• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

by Idris Aliyu Daudawa
2 hours ago
in Siyasa
0
APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyyar haɗaka ta ADC ta bayyana cewa APC na ƙoƙarin tarwatsa ta ne saboda kar ta ƙwace mulki a 2027, wanda ya sa take janyo rikici da tsorata ‘ya’yan jam’iyyar da take ganin shi ne mafita a gareta.

Idan za a iya tunawa dai ƴan daba sun tarwatsa taron masu ruwa da tsaki na jam’iyyar ADC a Jihar Kaduna a makon da ya gabata.

  • DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur
  • ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro

Haka nan, taron shugabannin ADC a Jihar Legas a ƙarshen mako ya zama tashin hankali bayan an kai hari ga mahalarta taron da ake zargin ‘yan daba ne suka kai hare-hare da nufin tarwatsa taron. Wannan lamari mai tashin hankali ya faru a lokacin da Gbadebo Rhodes-Viɓour, wanda shi ne ɗan takarar gwamna na jam’iyyar LP a Legas a shekarar 2023, ya canza sheka zuwa ADC.

An bayar da rahoton cewa yawancin ‘yan daban siyasa sun mamaye wurin taron a Alimosho, inda za a fara bayyana Rhodes-Viɓour a matsayin sabon mamba na ADC, bayan rufe wuri na asali da aka shirya taron a Lion Field, da jami’an tsaro suka yi.

Mai magana da yawun jam’iyyar ADC, Malam Bolaji Abdullahi, a cikin wata sanarwa da ya fitar, ya ce harin da aka kai a Legas ya nuna irin mulkin zalunci na jam’iyyar da ke mulki wadda ta nuna wa ƴan adawa a cikin makon da ya gabata.

Labarai Masu Nasaba

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

ADC ta ce, “APC tana tsoron ƙaruwar shaharar ADC a faɗin ƙasar nan ne, kuma yana bayyana cewa shi ne kawai hanyar da za su iya bi wajen tarwatsa ƴan adawa a ƙasar nan.

“An fara ne a Jihar Edo da gargaɗin shugabannin ADC kan ka da su ziyarci jihar, sannan Kogi ta biyo baya, tare da rufe tashar rediyo ta kashin kai a Jihar Neja, kafin ya ƙaru zuwa ga kai hare-haren da aka ɗauki nauyi kan taronmu na Kaduna, sannan kuma da hare-hare a kan ayarin motocin shugabannin ADC a Kebbi.

“Haka kuma an kai hari a wurin taron ADC a Alimosho a Jihar Lagos, wannan yana nuna cewa APC ta ji kunya kuma ba ta girma ko kaɗan. A ƙarƙashin gwamnatin APC, rundunar ‘yansandan Nijeriya ta zama wani sashi nak are jam’iyyar mulki.

“Bisa ga waɗannan hare-haren da ake kai mana, babu wanda zai iya hasashen cewa wannan gwamnati na APC da ke ƙarƙashin shugaban ƙasa Tinubu za ci gaba da zama a kan mulki har na tsawon shekaru 8.

“Yanzu, ƴan daban da APC ta ɗauki nauyinsu sun kai hari a coci. Idan cocin da sauran wuraren ibada ba a ɗauke su a matsayin wuraren da ba za a taɓa iya kai hari ga APC ba, ta yaya jam’iyyar za ta iya tabbatar wa duniya cewa ba gaskiya ba ne ba ta cikin ƙungiyoyin ƴan ta’adda. Bayan haka, harin wuraren ibada shi ne abin da ƴan ta’adda ke yi.”

Duk da haka, ADC ta yi barazanar cewa, “Ba za mu zauna muna kallon ana kai wa shugabanninmu da wuraren taronmu hare-hare ba ƙaƙƙautawa ba. Dole ne mu ɗauki matakin dakatar da lamarin. Cikin gaggawa ba tare da ɓata lokaci ba.”

Amma yake mayar da martani, daraktan yaɗa labarai na APC na ƙasa, Bala Ibrahim, ya karyata wannan zargin, yana cewa jam’iyyar da ke mulki ba ta da hannu wajen kawo rikici a jam’iyyun adawa. Har ila yau, ya ce ADC ba barazana ce ga APC ba, yana mai jaddada cewa jam’iyyar da ke mulki ba ta yarda da duk wani tashin hankali ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ADCAPCTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

Next Post

NARD Ta Janye Yajin Aikin Gargaɗi Da Ta Fara

Related

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya
Siyasa

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

1 day ago
INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC
Manyan Labarai

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

4 days ago
APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami
Manyan Labarai

APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami

5 days ago
Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa
Siyasa

Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

1 week ago
Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC
Siyasa

Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

1 week ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Siyasa

Ba Abin Da Zai Hana Tinubu Sake Lashe Zaɓe A 2027 – Jigon APC

2 weeks ago
Next Post
Likitoci

NARD Ta Janye Yajin Aikin Gargaɗi Da Ta Fara

LABARAI MASU NASABA

Likitoci

NARD Ta Janye Yajin Aikin Gargaɗi Da Ta Fara

September 14, 2025
APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

September 14, 2025
An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

September 14, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.