• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

APC Da PDP, Duk Kanwar Ja Ce -Kwankwaso

byYusuf Shuaibu
1 year ago
Kwankwaso

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP a zaben 2023, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya bayyana cewa APC da PDP dan juma ne da dan jummai sun gaza, a yanzu jam’iyyarsa ce kadai mafita ga ‘yan Nijeriya.

Tsohon gwamnan Jihar Kano ya bayyana hakan ne a wurin babban taron jam’iyyar NNPP na kasa da ya gudana a Abuja.

  • Liu Yuxi Ya Halarci Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kan Sin Da Afirka Karo Na Uku
  • Ya Kamata Jama’a Su Hada Kai Don Ciyar Da Nijeriya Gaba – Tinubu

Babban taron jam’iyyar ya samu halartar mambobin kwamitin zartarwa na jam’iyyar da shugabanninta na jihohi 36 ciki har da na Abuja da ‘yan majalisun jihohi, wanda aka tabbatar da zaben Ajuji Ahmed a matsayin mukaddashin shugaban jam’iyyar na kasa tare da tabbatar da kundin tsarin jam’iyyar da kuma sauya alaman tambarin jam’iyyar.

Kwankwaso ya siffanta APC da PDP a matsayin taron tsintsiya babu shara, wanda suka tara jiga-jigan ‘yan siyasa marasa amfani tare da kawo kuncin rayuwa ga ‘yan Nijeriya. Ya ce PDP jam’iyya ce da ta gaza, yayin da a yanzu gazawar APC ya fito kuru-kuru.

Ya tabbatar da cewa NNPP ce jam’iyya daya tilo da take kara bukasa a Nijeriya wacce ta fahimci muhimmancin ilimi wajen kawar da fatara da kuncin rayuwa da kuma yadda za a tsare rayukan da dukiyoyin ‘yan Nijeriya, ta hanyar tabbatar da hadin kai da kawo zaman lafiya da kuma wadata ga daukacin ‘yan Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

“Dukkanmu mun san cewa PDP ta gaza. Mafi yawancinmu mun yanke shawara a tsakanin 2014 da 2015 mu kawo sauyi mai ma’ana. Abun takaicin dai shi ne, mun ga abubuwan da suka faru a tsakanin 2015 har zuwa yau. Wannan babban abun kunya ne ga gwamnatin APC. Saboda haka, mu a wurinmu, mun tabbatar da cewa APC ta gaza. Mun yi imani da cewa wannan kasar tana bukatar samun sauyi daga APC da PDP, kuma jam’iyyar NNPP ce kadai mafita, domin ita ce a yanzu take bunkasa a duk fadin kasar nan.

“Haka kuma na tabbatar da cewa wannan shi ne kyakkyawan fata kamar yadda muka tsaya a yau. Mafi yawancin bangarorin kasar nan, musamman yankin Arewacin Nijeriya, yanki da na fito, mafi yawan mutane an kore su daga gidajensu, sannan an kashe mutane da dama. A yanzu haka wasu suna raywa ne a cikin dazuka sakamakon garkuwa da su da ‘yan bindiga suka yi da kuma sauran ayyukan ta’addanci. Sannan mafi yawancin mutane ba sa damuwa da hakan. Abun sauki ne a yi garkuwa da mutane a gidagensu ko kan hanya ko kuma a kasuwa. Na tabbatar da cewa a kasar nan ne kadai ake irin wannan mummunan dabi’a. Hakkin gwamnati ne ta kare rayuwakan ‘yan kasa da kuma dukiyoyinsu.

“A matsayina na tsohon ministan tsaro kuma babban hafsan tsaro na Jihar Kano tsawon shekara 8 na tabbatar kuna da kayan aiki da jami’an tsaro da za su iya kawo tsaro a kasar nan. Wannan dama ce a gare ni wajen ganin mun hada kai mun yi karfi na ceto Nijeriya. Ina mai tabbatar da cewa za a ci gaba da samun hadin kai a cikin wannan jam’iyyar tamu. Za a ci gaba da yi wa dukkan ‘ya’yan jam’iyyar adalci. Za mu ci gaba da gudanar da zaben fitar da gwani a wannan jam’iyya domin bai wa kowa damar samun matsayi.

“Ina godiya ga dukkaninku da kuka zabe ni a matsayin jagoran jam’iyyar na kasa a jam’iyyarmu. Ina alfahari da hakan. Sannan ina mai tabbatar muku cewa zai yi duk mai yuwuwa wajen tabbatar da cewa wannan jam’iyya ta kara karfi sosai,” in ji Kwankwaso.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

October 3, 2025
Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar
Tambarin Dimokuradiyya

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

October 3, 2025
Yadda Na Kawo Karshen Yajin Aikin ASUU Cikin Kwana Daya – Jonathan
Tambarin Dimokuradiyya

Lalacewar Tsarin Zabe Babbar Barazana Ce Ga Dorewar Dimokuradiyyar Afirka — Jonathan

September 27, 2025
Next Post
‘Yan Majalisa 60 Sun Yi Barazanar Ficewa Daga PDP

'Yan Majalisa 60 Sun Yi Barazanar Ficewa Daga PDP

LABARAI MASU NASABA

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version