• English
  • Business News
Saturday, June 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

APC Da PDP, Duk Kanwar Ja Ce -Kwankwaso

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Kiraye-kirayen Maye Ganduje Da Kwankwaso: Dattawan APC Sun Mayar Da Martani
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP a zaben 2023, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya bayyana cewa APC da PDP dan juma ne da dan jummai sun gaza, a yanzu jam’iyyarsa ce kadai mafita ga ‘yan Nijeriya.

Tsohon gwamnan Jihar Kano ya bayyana hakan ne a wurin babban taron jam’iyyar NNPP na kasa da ya gudana a Abuja.

  • Liu Yuxi Ya Halarci Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kan Sin Da Afirka Karo Na Uku
  • Ya Kamata Jama’a Su Hada Kai Don Ciyar Da Nijeriya Gaba – Tinubu

Babban taron jam’iyyar ya samu halartar mambobin kwamitin zartarwa na jam’iyyar da shugabanninta na jihohi 36 ciki har da na Abuja da ‘yan majalisun jihohi, wanda aka tabbatar da zaben Ajuji Ahmed a matsayin mukaddashin shugaban jam’iyyar na kasa tare da tabbatar da kundin tsarin jam’iyyar da kuma sauya alaman tambarin jam’iyyar.

Kwankwaso ya siffanta APC da PDP a matsayin taron tsintsiya babu shara, wanda suka tara jiga-jigan ‘yan siyasa marasa amfani tare da kawo kuncin rayuwa ga ‘yan Nijeriya. Ya ce PDP jam’iyya ce da ta gaza, yayin da a yanzu gazawar APC ya fito kuru-kuru.

Ya tabbatar da cewa NNPP ce jam’iyya daya tilo da take kara bukasa a Nijeriya wacce ta fahimci muhimmancin ilimi wajen kawar da fatara da kuncin rayuwa da kuma yadda za a tsare rayukan da dukiyoyin ‘yan Nijeriya, ta hanyar tabbatar da hadin kai da kawo zaman lafiya da kuma wadata ga daukacin ‘yan Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

“Dukkanmu mun san cewa PDP ta gaza. Mafi yawancinmu mun yanke shawara a tsakanin 2014 da 2015 mu kawo sauyi mai ma’ana. Abun takaicin dai shi ne, mun ga abubuwan da suka faru a tsakanin 2015 har zuwa yau. Wannan babban abun kunya ne ga gwamnatin APC. Saboda haka, mu a wurinmu, mun tabbatar da cewa APC ta gaza. Mun yi imani da cewa wannan kasar tana bukatar samun sauyi daga APC da PDP, kuma jam’iyyar NNPP ce kadai mafita, domin ita ce a yanzu take bunkasa a duk fadin kasar nan.

“Haka kuma na tabbatar da cewa wannan shi ne kyakkyawan fata kamar yadda muka tsaya a yau. Mafi yawancin bangarorin kasar nan, musamman yankin Arewacin Nijeriya, yanki da na fito, mafi yawan mutane an kore su daga gidajensu, sannan an kashe mutane da dama. A yanzu haka wasu suna raywa ne a cikin dazuka sakamakon garkuwa da su da ‘yan bindiga suka yi da kuma sauran ayyukan ta’addanci. Sannan mafi yawancin mutane ba sa damuwa da hakan. Abun sauki ne a yi garkuwa da mutane a gidagensu ko kan hanya ko kuma a kasuwa. Na tabbatar da cewa a kasar nan ne kadai ake irin wannan mummunan dabi’a. Hakkin gwamnati ne ta kare rayuwakan ‘yan kasa da kuma dukiyoyinsu.

“A matsayina na tsohon ministan tsaro kuma babban hafsan tsaro na Jihar Kano tsawon shekara 8 na tabbatar kuna da kayan aiki da jami’an tsaro da za su iya kawo tsaro a kasar nan. Wannan dama ce a gare ni wajen ganin mun hada kai mun yi karfi na ceto Nijeriya. Ina mai tabbatar da cewa za a ci gaba da samun hadin kai a cikin wannan jam’iyyar tamu. Za a ci gaba da yi wa dukkan ‘ya’yan jam’iyyar adalci. Za mu ci gaba da gudanar da zaben fitar da gwani a wannan jam’iyya domin bai wa kowa damar samun matsayi.

“Ina godiya ga dukkaninku da kuka zabe ni a matsayin jagoran jam’iyyar na kasa a jam’iyyarmu. Ina alfahari da hakan. Sannan ina mai tabbatar muku cewa zai yi duk mai yuwuwa wajen tabbatar da cewa wannan jam’iyya ta kara karfi sosai,” in ji Kwankwaso.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Ya Gana Da Shugaban Kasar Suriname

Next Post

‘Yan Majalisa 60 Sun Yi Barazanar Ficewa Daga PDP

Related

Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

7 days ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

2 weeks ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

3 weeks ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

3 weeks ago
Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

1 month ago
Kwankwaso
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

1 month ago
Next Post
‘Yan Majalisa 60 Sun Yi Barazanar Ficewa Daga PDP

'Yan Majalisa 60 Sun Yi Barazanar Ficewa Daga PDP

LABARAI MASU NASABA

Taron Koli Na Sin Da Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu Zai Ingiza Manufar Kara Dunkulewar Sassan Yankin

Taron Koli Na Sin Da Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu Zai Ingiza Manufar Kara Dunkulewar Sassan Yankin

June 13, 2025
jam'iyyu

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

June 13, 2025
Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai

Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai

June 13, 2025
Babban Jami’in Diflomasiyyar Kasar Sin Ya Yi Kiran Karfafa Alaka Da Afirka

Babban Jami’in Diflomasiyyar Kasar Sin Ya Yi Kiran Karfafa Alaka Da Afirka

June 13, 2025
Xi Ya Yi Kira Da A Kara Azamar Gina Kasa A Gabar Da Ake Bikin Cika Shekaru 120 Da Haihuwar Dan Mazan Jiya Chen Yun

Xi Ya Yi Kira Da A Kara Azamar Gina Kasa A Gabar Da Ake Bikin Cika Shekaru 120 Da Haihuwar Dan Mazan Jiya Chen Yun

June 13, 2025
Pogba Na Shirin Komawa Monaco Bayan Dakatar Da Shi

Pogba Na Shirin Komawa Monaco Bayan Dakatar Da Shi

June 13, 2025
Nijeriya Da Morocco Za Su Sanya Hannu Kan Kulla Yarjejeniyar Aikin Bututun Iskar Gas

Gwamnatin Tarayya Ta Himmatu Wajen Inganta Karfin Sashen Fetur Da Gas Na Cikin Gida

June 13, 2025
Bin Hanya Daya Da Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Muhimmin Mataki Ne Na Ba Da Tabbaci Ga Huldar Ciniki Da Tattalin Arzikin Sin Da Amurka

Bin Hanya Daya Da Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Muhimmin Mataki Ne Na Ba Da Tabbaci Ga Huldar Ciniki Da Tattalin Arzikin Sin Da Amurka

June 13, 2025
Sin Ta Bayyana Adawa Da Keta Hurumin ‘Yanci Tsaro Da Ikon Mulkin Yankunan Iran

Sin Ta Bayyana Adawa Da Keta Hurumin ‘Yanci Tsaro Da Ikon Mulkin Yankunan Iran

June 13, 2025
Gwamnati Ta Yi Karin Haske Kan Biyan Tallafin Rage Radadi Da Mafi Karancin Albashi

Gwamnati Ta Yi Karin Haske Kan Biyan Tallafin Rage Radadi Da Mafi Karancin Albashi

June 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.