ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Zargin Hukumar Zabe Da Hada Baki Da Gwamna Bagudu Don Shirin Murde Zaben Kebbi Ta Tsakiya

by Bello Hamza
3 years ago
Hukumar zabe

A halin yanzu bayani ya nuna cewa, ba a bayar da sakamakon zaben mazabar kujerar majalisar dattawa na Kebbi ta tsakiya ba saboda rashin samun sakamakon zabe daga mazaba daya daga cikin sakamakon kananan hukumomi 8 na yankin, bayani ya nuna cewa wai jami’in zaben mazabar Marafa wanda ita kadai ake jira ya yi batan dabo.

Wannan tsaikon ya tayar wa da al’ummar yankin hankali inda suke ganin kamar wata kutunguila ce ake yi na murde zaben, musamman ganin ya zuwa yanzu tazarar da ke tsakanin jam’iyyar PDP da jam’iyya mai ci ta APC ya zarce 50,000 abin kuma da ake jira daga mazabar Mafara bai zarce kuri’a 6,000 ba.

A jawabinsa ga manema labarai, jami’in watsa labarai na jami’iyyar PDP, kuma tsohon shugaban hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar Kebbi, Alhaji Sani Dododo, ya yi kira ga shugaban zabe Mahmood Yakubu da dukkan masu ruwa da tsaki, musamman Shugaban Kasa Muhammadu Buhari da su sa baki don ganin an bayyana sakamamon zaben da aka yi don kaucewa tashe-tashen hankula.

ADVERTISEMENT

Ya kara da cewa, “An kasa fitar da sakamakon zaben kananan hukumomi 7 daga cikin kananan hukumomi 8 dake cikin mazabar Kebbi ta tsakiya, kuma jam’iyar PDP tana da rata daga dukkan kananan hukumomin da aka bayyana sakamakonsu na fiye da kuri’a 50,000, a bayanan da muke samu saboda haka, bamu san dalilin da za a kawo wannan lokaci ba a sanar da sakamakon zaben ba, mu jam’iyyarmu masu bin doka da oda ne” in ji shi.

Ya kuma kara da cewa, “Muna amfani da wannan daman na kira ga shugaban hukumar zabe ta kasa INEC, Farfesa Mahmud Yakubu da shugaban hukumar a jihar Kebbi da kuma shugaban kasa Muhammadu Buhari, musamman ganin bayanan da yake yawan yi na cewa, zai tabbatar da an ba duk wanda ya lashe hakkinsa ba tare da nuna banbancin siyasa ko bangare ba. Muna da tabbacin cewa mun ci zabe saboda haka a zo a sanar mana da nasarar da muka samu, muna da mazabar 8 a wannan yankin an bayar da sakamakon zabe daga mazabu 7 saura gudummar Marafa kadai ta rage kuma mazabar bashi da nisa daga ofishin zabe, bai kai nisan rabin kilomita ba kuma wai an kasa gano jami’in masu tattara sakamakon zaben yankin wai ya bace ba a san inda ya shiga ba, duk da cewa, ita hukumar zabe ta dauke shi aiki, kafin ta dauke shi aiki ya kamata a ce ta sassan cikakken adireshinsa, kuma mutum ne ba aljani ba ne, akan haka muke kira da gaggawa kuma da babbar lafazi a kan cewa a gaggauta fadin sakamakon zaben da aka yi na yankin Kebbi central, kuma du kwai shiri ko kutungwuila, ko wani hauma-hauma da ake shirya muna da labari, duk inda aka kuskura aka kaucewa tsari da aka yi to wallahi za a ga abin da aka biyo baya za a ga abin da zamu yi, inda aka dauki doka a hanun muna zamu dauka, bamu fatan mu yi muna kada ayi mana”.

LABARAI MASU NASABA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

Hukumar zabe
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata

MASU ALAKA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Next Post
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Gabatar Da Jawabi Ga Majalisar Kare Hakkin Dan Adam Ta MDD

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Gabatar Da Jawabi Ga Majalisar Kare Hakkin Dan Adam Ta MDD

LABARAI MASU NASABA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.