• English
  • Business News
Monday, October 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

by Idris Aliyu Daudawa
1 month ago
APC

Jam’iyyar haɗaka ta ADC ta bayyana cewa APC na ƙoƙarin tarwatsa ta ne saboda kar ta ƙwace mulki a 2027, wanda ya sa take janyo rikici da tsorata ‘ya’yan jam’iyyar da take ganin shi ne mafita a gareta.

Idan za a iya tunawa dai ƴan daba sun tarwatsa taron masu ruwa da tsaki na jam’iyyar ADC a Jihar Kaduna a makon da ya gabata.

  • DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur
  • ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro

Haka nan, taron shugabannin ADC a Jihar Legas a ƙarshen mako ya zama tashin hankali bayan an kai hari ga mahalarta taron da ake zargin ‘yan daba ne suka kai hare-hare da nufin tarwatsa taron. Wannan lamari mai tashin hankali ya faru a lokacin da Gbadebo Rhodes-Viɓour, wanda shi ne ɗan takarar gwamna na jam’iyyar LP a Legas a shekarar 2023, ya canza sheka zuwa ADC.

An bayar da rahoton cewa yawancin ‘yan daban siyasa sun mamaye wurin taron a Alimosho, inda za a fara bayyana Rhodes-Viɓour a matsayin sabon mamba na ADC, bayan rufe wuri na asali da aka shirya taron a Lion Field, da jami’an tsaro suka yi.

Mai magana da yawun jam’iyyar ADC, Malam Bolaji Abdullahi, a cikin wata sanarwa da ya fitar, ya ce harin da aka kai a Legas ya nuna irin mulkin zalunci na jam’iyyar da ke mulki wadda ta nuna wa ƴan adawa a cikin makon da ya gabata.

LABARAI MASU NASABA

Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

ADC ta ce, “APC tana tsoron ƙaruwar shaharar ADC a faɗin ƙasar nan ne, kuma yana bayyana cewa shi ne kawai hanyar da za su iya bi wajen tarwatsa ƴan adawa a ƙasar nan.

“An fara ne a Jihar Edo da gargaɗin shugabannin ADC kan ka da su ziyarci jihar, sannan Kogi ta biyo baya, tare da rufe tashar rediyo ta kashin kai a Jihar Neja, kafin ya ƙaru zuwa ga kai hare-haren da aka ɗauki nauyi kan taronmu na Kaduna, sannan kuma da hare-hare a kan ayarin motocin shugabannin ADC a Kebbi.

“Haka kuma an kai hari a wurin taron ADC a Alimosho a Jihar Lagos, wannan yana nuna cewa APC ta ji kunya kuma ba ta girma ko kaɗan. A ƙarƙashin gwamnatin APC, rundunar ‘yansandan Nijeriya ta zama wani sashi nak are jam’iyyar mulki.

“Bisa ga waɗannan hare-haren da ake kai mana, babu wanda zai iya hasashen cewa wannan gwamnati na APC da ke ƙarƙashin shugaban ƙasa Tinubu za ci gaba da zama a kan mulki har na tsawon shekaru 8.

“Yanzu, ƴan daban da APC ta ɗauki nauyinsu sun kai hari a coci. Idan cocin da sauran wuraren ibada ba a ɗauke su a matsayin wuraren da ba za a taɓa iya kai hari ga APC ba, ta yaya jam’iyyar za ta iya tabbatar wa duniya cewa ba gaskiya ba ne ba ta cikin ƙungiyoyin ƴan ta’adda. Bayan haka, harin wuraren ibada shi ne abin da ƴan ta’adda ke yi.”

Duk da haka, ADC ta yi barazanar cewa, “Ba za mu zauna muna kallon ana kai wa shugabanninmu da wuraren taronmu hare-hare ba ƙaƙƙautawa ba. Dole ne mu ɗauki matakin dakatar da lamarin. Cikin gaggawa ba tare da ɓata lokaci ba.”

Amma yake mayar da martani, daraktan yaɗa labarai na APC na ƙasa, Bala Ibrahim, ya karyata wannan zargin, yana cewa jam’iyyar da ke mulki ba ta da hannu wajen kawo rikici a jam’iyyun adawa. Har ila yau, ya ce ADC ba barazana ce ga APC ba, yana mai jaddada cewa jam’iyyar da ke mulki ba ta yarda da duk wani tashin hankali ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta
Siyasa

Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

October 24, 2025
ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa
Siyasa

ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

October 22, 2025
Babu Rikici A Jam’iyyar APC A Nasarawa — Shugaban Jam’iyya
Siyasa

Babu Rikici A Jam’iyyar APC A Nasarawa — Shugaban Jam’iyya

October 21, 2025
Next Post
Likitoci

NARD Ta Janye Yajin Aikin Gargaɗi Da Ta Fara

LABARAI MASU NASABA

Tunawa Da Dawowar Taiwan Kasar Sin Shekaru 80 Da Suka Wuce Yana Da Ma’ana Sosai

Tunawa Da Dawowar Taiwan Kasar Sin Shekaru 80 Da Suka Wuce Yana Da Ma’ana Sosai

October 26, 2025
Matatar Dangote Za Ta Faɗaɗa Ƙarfin Aiki Zuwa Ganga Miliyan 1.4 Kullum

Matatar Dangote Za Ta Faɗaɗa Ƙarfin Aiki Zuwa Ganga Miliyan 1.4 Kullum

October 26, 2025
Kara Bude Kofofin Sin Zai Samar Da Karin Gajiya A Fannin Bunkasar Duniya

Kara Bude Kofofin Sin Zai Samar Da Karin Gajiya A Fannin Bunkasar Duniya

October 26, 2025
“Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”

“Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”

October 26, 2025
Ya Zuwa Satumban Bana Adadin Lantarki Da Sin Ta Samar Ya Karu Da Kaso 17.5%

Ya Zuwa Satumban Bana Adadin Lantarki Da Sin Ta Samar Ya Karu Da Kaso 17.5%

October 26, 2025
Dalilin Da Suka Sa Hisbah Ta Dakatar Da Auren Ƴan TikTok A Kano

Dalilin Da Suka Sa Hisbah Ta Dakatar Da Auren Ƴan TikTok A Kano

October 26, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Ma’aikacin Gwamnati Na Shekarar 2025, Dakta Zacch Adedeji

October 26, 2025
An Yi Taron Tattaunawa Mai Taken “Shugabancin Duniya Da Samun Wadata Tare A Yankin Asiya Da Pasifik” A Beijing

An Yi Taron Tattaunawa Mai Taken “Shugabancin Duniya Da Samun Wadata Tare A Yankin Asiya Da Pasifik” A Beijing

October 26, 2025
Sin Da Amurka Sun Cimma Matsaya Dangane Da Tsare-Tsaren Warware Batutuwan Cinikayya Da Suke Mayar Da Hankali A Kai

Sin Da Amurka Sun Cimma Matsaya Dangane Da Tsare-Tsaren Warware Batutuwan Cinikayya Da Suke Mayar Da Hankali A Kai

October 26, 2025
Sharhi: Wannan Manufar Sin Za Ta Sa Kaimin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

Sharhi: Wannan Manufar Sin Za Ta Sa Kaimin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

October 26, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.