ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Zargin Hukumar Zabe Da Hada Baki Da Gwamna Bagudu Don Shirin Murde Zaben Kebbi Ta Tsakiya

by Bello Hamza
3 years ago
Hukumar zabe

A halin yanzu bayani ya nuna cewa, ba a bayar da sakamakon zaben mazabar kujerar majalisar dattawa na Kebbi ta tsakiya ba saboda rashin samun sakamakon zabe daga mazaba daya daga cikin sakamakon kananan hukumomi 8 na yankin, bayani ya nuna cewa wai jami’in zaben mazabar Marafa wanda ita kadai ake jira ya yi batan dabo.

Wannan tsaikon ya tayar wa da al’ummar yankin hankali inda suke ganin kamar wata kutunguila ce ake yi na murde zaben, musamman ganin ya zuwa yanzu tazarar da ke tsakanin jam’iyyar PDP da jam’iyya mai ci ta APC ya zarce 50,000 abin kuma da ake jira daga mazabar Mafara bai zarce kuri’a 6,000 ba.

A jawabinsa ga manema labarai, jami’in watsa labarai na jami’iyyar PDP, kuma tsohon shugaban hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar Kebbi, Alhaji Sani Dododo, ya yi kira ga shugaban zabe Mahmood Yakubu da dukkan masu ruwa da tsaki, musamman Shugaban Kasa Muhammadu Buhari da su sa baki don ganin an bayyana sakamamon zaben da aka yi don kaucewa tashe-tashen hankula.

ADVERTISEMENT

Ya kara da cewa, “An kasa fitar da sakamakon zaben kananan hukumomi 7 daga cikin kananan hukumomi 8 dake cikin mazabar Kebbi ta tsakiya, kuma jam’iyar PDP tana da rata daga dukkan kananan hukumomin da aka bayyana sakamakonsu na fiye da kuri’a 50,000, a bayanan da muke samu saboda haka, bamu san dalilin da za a kawo wannan lokaci ba a sanar da sakamakon zaben ba, mu jam’iyyarmu masu bin doka da oda ne” in ji shi.

Ya kuma kara da cewa, “Muna amfani da wannan daman na kira ga shugaban hukumar zabe ta kasa INEC, Farfesa Mahmud Yakubu da shugaban hukumar a jihar Kebbi da kuma shugaban kasa Muhammadu Buhari, musamman ganin bayanan da yake yawan yi na cewa, zai tabbatar da an ba duk wanda ya lashe hakkinsa ba tare da nuna banbancin siyasa ko bangare ba. Muna da tabbacin cewa mun ci zabe saboda haka a zo a sanar mana da nasarar da muka samu, muna da mazabar 8 a wannan yankin an bayar da sakamakon zabe daga mazabu 7 saura gudummar Marafa kadai ta rage kuma mazabar bashi da nisa daga ofishin zabe, bai kai nisan rabin kilomita ba kuma wai an kasa gano jami’in masu tattara sakamakon zaben yankin wai ya bace ba a san inda ya shiga ba, duk da cewa, ita hukumar zabe ta dauke shi aiki, kafin ta dauke shi aiki ya kamata a ce ta sassan cikakken adireshinsa, kuma mutum ne ba aljani ba ne, akan haka muke kira da gaggawa kuma da babbar lafazi a kan cewa a gaggauta fadin sakamakon zaben da aka yi na yankin Kebbi central, kuma du kwai shiri ko kutungwuila, ko wani hauma-hauma da ake shirya muna da labari, duk inda aka kuskura aka kaucewa tsari da aka yi to wallahi za a ga abin da aka biyo baya za a ga abin da zamu yi, inda aka dauki doka a hanun muna zamu dauka, bamu fatan mu yi muna kada ayi mana”.

LABARAI MASU NASABA

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Hukumar zabe
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Yadda Oyetola Ya Ƙaddamar Da Babban Taron Ƙungiyar  PMAWCA A Legas
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Lokaci Ya Yi Da Matasan Nijeriya Za Su Ƙwato Ƙasarsu — Kwamred Yahaya Abdullahi
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kamfanin Dangote Na Kara Karfafa Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Jihar Neja

MASU ALAKA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Next Post
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Gabatar Da Jawabi Ga Majalisar Kare Hakkin Dan Adam Ta MDD

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Gabatar Da Jawabi Ga Majalisar Kare Hakkin Dan Adam Ta MDD

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.