• English
  • Business News
Sunday, October 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Zaton Wuta A Makera…

by CMG Hausa
3 years ago
Wuta

A kwanakin baya ne, aka bude taron kasa da kasa kan cutar kanjamau wato AIDS a birnin Montreal na Canada, taron dake zama irinsa mafi girma kan cutar a duniya, baya kasancewarsa wani muhimmin dandali na yayata matakan kariya da magance cutar.

Galibi masana kimiyya da masu fafutuka daga sassa daban-daban na duniya, su kan yi amfani da wannan dama, wajen tattauna batutuwan da suka shafi yaki da cutar ta kanjamau.

  • Mugun Matakin Amurka A Tekun Kudancin Kasar Sin Ba Zai Yi Nasara Ba

Sai dai duk da muhimmancin wannan taro, a bana, daruruwan mahalarta daga nahiyar Afrika, ba su samu damar halarta ba kamar yadda aka tsara, saboda wasu manufofi na nuna wariya wajen bada takardun iznin shiga kasar ta Canada wato visa da gwamnatin kasar Canada ta bullo da su.

Wasu masu ruwa da tsaki kan yaki da cutar kanjamau da suka halarci taro, sun bayyana bacin ransu kan wannan mataki da mai masaukin taron, wato kasar Canada ta dauka. Wai ana zaton wuta a makera, sai ta tashi a masaka.

A baya ana zargin kasashen yamma da nuna wariya da kyama da neman bata sunan kasashe da ma dakushe ci gabansu, sai ga shi irin wannan mummunan dabi’ar ta bulla a kasa kamar Canada.

LABARAI MASU NASABA

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

Wannan ne ma ya sa, masu fafutuka ke cewa, bai kamata a rika gudanar da irin wannan taro mai muhimmanci dake da nufin kare rayuwar al’umma a kasar dake nuna wariyar launin fata ba.

Masu zanga-zanga ma sun bayyana adawa da matakin gwamnatin Canada, na hana daruruwan mahalarta taron shiga kasar, galibinsu daga Afrika, saboda rashin daidaiton da ya kai ga karuwar yaduwar cutar. Suna masu bayyana cewa, ya kamata tarukan duniya kan yaki da cutar kanjamau, su tabbatar da ana damawa da kwararru daga yankunan da suka fi fama da cutar.

Wani abin takaici shi ne, gwamnatin Canada dai ba ta bayyana dalilanta na hana visar shiga kasar ba, amma wasu daga cikin wadanda ta hanawa visar, sun ce wai kasar ba ta yarda cewa, za su koma kasashensu bayan an kammala taron ba. Zato dai zunubi, ko da ya kasance gaskiya.

Masu fashin baki dai na fatan za a daina amfani da wasu matakai marasa dacewa, wajen mayar da hannun agogo baya, a kokarin da ake yi na kiyaye lafiyar al’ummar duniya. (Ibrahim Yaya)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan
Daga Birnin Sin

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 25, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

October 25, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

October 25, 2025
Next Post
Wang Yi Ya Yi Tir Da Matakin Nancy Pelosi Na Ziyartar Yankin Taiwan

Wang Yi Ya Yi Tir Da Matakin Nancy Pelosi Na Ziyartar Yankin Taiwan

LABARAI MASU NASABA

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 25, 2025

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

October 25, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Banki Na Shekarar 2025 Bankin Providus

October 25, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

October 25, 2025
Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

October 25, 2025
An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

October 25, 2025

Daɓid Adeyemi

October 25, 2025
Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

October 25, 2025
Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

October 25, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.