• English
  • Business News
Monday, September 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

APC Da PDP Na Zargin Juna Kan Amfani Da Addini Wajen Neman Nasara A 2027

by Shehu Yahaya
2 hours ago
in Manyan Labarai
0
APC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyyar APC ta zargi jam’iyyar PDP mai mulki a Jihar Filato kan shirin yin amfani da addini don samun nasarar siyasa a zaɓen gwamna na 2027.

Zargin ya fito ne a daidai lokacin da jam’iyyar APC keke ƙoƙarin ƙwace iko a jihar a 2027. Idan za a iya tuna dai a halin hanzu, shugaban jam’iyyar APC, Farfesa Nentawe Yilwatda, ya fito ne daga Jihar Filato, wanda hakan ta ƙara zazzafar siyasar jihar, inda APC ke ƙoƙarin lallai sai ta amshi mulkin jihar a 2027.

APC ta zargi PDP da cewa tana ƙoƙarin raba kan Musulmai a jihar tare da ƴ an asalin da wadɗanda ba ƴ an asalin jihar ba domin ta ci gaba da mulkin jihar ta kowane hali.

  • 2027: Su Wane Ne Ke Tsoron Guguwar Makinde A Jam’iyyar  PDP
  • Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

Muƙaddashin mai magana da yawun APC a jiha, Shittu Bamaiyi, wanda ya yi iƙirarin a cikin wata sanarwa da ya fitar, ya kuma ce PDP tana ƙoƙaƙin yin amfani da wannan dabarar ce saboda ta kusa rasa iko a fagen siyasar jihar.

“Akwai tsananin damuwa da fargabar a cikin harkokin siyasar Jihar Filato, domin kuwa PDP ta zaɓi wasu sabbin dubaru da za su ba ta damar ci gaba da mulki ko da kuwa sun saɓ awa doka.

Labarai Masu Nasaba

Birtaniya Ta Amince Da Kafa Falasɗin A Matsayin Ƙasa

Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban Ƙasa

“A wani ɓangare na wannan dubarar, jam’iyyar a ƙarƙashin kulawar ɗaya daga cikin manyan ma’aikatan gwamnati, ta yi ƙoƙarin shirya zaɓen jagoranci ƙungiyar Musulmai ƴ an asalin Jihar Filato a cibiyar Azi Nyako da ke Dadin-Kowa a garin Jos, wanda daga bayanan da aka samu lamarin ya kasa samun nasara.

“PDP na ganin cewa da wannan dubarar na raba kan Musulmin Jihar Filato za ta iya samun nasara a zaɓen 2027, wanda wannan ka iya kawo rashin jituwa da haɗin kan al’umma, musamman a irin wannan lokaci da ake fama da rikice-rikice addini da ƙabilanci da kuma ayyukan ƴ an ta’adda, wanda hakan bai kamata a siyasantar da addini ba.

“Yadda PDP ke amfani da addini a matsayin hanyar lashe zaɓe, tana sake dawo da amfani da siyasa mara tsafta wajen lashe zaɓen 2027 da kowacce hanya,” in ji mai magana da yawun APC.

Amma shugaban PDP na yankin tsakiyar Nijeriya, Monday Daspan, ya musanta wannan zargin a matsayin wanda ba shi da tushe ballantana makama.

“Bamaiyi ya shigo harkar siyasa ta bayan fage ba hanyar da ya kamata ba. Wannan shi ne dalilin da ya sa hakan ya yi masa sauƙi wajen gwama addini da harkokin siyasa. Mafi yawan waɗanda suka shigo harkar siyasa ta bayan fage ba su da cikakken ƙwarewa wajen yin magana a cikin harkokin siyasar ƙasar nan.

