ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, June 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

APC Da PDP, Duk Kanwar Ja Ce -Kwankwaso

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Kwankwaso

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP a zaben 2023, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya bayyana cewa APC da PDP dan juma ne da dan jummai sun gaza, a yanzu jam’iyyarsa ce kadai mafita ga ‘yan Nijeriya.

Tsohon gwamnan Jihar Kano ya bayyana hakan ne a wurin babban taron jam’iyyar NNPP na kasa da ya gudana a Abuja.

  • Liu Yuxi Ya Halarci Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kan Sin Da Afirka Karo Na Uku
  • Ya Kamata Jama’a Su Hada Kai Don Ciyar Da Nijeriya Gaba – Tinubu

Babban taron jam’iyyar ya samu halartar mambobin kwamitin zartarwa na jam’iyyar da shugabanninta na jihohi 36 ciki har da na Abuja da ‘yan majalisun jihohi, wanda aka tabbatar da zaben Ajuji Ahmed a matsayin mukaddashin shugaban jam’iyyar na kasa tare da tabbatar da kundin tsarin jam’iyyar da kuma sauya alaman tambarin jam’iyyar.

ADVERTISEMENT

Kwankwaso ya siffanta APC da PDP a matsayin taron tsintsiya babu shara, wanda suka tara jiga-jigan ‘yan siyasa marasa amfani tare da kawo kuncin rayuwa ga ‘yan Nijeriya. Ya ce PDP jam’iyya ce da ta gaza, yayin da a yanzu gazawar APC ya fito kuru-kuru.

Ya tabbatar da cewa NNPP ce jam’iyya daya tilo da take kara bukasa a Nijeriya wacce ta fahimci muhimmancin ilimi wajen kawar da fatara da kuncin rayuwa da kuma yadda za a tsare rayukan da dukiyoyin ‘yan Nijeriya, ta hanyar tabbatar da hadin kai da kawo zaman lafiya da kuma wadata ga daukacin ‘yan Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Zaben Fitar Da Gwani Na APC: Tinubu Zai Shiga Tsakani Wajen Warware Rikicin Jam’iyyar

2027:Gwamnoni Na Fuskantar Turjiya Wajen Gwagwarmayar Kare Kujerunsu Da Kuma Samar Da Magadansu

“Dukkanmu mun san cewa PDP ta gaza. Mafi yawancinmu mun yanke shawara a tsakanin 2014 da 2015 mu kawo sauyi mai ma’ana. Abun takaicin dai shi ne, mun ga abubuwan da suka faru a tsakanin 2015 har zuwa yau. Wannan babban abun kunya ne ga gwamnatin APC. Saboda haka, mu a wurinmu, mun tabbatar da cewa APC ta gaza. Mun yi imani da cewa wannan kasar tana bukatar samun sauyi daga APC da PDP, kuma jam’iyyar NNPP ce kadai mafita, domin ita ce a yanzu take bunkasa a duk fadin kasar nan.

“Haka kuma na tabbatar da cewa wannan shi ne kyakkyawan fata kamar yadda muka tsaya a yau. Mafi yawancin bangarorin kasar nan, musamman yankin Arewacin Nijeriya, yanki da na fito, mafi yawan mutane an kore su daga gidajensu, sannan an kashe mutane da dama. A yanzu haka wasu suna raywa ne a cikin dazuka sakamakon garkuwa da su da ‘yan bindiga suka yi da kuma sauran ayyukan ta’addanci. Sannan mafi yawancin mutane ba sa damuwa da hakan. Abun sauki ne a yi garkuwa da mutane a gidagensu ko kan hanya ko kuma a kasuwa. Na tabbatar da cewa a kasar nan ne kadai ake irin wannan mummunan dabi’a. Hakkin gwamnati ne ta kare rayuwakan ‘yan kasa da kuma dukiyoyinsu.

