• English
  • Business News
Monday, June 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Zargin Hukumar Zabe Da Hada Baki Da Gwamna Bagudu Don Shirin Murde Zaben Kebbi Ta Tsakiya

by Bello Hamza
2 years ago
in Labarai
0
Ana Zargin Hukumar Zabe Da Hada Baki Da Gwamna Bagudu Don Shirin Murde Zaben Kebbi Ta Tsakiya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A halin yanzu bayani ya nuna cewa, ba a bayar da sakamakon zaben mazabar kujerar majalisar dattawa na Kebbi ta tsakiya ba saboda rashin samun sakamakon zabe daga mazaba daya daga cikin sakamakon kananan hukumomi 8 na yankin, bayani ya nuna cewa wai jami’in zaben mazabar Marafa wanda ita kadai ake jira ya yi batan dabo.

Wannan tsaikon ya tayar wa da al’ummar yankin hankali inda suke ganin kamar wata kutunguila ce ake yi na murde zaben, musamman ganin ya zuwa yanzu tazarar da ke tsakanin jam’iyyar PDP da jam’iyya mai ci ta APC ya zarce 50,000 abin kuma da ake jira daga mazabar Mafara bai zarce kuri’a 6,000 ba.

A jawabinsa ga manema labarai, jami’in watsa labarai na jami’iyyar PDP, kuma tsohon shugaban hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar Kebbi, Alhaji Sani Dododo, ya yi kira ga shugaban zabe Mahmood Yakubu da dukkan masu ruwa da tsaki, musamman Shugaban Kasa Muhammadu Buhari da su sa baki don ganin an bayyana sakamamon zaben da aka yi don kaucewa tashe-tashen hankula.

Ya kara da cewa, “An kasa fitar da sakamakon zaben kananan hukumomi 7 daga cikin kananan hukumomi 8 dake cikin mazabar Kebbi ta tsakiya, kuma jam’iyar PDP tana da rata daga dukkan kananan hukumomin da aka bayyana sakamakonsu na fiye da kuri’a 50,000, a bayanan da muke samu saboda haka, bamu san dalilin da za a kawo wannan lokaci ba a sanar da sakamakon zaben ba, mu jam’iyyarmu masu bin doka da oda ne” in ji shi.

Ya kuma kara da cewa, “Muna amfani da wannan daman na kira ga shugaban hukumar zabe ta kasa INEC, Farfesa Mahmud Yakubu da shugaban hukumar a jihar Kebbi da kuma shugaban kasa Muhammadu Buhari, musamman ganin bayanan da yake yawan yi na cewa, zai tabbatar da an ba duk wanda ya lashe hakkinsa ba tare da nuna banbancin siyasa ko bangare ba. Muna da tabbacin cewa mun ci zabe saboda haka a zo a sanar mana da nasarar da muka samu, muna da mazabar 8 a wannan yankin an bayar da sakamakon zabe daga mazabu 7 saura gudummar Marafa kadai ta rage kuma mazabar bashi da nisa daga ofishin zabe, bai kai nisan rabin kilomita ba kuma wai an kasa gano jami’in masu tattara sakamakon zaben yankin wai ya bace ba a san inda ya shiga ba, duk da cewa, ita hukumar zabe ta dauke shi aiki, kafin ta dauke shi aiki ya kamata a ce ta sassan cikakken adireshinsa, kuma mutum ne ba aljani ba ne, akan haka muke kira da gaggawa kuma da babbar lafazi a kan cewa a gaggauta fadin sakamakon zaben da aka yi na yankin Kebbi central, kuma du kwai shiri ko kutungwuila, ko wani hauma-hauma da ake shirya muna da labari, duk inda aka kuskura aka kaucewa tsari da aka yi to wallahi za a ga abin da aka biyo baya za a ga abin da zamu yi, inda aka dauki doka a hanun muna zamu dauka, bamu fatan mu yi muna kada ayi mana”.

Labarai Masu Nasaba

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yanzu-yanzu: Almajirin Abduljabbar Kabara Ya Janye Kalamansa Kan Abba Gida-gida

Next Post

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Gabatar Da Jawabi Ga Majalisar Kare Hakkin Dan Adam Ta MDD

Related

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

3 hours ago
Yaushe Za A Dakatar Da Yi Wa `Yan Arewa Kisan Gilla?
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4

4 hours ago
Ganduje Ba Zai Hana Kwankwaso Shiga APC Ba
Labarai

Murabus Ɗin Ganduje: ‘Yan Kwankwasiyya Na Shirin Ɗaukar Wani Mataki

5 hours ago
Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

8 hours ago
Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

17 hours ago
Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu
Labarai

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

19 hours ago
Next Post
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Gabatar Da Jawabi Ga Majalisar Kare Hakkin Dan Adam Ta MDD

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Gabatar Da Jawabi Ga Majalisar Kare Hakkin Dan Adam Ta MDD

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

June 30, 2025
Yaushe Za A Dakatar Da Yi Wa `Yan Arewa Kisan Gilla?

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4

June 30, 2025
Sin Ta Kalubalanci Kasashen Yammacin Duniya Da Su Tuna Da Laifinsu Na Mulkin Mallaka

Cikar MDD Shekara 80: Nasarorinmu Sun Kara Mana Kaimi Da Kyakkyawar Makoma A Nan Gaba

June 30, 2025
Ganduje Ba Zai Hana Kwankwaso Shiga APC Ba

Murabus Ɗin Ganduje: ‘Yan Kwankwasiyya Na Shirin Ɗaukar Wani Mataki

June 30, 2025
Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

June 30, 2025
Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

June 29, 2025
Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

June 29, 2025
An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

June 29, 2025
Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

June 29, 2025
Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.