• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Zargin Dan Majalisar Wakilai Na Gaya/Ajingi/Albasu Da Amfani Da Takardun Karatu Na Bogi

by Muhammad
2 years ago
in Siyasa
0
Ana Zargin Dan Majalisar Wakilai Na Gaya/Ajingi/Albasu Da Amfani Da Takardun Karatu Na Bogi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata kungiya mai suna ‘Gamayyar matasan Gaya’, a karshen makon nan, ta bayyana yadda ta bankado wani dan majalisar wakilai mai wakiltar Gaya/Ajinji/ Albasu a jam’iyyar APC, Abdullahi Mahmud Gaya, yake amfani da takardun shaidar karatu na bogi.

Jaridar Daily Times ta rawaito cewa, Kungiyar ta bayyana haka a cikin wata sanarwa da suka rabawa manema labarai, tare da sa hannun ‘Yan kungiyar baki-daya.

  • ‘Yansanda Sun Cafke Mutane 5 Da Ake Zargi Da Hannu A Kisan Dan Sanata Gaya 
  • Zaben APC: Yanzu Haka ‘Yan Takara Uku Sun Janye Wa Osinbajo —Sanata Gaya

Sanarwar ta ce: “A wani lamari mai ban mamaki da al’ajabi, an gano wani dan siyasa a Kano da yin amfani da takardun karatu na bogi.”

“Dan siyasar wanda ya rike mukami a gwamnatin jiha, yanzu kuma dan majalisa ne mai ci mai wakiltar mazabar Gaya, Ajingi da Albasu, ya yi ikirarin cewa ya samu takardar shaidar kammala karatun ‘Advance Diploma’ a Jami’ar Abuja.

Kungiyar ta yi ikirarin cewa bayan binciken da aka yi an gano cewa ba a bi doka ba wajen kammala karatun kuma takardun shaidar karatun sun nuna yadda dan majalisar ya fadi wani kwas bai gyara jarrabawar ba, amma ba’a san dalilin da ya sa hukumar jami’ar ta kawar da kai ta bayar da sakamakon ba tare da bin tsarin da ya dace ba a shekarar 2001.

Labarai Masu Nasaba

Dalilin Gwamnatin Kano Na Haramta Shirye-shiryen Siyasa Kai Tsaye

Gwamna Fintiri Ba Zai Bar PDP Ba – Humwashi

Kungiyar ta ce wasu gungun ‘yan jarida ne da suka gudanar da bincike kan dan siyasar suka gano hakan, inda suka tuntubi jami’ar da tambayoyi domin tabbatar da sahihancin takardar da ya haifar da rudani.

Wakilin LEADERSHIP HAUSA ya tuntubi mai taimaka wa dan majalisar a bangaren yada labarai, Malam Abba Dukawa, ya ce sam maganar zargin da ake wa dan majalisar ba shi da tushe bare makama, kuma su bama su san da wata kungiya mai wannan sunan ba.

Sai dai kuma Jaridar ta Daily Times ta ci gaba da cewa binchiken na duba sahihancin takardun an gano hakan ne biyo bayan gano takardun da dan majalisar ya mika wa hukumar INEC na shaidar kammala makarantar firamare wacce ke dauke da sunan wani daban da nasa sunan, daga takardun da ya mika a fom dinsa mai suna CF001 wadda ita ce takardar rantsuwa da shaida wadda ita Hukumar zaben take amfani da ita wajen tantance ‘yan takara, an gano cewa a nan ma ya mika takardar shaidar kammala karatun firamare ta bogi mai dauke da sunan Abdullahi Mohd yayin da sauran takardunsa ke dauke da sunan Mahmud Abdullahi Gaya.

Kungiyar ta ce bata san dalilin da yasa ya cire takardar shaidar ‘Advance Difloma’ daga wannan fom din na CF001 da ya cike domin yin takara a zaben 2023 ba, wadda ya saka ta yayin da yayi takara a zaben 2019.

Kungiyar ta ce mutane da yawa sun nuna shakku kan aminncewar INEC idan har za a iya amfani da wannan kwamachala akan idonta, wannan kuma ya kawo ayar tambaya game ingancin ilmin da dan siyasar ya yi a baya.

Idan za a iya tunawa an taba samun makamancin irin wannan zargin kan, Salisu Buhari, wanda shi ma ya ahiga zabe ya kuma yi nasara da jabun takardun karatu kamar yadda zargin ya nuna a wancan lokacin kuma lokacin da ya nemi wakilcin majalisar tarayya a karamar hukumar Nasarawa ta Jihar Kano.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Abdullahi Mahmud GayaAlhajin GayaAPCTakardun BogiZargi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Atiku Ya Gana Da Masu Ruwa Da Tsaki Na Jam’iyyar PDP Na Jihar Ribas A Abuja

Next Post

Sharhi:Yadda Amurka Ke Wasa Da Hankalin Al’umma

Related

Dalilin Gwamnatin Kano Na Haramta Shirye-shiryen Siyasa Kai Tsaye
Siyasa

Dalilin Gwamnatin Kano Na Haramta Shirye-shiryen Siyasa Kai Tsaye

1 day ago
Gwamna Fintiri Ba Zai Bar PDP Ba – Humwashi
Siyasa

Gwamna Fintiri Ba Zai Bar PDP Ba – Humwashi

4 days ago
Gwamna Abba Kabir Ya Mayar Wa Da Bappa Bichi Martani
Siyasa

Gwamna Abba Kabir Ya Mayar Wa Da Bappa Bichi Martani

5 days ago
Atiku Ne Rikitacce Ba Tinubu Ba
Labarai

Atiku Ne Rikitacce Ba Tinubu Ba

1 week ago
Mataimakin Gwamnan Neja Ya Ki Halartar Bikin Ranar Ma’aikata, Ana Zargin Akwai Takun Saka
Siyasa

Mataimakin Gwamnan Neja Ya Ki Halartar Bikin Ranar Ma’aikata, Ana Zargin Akwai Takun Saka

1 week ago
‘Yan Siyasa Na Komawa APC Don Buƙatar Kansu, Ba Don Jama’a Ba – Dalung
Siyasa

‘Yan Siyasa Na Komawa APC Don Buƙatar Kansu, Ba Don Jama’a Ba – Dalung

1 week ago
Next Post
Sharhi:Yadda Amurka Ke Wasa Da Hankalin Al’umma

Sharhi:Yadda Amurka Ke Wasa Da Hankalin Al’umma

LABARAI MASU NASABA

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

May 9, 2025
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

May 9, 2025
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

May 9, 2025
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

May 9, 2025
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.