“A matsayina na tsohon ministan tsaro kuma babban hafsan tsaro na Jihar Kano tsawon shekara 8 na tabbatar kuna da kayan aiki da jami’an tsaro da za su iya kawo tsaro a kasar nan. Wannan dama ce a gare ni wajen ganin mun hada kai mun yi karfi na ceto Nijeriya. Ina mai tabbatar da cewa za a ci gaba da samun hadin kai a cikin wannan jam’iyyar tamu. Za a ci gaba da yi wa dukkan ‘ya’yan jam’iyyar adalci. Za mu ci gaba da gudanar da zaben fitar da gwani a wannan jam’iyya domin bai wa kowa damar samun matsayi.

“Ina godiya ga dukkaninku da kuka zabe ni a matsayin jagoran jam’iyyar na kasa a jam’iyyarmu. Ina alfahari da hakan. Sannan ina mai tabbatar muku cewa zai yi duk mai yuwuwa wajen tabbatar da cewa wannan jam’iyya ta kara karfi sosai,” in ji Kwankwaso.

Kwankwaso
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaben Fitar Da Gwani Na APC: Tinubu Zai Shiga Tsakani Wajen Warware Rikicin Jam’iyyar
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Gwamnoni Na Fuskantar Turjiya Wajen Gwagwarmayar Kare Kujerunsu Da Kuma Samar Da Magadansu
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki

MASU ALAKA

Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Tambarin Dimokuradiyya

Zaben Fitar Da Gwani Na APC: Tinubu Zai Shiga Tsakani Wajen Warware Rikicin Jam’iyyar

June 5, 2026
2027:Gwamnoni Na Fuskantar Turjiya Wajen Gwagwarmayar Kare Kujerunsu Da Kuma Samar Da Magadansu
Tambarin Dimokuradiyya

2027:Gwamnoni Na Fuskantar Turjiya Wajen Gwagwarmayar Kare Kujerunsu Da Kuma Samar Da Magadansu

June 5, 2026
Kwankwaso
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Next Post
‘Yan Majalisa 60 Sun Yi Barazanar Ficewa Daga PDP

'Yan Majalisa 60 Sun Yi Barazanar Ficewa Daga PDP

LABARAI MASU NASABA

Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

June 9, 2026
ADC: Hayatu-Deen Ya Fi Atiku Ƙwarewa Da Gogewa – Babachir

ADC: Hayatu-Deen Ya Fi Atiku Ƙwarewa Da Gogewa – Babachir

June 9, 2026
‘Yansanda Sun Kama Mutum 7 Da Ake Zargin ‘Yan Bindiga Ne A Kebbi

‘Yansanda Sun Kama Mutum 7 Da Ake Zargin ‘Yan Bindiga Ne A Kebbi

June 9, 2026
Legas Ce Ta Samar Da Dangote Da Abdulsamad Ba Kano Ba – Shettima

Legas Ce Ta Samar Da Dangote Da Abdulsamad Ba Kano Ba – Shettima

June 9, 2026
Sojoji

Ilimi Ne Babban Makamin Daƙile Ta’addanci — Ministan Tsaro

June 8, 2026
Sin Da Koriya Ta Arewa Na Fuskantar Sabbin Damammaki Da Kudurori In Ji Shugaba Xi Jinping

Sin Da Koriya Ta Arewa Na Fuskantar Sabbin Damammaki Da Kudurori In Ji Shugaba Xi Jinping

June 8, 2026
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga EU Ta Hada Hannu Da Ita Domin Inganta Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakaninsu

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga EU Ta Hada Hannu Da Ita Domin Inganta Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakaninsu

June 8, 2026
Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

Gwamnatin Borno Ta Musanta Biyan Kuɗin Fansa Domin Kuɓutar da Mutane 360

June 8, 2026
Kasar Sin Ta Fara Wani Aikin Hanyar Ruwa A Kogi Mafi Tsawo Na 3 A Duniya

Kasar Sin Ta Fara Wani Aikin Hanyar Ruwa A Kogi Mafi Tsawo Na 3 A Duniya

June 8, 2026
Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Dattawan Zamfara 50 Yayin Taron Sulhu A Cikin Daji

June 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.