• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Annobar Tura Yara Mata Aikatau!

by Sister Iyami Jalo
3 years ago
in Labarai
0
Annobar Tura Yara Mata Aikatau!
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kadan daga cikin matsalolin dake addabar mata musamman yara, matasa, ita ce tura su aikatau wassu garuruwa ba tare da la’akarin wadanne irin matsaloli za su fuskanta a can ba. 

Iyaye kan tura yara mata wasu garuruwa da sunan neman kudi ko samo abin duniya, wanda kafin a samu yaro namiji daya da aka tura aikatau sai an samu yara mata sama da goma da aka tura, me ya sa?

  • Malam Ina So Na Hadu Da Mijina Na Farko A Aljanna, Ko Zai Yiwu?
  • GORON JUMA’A

Yana da kyau iyaye mata su fahimci cewar ‘ya mace abar tattali ce da kulawa, tana bukatar tallafi fiye da namiji ta kowacce fuska amma iyaye ba sa duba haka.

Wasu iyaye dai bukatarsu a sama musu kudi ta kowacce hanya.

Me ya sa iyaye ke tauye rayuwar ‘ya mace? Me ya sa ba za a ba ta dama ba ta yadda za ta kula da rayuwarta da na yaran da za ta haifa a gaba ba? Inda a ce za a ba wa yara dama a ji ta ra’ayinsu fiye da rabinsu ba wai suna so ba ne ake tura su wannan aikatau din.

Labarai Masu Nasaba

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

Matsalolin Da Tura Yara Mata Aikatau Ke Haifarwa Akwai matsaloli da tura yara mata aikatau ke haifarwa masu tarin yawa amma ga kadan daga cikin su:

1: Yana hana ta neman ilmi.

2: Yana dakushe mata mafarkinta ya hana mata cikar burinta.

3: Yana bata tarbiyya.

4: Yana mayar da ita marar ‘yanci.

5: Yana mayar da ita tamkar baiwa

6: Yana haifar da rashin tausayi a zuciyarta. Ta yadda za ta sa a ranta cewar ba a sonta ya sa aka kai ta wani wuri da sunan aiki wannan dalili sai ya kangarar mata da zuciya.

7: Yana jefa yara harkar sace -sace.

8: Wasu na fadawa harkar zinace-zinace.

9: Karshe wasu su dawo gida da ciki hade da ciwon zamani.

Ina Mafita? 

Mafita a nan ita ce:

1: Iyaye mu sani cewar duk kudin da za a yi nema ta wani gari to ana iya samunsa a gida.

2: Mu tabbata in zamu tura yara aikatau a yi yarjejeniyar ba su damar neman ilmi.

3: A rinka bibiyar halin da suke ciki a kodayaushe.

4: Mu saurare su a lokacin da muka kai musu ziyara ta nan za mu fahimci matsalarsu.

5: Mu rinka tuntubar su ta wayar hannu mu ji labarinsu.

6: Idan sun zo ganin gida mu tabbatar da mun bincike su.

7: Mu sa ido sosai don ganin halayyarsu ba ta canja ba.

8: Idan da hali mu kyale su su yi aikin kusa da mu muna ganin shiga da fitar su.

Shawara

A shawarce yana da kyau iyaye mu sa ni cewar babu alheri wurin tura yara aikatau wasu garuruwa, yara mata da yawa kan fada garari da kuncin rayuwa a lokacin da suka bar gaban iyayensu da sunan neman kudi a wurare dabandabam. Mu sani daraja da mutunci hade da rayuwar yaranmu sun fi mana komai a rayuwa. Iyaye mata a kula da wannan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AikataiFyadeIllaRainoTarbiyyaYara
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yar Shekara 13 Ta Haddace Tare Da Rubuta Alkur’ani A Katsina

Next Post

Neman Illata Kasar Sin Ya Haifar Da Matsalar Tattalin Arziki Ga Amurka

Related

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita
Labarai

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

10 minutes ago
NNPP
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

2 hours ago
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Manyan Labarai

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

4 hours ago
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

5 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Labarai

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

7 hours ago
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye
Labarai

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

9 hours ago
Next Post
Neman Illata Kasar Sin Ya Haifar Da Matsalar Tattalin Arziki Ga Amurka

Neman Illata Kasar Sin Ya Haifar Da Matsalar Tattalin Arziki Ga Amurka

LABARAI MASU NASABA

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

September 18, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

September 18, 2025
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.