ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharhi:Yadda Amurka Ke Wasa Da Hankalin Al’umma

by CMG Hausa
3 years ago
Amurka

A kwanakin baya, yadda wasu manyan abubuwan da suka faru a kasar Amurka sun jawo hankalin kasa da kasa. Na farko shi ne yadda wani jirgin kasa ya kauce daga layin dogon da yake bi a jihar Ohio ta kasar, na biyu shi ne yadda ake zargin gwamnatin Biden da tsara shirin lalata bututun iskar gas da ke tsakanin Rasha da Turai, na uku kuma shi ne yadda kasar Amurka ta harbo wani balan-balan na kasar Sin da makami mai linzami, sai dai yadda gwamnatin kasar Amurka ke mayar da martani ga batutuwan da ma yadda kafofin watsa labarai na kasar ke ba da rahotanni suna ba jama’a mamaki.

Jirgin kasan da ya kauce daga kan layin dogo yana dauke da sinadarai masu guba, lamarin da ya gurbata muhallin wurin sakamakon yadda sashen kula da al’amuran gaggawa na wurin ya daidaita hadarin, inda mazauna wurin suka fara ciwon kai da nuna sauran alamu na rashin lafiya, baya ga kuma dimbin kifayen da aka gano sun mutu a cikin kogunan wurin.

A sa’i daya kuma, sanannen dan jarida na kasar Seymour Hersh ya fitar da wani rahoton bincike, inda ya zargi gwamnatin Joe Biden da lalata bututun jigilar iskar gas na Nord Stream, don neman cimma moriyar kanta. Wadannan manyan abubuwa ne da suka shafi rayuwar al’ummar kasar Amurka da ma sunan kasar, amma abin mamaki shi ne, gwamnatin Amurka da kuma manyan kafofin yada labarai na kasar duk sun yi shiru, a yayin da kuma suke ta rura wutar batun wai “balan-balan na kasar Sin”.

ADVERTISEMENT

Shin me ya faru ga gwamnatin Amurka da kafofin watsa labarai na kasar?

Me ya sa suke iya ganin balan balan da ta ratsa sararin samaniyar kasar bisa kuskure wanda ke da tsayin mita 18,000 daga doron duniyarmu, amma sun kasa ganin gurbatacciyar hayakin da ke saman jihar Ohio? Me ya sa suke ta rura wutar zancen barazana daga sauran kasashe, amma kuma suka kawar da ido daga hakikanin abin da ke barazana ga lafiyar al’ummar kasar?

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Me ya sa a farkon fashewar bututun Nord Stream, suka daga murya suka ce dole a hukunta wadanda suka aikata laifin, amma kuma suka yi shiru bayan da Seymour Hersh ya fitar da rahotonsa?

A game da wannan, mai fashin baki kan harkokin siyasar kasar Amurka Alex Krainer ya yi nuni da cewa, lokacin da Amurka ke kokarin rura wutar batun “balan-balan na kasar Sin, a daidai lokacin ne da jirgin kasan ya kauce daga kan layin dogo da kuma Seymour Hersh ya fitar da rahotonsa, kuma dalilin da ya sa ta yi hakan shi ne don kawar da hankalin al’umma daga hakikanin matsalolin da suke fuskanta.

To, ashe wasa da hankalin al’umma ke nan Amurka ke yi. (Mai zane:Mustapha Bulama)

Amurka
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa
Daga Birnin Sin

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Next Post
Jami’in MDD: Fasahohin Sin Za Su Taimaka Wa Afirka Tinkarar Matsalar Sauyin Yanayi

Jami’in MDD: Fasahohin Sin Za Su Taimaka Wa Afirka Tinkarar Matsalar Sauyin Yanayi

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.