kano da yin amfani da takardun karatu na bogi.”

“Dan siyasar wanda ya rike mukami a gwamnatin jiha, yanzu kuma dan majalisa ne mai ci mai wakiltar mazabar Gaya, Ajingi da Albasu, ya yi ikirarin cewa ya samu takardar shaidar kammala karatun ‘Advance Diploma’ a Jami’ar Abuja.

Kungiyar ta yi ikirarin cewa bayan binciken da aka yi an gano cewa ba a bi doka ba wajen kammala karatun kuma takardun shaidar karatun sun nuna yadda dan majalisar ya fadi wani kwas bai gyara jarrabawar ba, amma ba’a san dalilin da ya sa hukumar jami’ar ta kawar da kai ta bayar da sakamakon ba tare da bin tsarin da ya dace ba a shekarar 2001.

Labarai Masu Nasaba

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Kungiyar ta ce wasu gungun ‘yan jarida ne da suka gudanar da bincike kan dan siyasar suka gano hakan, inda suka tuntubi jami’ar da tambayoyi domin tabbatar da sahihancin takardar da ya haifar da rudani.

Wakilin LEADERSHIP HAUSA ya tuntubi mai taimaka wa dan majalisar a bangaren yada labarai, Malam Abba Dukawa, ya ce sam maganar zargin da ake wa dan majalisar ba shi da tushe bare makama, kuma su bama su san da wata kungiya mai wannan sunan ba.

Sai dai kuma Jaridar ta Daily Times ta ci gaba da cewa binchiken na duba sahihancin takardun an gano hakan ne biyo bayan gano takardun da dan majalisar ya mika wa hukumar INEC na shaidar kammala makarantar firamare wacce ke dauke da sunan wani daban da nasa sunan, daga takardun da ya mika a fom dinsa mai suna CF001 wadda ita ce takardar rantsuwa da shaida wadda ita Hukumar zaben take amfani da ita wajen tantance ‘yan takara, an gano cewa a nan ma ya mika takardar shaidar kammala karatun firamare ta bogi mai dauke da sunan Abdullahi Mohd yayin da sauran takardunsa ke dauke da sunan Mahmud Abdullahi Gaya.

Kungiyar ta ce bata san dalilin da yasa ya cire takardar shaidar ‘Advance Difloma’ daga wannan fom din na CF001 da ya cike domin yin takara a zaben 2023 ba, wadda ya saka ta yayin da yayi takara a zaben 2019.

Kungiyar ta ce mutane da yawa sun nuna shakku kan aminncewar INEC idan har za a iya amfani da wannan kwamachala akan idonta, wannan kuma ya kawo ayar tambaya game ingancin ilmin da dan siyasar ya yi a baya.

Idan za a iya tunawa an taba samun makamancin irin wannan zargin kan, Salisu Buhari, wanda shi ma ya ahiga zabe ya kuma yi nasara da jabun takardun karatu kamar yadda zargin ya nuna a wancan lokacin kuma lokacin da ya nemi wakilcin majalisar tarayya a karamar hukumar Nasarawa ta Jihar Kano.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Abdullahi Mahmud GayaAlhajin GayaAPCTakardun BogiZargi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Atiku Ya Gana Da Masu Ruwa Da Tsaki Na Jam’iyyar PDP Na Jihar Ribas A Abuja

Next Post

Sharhi:Yadda Amurka Ke Wasa Da Hankalin Al’umma

Related

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya
Siyasa

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

17 hours ago
INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC
Manyan Labarai

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

3 days ago
APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami
Manyan Labarai

APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami

5 days ago
Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa
Siyasa

Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

1 week ago
Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC
Siyasa

Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

1 week ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Siyasa

Ba Abin Da Zai Hana Tinubu Sake Lashe Zaɓe A 2027 – Jigon APC

2 weeks ago
Next Post
Sharhi:Yadda Amurka Ke Wasa Da Hankalin Al’umma

Sharhi:Yadda Amurka Ke Wasa Da Hankalin Al’umma

LABARAI MASU NASABA

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.