“Mu a matsayinmu, APC ba za su iya daidaita tsakanin mulki da ci gaba ba. Sun yi rashin nasara kan zaɓe kuma suna son danganta shi da wani abu. Matsalar a nan dai ita ce, Gwamna Celeb Mutfwang yana aiki ko kuma ba ya yi? Eh. Shin Lalong ya yi aiki da ya yi? A’a,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 2027APCPDP
ShareTweetSendShare
Previous Post

Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban Ƙasa

Next Post

Birtaniya Ta Amince Da Kafa Falasɗin A Matsayin Ƙasa

Related

Birtaniya Ta Amince Da Kafa Falasɗin A Matsayin Ƙasa
Kasashen Ketare

Birtaniya Ta Amince Da Kafa Falasɗin A Matsayin Ƙasa

1 hour ago
Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban
Manyan Labarai

Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban Ƙasa

2 hours ago
Bayan Nesanta Kanta, Jami’ar European American Ta Yi Wa Rarara Tayin Digiri
Manyan Labarai

Bayan Nesanta Kanta, Jami’ar European American Ta Yi Wa Rarara Tayin Digiri

3 hours ago
SERAP, Amnesty Sun Bukaci Tinubu Ya Janye Ƙarar Da Ya Shigar Kan Sowore, X Da Facebook
Manyan Labarai

SERAP, Amnesty Sun Bukaci Tinubu Ya Janye Ƙarar Da Ya Shigar Kan Sowore, X Da Facebook

7 hours ago
Komai Nisan Dare Gari Zai Waye
Ra'ayi Riga

Komai Nisan Dare Gari Zai Waye

8 hours ago
Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan Arsenal Da Manchester City 
Wasanni

Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan Arsenal Da Manchester City 

10 hours ago
Next Post
Birtaniya Ta Amince Da Kafa Falasɗin A Matsayin Ƙasa

Birtaniya Ta Amince Da Kafa Falasɗin A Matsayin Ƙasa

LABARAI MASU NASABA

Birtaniya Ta Amince Da Kafa Falasɗin A Matsayin Ƙasa

Birtaniya Ta Amince Da Kafa Falasɗin A Matsayin Ƙasa

September 21, 2025
APC

APC Da PDP Na Zargin Juna Kan Amfani Da Addini Wajen Neman Nasara A 2027

September 21, 2025
Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban Ƙasa

September 21, 2025
Li Qiang Ya Gana Da Tawagar Membobin Majalisar Wakilai Ta Amurka

Li Qiang Ya Gana Da Tawagar Membobin Majalisar Wakilai Ta Amurka

September 21, 2025
Bayan Nesanta Kanta, Jami’ar European American Ta Yi Wa Rarara Tayin Digiri

Bayan Nesanta Kanta, Jami’ar European American Ta Yi Wa Rarara Tayin Digiri

September 21, 2025
Masana Sun Yaba Da Shawarar GGI Da Kasar Sin Ta Gabatar A Taron Kara Wa Juna Sani Na CMG 

Masana Sun Yaba Da Shawarar GGI Da Kasar Sin Ta Gabatar A Taron Kara Wa Juna Sani Na CMG 

September 21, 2025
arewa

Lokaci Yayi Da Shugabannin Arewa Za Su Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Yankin –  ACI

September 21, 2025
Yadda Wasu Mata Ke Gwada Mazansu Ta Hanyar Magana Da Su Ta Wasu Hanyoyi Don Sanin Ku Suna Kula Mata

Yadda Wasu Mata Ke Gwada Mazansu Ta Hanyar Magana Da Su Ta Wasu Hanyoyi Don Sanin Ku Suna Kula Mata

September 21, 2025
Ya Kamata Sin Da Amurka Su Hau Turbar Hadin Gwiwa Da Samun Moriyar Juna A Sabon Lokaci

Ya Kamata Sin Da Amurka Su Hau Turbar Hadin Gwiwa Da Samun Moriyar Juna A Sabon Lokaci

September 21, 2025
APC

Mata Ne Ƙashin Bayan Gyaran Duk Wata Al’umma, In Ji  Sheik Shamsudeen

September 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.