ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 22, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

by Abubakar Sulaiman
10 months ago
Gombe

Tsohon mataimakin gwamnan jihar Gombe, Tha’anda Jason Rubainu tare da wani jigo na jam’iyyar PDP, Hon. Jerry Joseph Damara, sun fice daga jam’iyyar PDP zuwa jam’iyyar APC mai mulki.

An karɓe su tare da wasu fitattun ƴan jam’iyyar PDP, mafi yawa daga yankin Gombe ta Kudu, a fadar gwamnati da ke Gombe, inda Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya ya tarɓe su. Rubainu ya kasance mataimakin gwamna a lokacin mulkin tsohon Gwamna Ibrahim Hassan Dankwambo daga 2011 zuwa 2015, yayin da Damara ya bayyana shigarsa APC a matsayin babban sauyi na siyasa a jihar.

  • Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe
  • Bauchi Da Gombe Sun Koka Kan Jinkirin Aikin Haƙo Mai Na Kolmani

Damara, wanda aka san shi a matsayin ɗan kasuwa kuma mai taimakon jama’a, ya ce manufar sa ta sauya sheka ta samo asali ne daga gamsuwa da salon shugabancin Gwamna Yahaya, musamman a fannin ayyukan gine-gine da tsaro. Ya ƙara da cewa bai shigo shi kaɗai ba, ya zo da magoya baya da dama, tare da alƙawarin cikakken goyon baya ga jam’iyyar APC.

ADVERTISEMENT

A nasa jawabin, Gwamna Yahaya ya bayyana wannan sauya sheƙar a matsayin rana ta musamman ga jam’iyyar APC a Gombe da ma ƙasa baki ɗaya. Ya ce samun goyon baya daga Gombe ta Kudu abin da ya ke da matuƙar muhimmanci ne, musamman ganin jam’iyyar bata yi nasara sosai a can a zaɓen da ya gabata ba.

Ya kuma yaba wa Shugaban ƙasa Bola Tinubu bisa ƙirƙirar yanayin siyasa da tattalin arziƙi mai kyau, tare da jinjina masa kan cire tallafin mai da ya kira matakin jarumta da ya taimaka wajen daidaita tattalin arziƙin ƙasa. A kan ayyukansa a jihar, Gwamnan ya ce, “Ayyukan da muke yi a Gombe abubuwa ne da ya kamata an yi su shekaru 30 da suka wuce,” yana mai tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta hanzarta ƙara yin abubuwan ci gaba da haɗa kan jama’a.

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

Mutum 1,000 Daga Jam’iyyar ADC Sun Koma PDP A Jihar Katsina

Gombe
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Mutane 842 Ne Suka Rasa Ransu, Aka Yi Garkuwa Da Sama Da 270 A Watan Mayu – Rahoto
  • Abubakar Sulaiman
    PRP Ta Zargi Kwankwaso Da Saye Fom Ɗin Takarar Jamiyyar
  • Abubakar Sulaiman
    An Ƙaddamar Da Dakarun Tsaron Daji 2,187 A Bauchi
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

MASU ALAKA

ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027
Siyasa

ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

June 21, 2026
Kotun Ƙoli Za Ta Yanke Hukunci Kan Rikicin PDP Da ADC Yau
Siyasa

Mutum 1,000 Daga Jam’iyyar ADC Sun Koma PDP A Jihar Katsina

June 19, 2026
Tinubu
Siyasa

Rashin Tsaro: CUPP Ta Goyi Bayan Kiran Da Aka Yi Wa Tinubu Na Jagoranci Ko Murabus

June 18, 2026
Next Post
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

LABARAI MASU NASABA

Mutane 842 Ne Suka Rasa Ransu, Aka Yi Garkuwa Da Sama Da 270 A Watan Mayu – Rahoto

June 21, 2026
PRP Ta Zargi Kwankwaso Da Saye Fom Ɗin Takarar  Jamiyyar

PRP Ta Zargi Kwankwaso Da Saye Fom Ɗin Takarar Jamiyyar

June 21, 2026
An Ƙaddamar Da Dakarun Tsaron Daji 2,187 A Bauchi

An Ƙaddamar Da Dakarun Tsaron Daji 2,187 A Bauchi

June 21, 2026
An Sanar Da Wadanda Suka Lashe Golden Goblet Na Bikin Fina-Finen Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

An Sanar Da Wadanda Suka Lashe Golden Goblet Na Bikin Fina-Finen Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

June 21, 2026
Cibiyar CBA Ta Kenya Za Ta Yi Hadin Gwiwa Da Wata Cibiyar Sin Wajen Bunkasa Noma Da Cinikayyar Lemar Kwadi

Cibiyar CBA Ta Kenya Za Ta Yi Hadin Gwiwa Da Wata Cibiyar Sin Wajen Bunkasa Noma Da Cinikayyar Lemar Kwadi

June 21, 2026
Wasu Abubuwa Da Ke Sa Maza Hana Mata Fita Unguwa (Uwargida)

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)

June 21, 2026
Kasar Sin Ta Karbi Bakuncin Taron Daidaita Batun Kare Hakkin Dan Adam

Kasar Sin Ta Karbi Bakuncin Taron Daidaita Batun Kare Hakkin Dan Adam

June 21, 2026
Wakilin Sin Ya Yi Jawabi A Taron Majalissar UNHRC

Wakilin Sin Ya Yi Jawabi A Taron Majalissar UNHRC

June 21, 2026
Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

June 21, 2026
Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada

Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada

June 21, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.