ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Zargin Hukumar Zabe Da Hada Baki Da Gwamna Bagudu Don Shirin Murde Zaben Kebbi Ta Tsakiya

by Bello Hamza
3 years ago
Hukumar zabe

A halin yanzu bayani ya nuna cewa, ba a bayar da sakamakon zaben mazabar kujerar majalisar dattawa na Kebbi ta tsakiya ba saboda rashin samun sakamakon zabe daga mazaba daya daga cikin sakamakon kananan hukumomi 8 na yankin, bayani ya nuna cewa wai jami’in zaben mazabar Marafa wanda ita kadai ake jira ya yi batan dabo.

Wannan tsaikon ya tayar wa da al’ummar yankin hankali inda suke ganin kamar wata kutunguila ce ake yi na murde zaben, musamman ganin ya zuwa yanzu tazarar da ke tsakanin jam’iyyar PDP da jam’iyya mai ci ta APC ya zarce 50,000 abin kuma da ake jira daga mazabar Mafara bai zarce kuri’a 6,000 ba.

A jawabinsa ga manema labarai, jami’in watsa labarai na jami’iyyar PDP, kuma tsohon shugaban hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar Kebbi, Alhaji Sani Dododo, ya yi kira ga shugaban zabe Mahmood Yakubu da dukkan masu ruwa da tsaki, musamman Shugaban Kasa Muhammadu Buhari da su sa baki don ganin an bayyana sakamamon zaben da aka yi don kaucewa tashe-tashen hankula.

ADVERTISEMENT

Ya kara da cewa, “An kasa fitar da sakamakon zaben kananan hukumomi 7 daga cikin kananan hukumomi 8 dake cikin mazabar Kebbi ta tsakiya, kuma jam’iyar PDP tana da rata daga dukkan kananan hukumomin da aka bayyana sakamakonsu na fiye da kuri’a 50,000, a bayanan da muke samu saboda haka, bamu san dalilin da za a kawo wannan lokaci ba a sanar da sakamakon zaben ba, mu jam’iyyarmu masu bin doka da oda ne” in ji shi.

Ya kuma kara da cewa, “Muna amfani da wannan daman na kira ga shugaban hukumar zabe ta kasa INEC, Farfesa Mahmud Yakubu da shugaban hukumar a jihar Kebbi da kuma shugaban kasa Muhammadu Buhari, musamman ganin bayanan da yake yawan yi na cewa, zai tabbatar da an ba duk wanda ya lashe hakkinsa ba tare da nuna banbancin siyasa ko bangare ba. Muna da tabbacin cewa mun ci zabe saboda haka a zo a sanar mana da nasarar da muka samu, muna da mazabar 8 a wannan yankin an bayar da sakamakon zabe daga mazabu 7 saura gudummar Marafa kadai ta rage kuma mazabar bashi da nisa daga ofishin zabe, bai kai nisan rabin kilomita ba kuma wai an kasa gano jami’in masu tattara sakamakon zaben yankin wai ya bace ba a san inda ya shiga ba, duk da cewa, ita hukumar zabe ta dauke shi aiki, kafin ta dauke shi aiki ya kamata a ce ta sassan cikakken adireshinsa, kuma mutum ne ba aljani ba ne, akan haka muke kira da gaggawa kuma da babbar lafazi a kan cewa a gaggauta fadin sakamakon zaben da aka yi na yankin Kebbi central, kuma du kwai shiri ko kutungwuila, ko wani hauma-hauma da ake shirya muna da labari, duk inda aka kuskura aka kaucewa tsari da aka yi to wallahi za a ga abin da aka biyo baya za a ga abin da zamu yi, inda aka dauki doka a hanun muna zamu dauka, bamu fatan mu yi muna kada ayi mana”.

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Hukumar zabe
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ƙungiyar Kansilolin APC Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Idan Ba A Daina Zargin Sanata Yari Ba

MASU ALAKA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya
Manyan Labarai

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221
Labarai

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
Next Post
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Gabatar Da Jawabi Ga Majalisar Kare Hakkin Dan Adam Ta MDD

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Gabatar Da Jawabi Ga Majalisar Kare Hakkin Dan Adam Ta MDD

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.