ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Annobar Tura Yara Mata Aikatau!

by Sister Iyami Jalo
4 years ago
Aikatau

Kadan daga cikin matsalolin dake addabar mata musamman yara, matasa, ita ce tura su aikatau wassu garuruwa ba tare da la’akarin wadanne irin matsaloli za su fuskanta a can ba. 

Iyaye kan tura yara mata wasu garuruwa da sunan neman kudi ko samo abin duniya, wanda kafin a samu yaro namiji daya da aka tura aikatau sai an samu yara mata sama da goma da aka tura, me ya sa?

  • Malam Ina So Na Hadu Da Mijina Na Farko A Aljanna, Ko Zai Yiwu?
  • GORON JUMA’A

Yana da kyau iyaye mata su fahimci cewar ‘ya mace abar tattali ce da kulawa, tana bukatar tallafi fiye da namiji ta kowacce fuska amma iyaye ba sa duba haka.

ADVERTISEMENT

Wasu iyaye dai bukatarsu a sama musu kudi ta kowacce hanya.

Me ya sa iyaye ke tauye rayuwar ‘ya mace? Me ya sa ba za a ba ta dama ba ta yadda za ta kula da rayuwarta da na yaran da za ta haifa a gaba ba? Inda a ce za a ba wa yara dama a ji ta ra’ayinsu fiye da rabinsu ba wai suna so ba ne ake tura su wannan aikatau din.

LABARAI MASU NASABA

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

Matsalolin Da Tura Yara Mata Aikatau Ke Haifarwa Akwai matsaloli da tura yara mata aikatau ke haifarwa masu tarin yawa amma ga kadan daga cikin su:

1: Yana hana ta neman ilmi.

2: Yana dakushe mata mafarkinta ya hana mata cikar burinta.

3: Yana bata tarbiyya.

4: Yana mayar da ita marar ‘yanci.

5: Yana mayar da ita tamkar baiwa

6: Yana haifar da rashin tausayi a zuciyarta. Ta yadda za ta sa a ranta cewar ba a sonta ya sa aka kai ta wani wuri da sunan aiki wannan dalili sai ya kangarar mata da zuciya.

7: Yana jefa yara harkar sace -sace.

8: Wasu na fadawa harkar zinace-zinace.

9: Karshe wasu su dawo gida da ciki hade da ciwon zamani.

Ina Mafita? 

Mafita a nan ita ce:

1: Iyaye mu sani cewar duk kudin da za a yi nema ta wani gari to ana iya samunsa a gida.

2: Mu tabbata in zamu tura yara aikatau a yi yarjejeniyar ba su damar neman ilmi.

3: A rinka bibiyar halin da suke ciki a kodayaushe.

4: Mu saurare su a lokacin da muka kai musu ziyara ta nan za mu fahimci matsalarsu.

5: Mu rinka tuntubar su ta wayar hannu mu ji labarinsu.

6: Idan sun zo ganin gida mu tabbatar da mun bincike su.

7: Mu sa ido sosai don ganin halayyarsu ba ta canja ba.

8: Idan da hali mu kyale su su yi aikin kusa da mu muna ganin shiga da fitar su.

Shawara

A shawarce yana da kyau iyaye mu sa ni cewar babu alheri wurin tura yara aikatau wasu garuruwa, yara mata da yawa kan fada garari da kuncin rayuwa a lokacin da suka bar gaban iyayensu da sunan neman kudi a wurare dabandabam. Mu sani daraja da mutunci hade da rayuwar yaranmu sun fi mana komai a rayuwa. Iyaye mata a kula da wannan.

Aikatau
Sister Iyami Jalo
+ postsBio
  • Sister Iyami Jalo
    https://hausa.leadership.ng/author/sister-iyami-jalo/
    Hanyoyin Mallakar Zuciyar Iyali Cikin Sauki Ga Magidanta
  • Sister Iyami Jalo
    https://hausa.leadership.ng/author/sister-iyami-jalo/
    Rashin Dacewar Koya Wa ‘Ya’ya Taya Uwa Kishi
  • Sister Iyami Jalo
    https://hausa.leadership.ng/author/sister-iyami-jalo/
    Yadda Za Mu Kula Da Yara Lokacin Sanyi
  • Sister Iyami Jalo
    https://hausa.leadership.ng/author/sister-iyami-jalo/
    Kulawa Da Yara A Lokacin Hunturu

MASU ALAKA

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara
Labarai

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

July 6, 2026
Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi
Labarai

Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

July 6, 2026
Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC
Ra'ayi Riga

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

July 6, 2026
Next Post
Neman Illata Kasar Sin Ya Haifar Da Matsalar Tattalin Arziki Ga Amurka

Neman Illata Kasar Sin Ya Haifar Da Matsalar Tattalin Arziki Ga Amurka

LABARAI MASU NASABA

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

July 6, 2026
Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

July 6, 2026
Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

July 6, 2026
Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

July 6, 2026
FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

July 6, 2026
Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

July 6, 2026
Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

July 6, 2026
Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

July 6, 2026
ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

July 6, 2026
Rundunar Sojin Ruwan Sin Ta Yi Gwajin Makami Mai Linzami Ta Amfani Da Jirgin Ruwa Mai Nutso

Rundunar Sojin Ruwan Sin Ta Yi Gwajin Makami Mai Linzami Ta Amfani Da Jirgin Ruwa Mai Nutso

July 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.