• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Arsenal Ta Nuna Sha’awar Daukar Osimhen Idan Ya Yanke Shawarar Barin Napoli

by Rabilu Sanusi Bena
2 years ago
in Wasanni
0
Arsenal Ta Nuna Sha’awar Daukar Osimhen Idan Ya Yanke Shawarar Barin Napoli
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An bai wa Arsenal damar sayen dan wasan gaba na Napoli Victor Osimhen a kasuwar musayar ‘yan wasa, amma hakan zai sa ta rasa daya daga cikin manyan ‘yan wasanta Gabriel Jeauy.

Hakan na zuwa ne yayin da ake ci gaba da alakanta Gunners da karfafa zabin ‘yan wasan gabanta tare da Victor Osimhen a kasuwar musayar ‘yan wasa. Biyo bayan kashe fam miliyan 200 da suka yi a kasuwar saye da sayar da ‘yan wasa ta bazara, har yanzu akwai bukatar kungiyar da ke Arewacin Landan ta samu ‘yan wasan da suka kware wajen cin kwallaye.

  • Manchester United Zata Sayar Da Kashi 25 Na Kungiyar Akan Yuro Biliyan 1.3
  • An Bude Baje Kolin Canton Karo Na 134 A Guangzhou

Duk da cewa suna matsayi na biyu kuma har yanzu ba doke su ba a gasar Premier ta bana ba Arsenal na neman ganin ta tabuka abin azo a gani a wannan kakar. Gabriel Jesus da Eddie Nketiah su ne yan wasa masu zura kwallaye da Arsenal ta dogara da shi amma kuma har yanzu kwallaye uku kawai suka jefa su duka biyun abin da ya sa koci Arteta ke ganin akwai bukatar samun wanda zai jefa ma kungiyar kwallaye.

An alakanta Iban Toney na Brentford da kuma Ollie Watkins na Aston Billa duk da cewa ya rattaba hannu kan wata sabuwar yarjejeniya a Billa Park.

Sai kuma Osimhen, wanda ya kasance zabi mafi tsada amma wanda zai iya samuwa nan ba da jimawa ba.

Labarai Masu Nasaba

Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan El Classico Na Yau

Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

An ci gaba da yayata rade-radin cewa dan wasan na Nijeriya zai rattaba hannu a wani sabon kwantiragi a Napoli,sai dai al’amura sun yi tsami tsakaninsa da masu rike da kofin na Italiya a ‘yan makonnin da suka gabata.

Abin da ya sa wakilin Osimhen ya yi barazanar daukar matakin shari’a a kan kulob din saboda bidiyon da aka yada a shafukan sada zumunta game da tauraron.

Hakan dai ya kara tayar da hankali kan batun ficewarsa daga kungiyar kuma mai yiyuwa ne Arsenal ta dauko shi idan ya yanke shawarar barin Italiya. Hakan na iya faruwa a cikin watan Janairu domin Napoli ta fara neman wanda zai maye gurbin Osimhem kuma yana iya zama Gabriel Jesus na Arsenal wanda ka iya zama wani bangare na yarjejeniyar musaya.

Jesus na iya taka rawar gani a Napoli idan aka yi la’akari da muhimmancin dan wasan na Brazil tun da ya koma kungiyar daga Manchester City a bazarar da ta wuce.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ArsenalHazardOsimhen
ShareTweetSendShare
Previous Post

CMG Da Kafofin Watsa Labaran Afirka Sun Fitar Da Shawarar Aiki Kan Ziri Daya Da Hanya Daya

Next Post

Manufar Kafa Kasashe Biyu Hanya Ce Daya Tilo Ta Warware Rikicin Palesdinu Da Isra’ila

Related

Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan El Classico Na Yau
Wasanni

Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan El Classico Na Yau

3 days ago
Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 
Wasanni

Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

3 days ago
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa
Manyan Labarai

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

6 days ago
Zamalek Ta Sallami Tsohon Kocin Super Eagles, Peseiro
Wasanni

Zamalek Ta Sallami Tsohon Kocin Super Eagles, Peseiro

6 days ago
PSG Ta Yi Waje Rod Da Arsenal A Gasar Zakarun Turai 
Wasanni

PSG Ta Yi Waje Rod Da Arsenal A Gasar Zakarun Turai 

7 days ago
UEFA: Inter Milan Ta Yi Wa Barcelona Kancal
Wasanni

UEFA: An Kai Ruwa Rana Yayin Da Inter Ta Koro Barcelona Gida

1 week ago
Next Post
Manufar Kafa Kasashe Biyu Hanya Ce Daya Tilo Ta Warware Rikicin Palesdinu Da Isra’ila

Manufar Kafa Kasashe Biyu Hanya Ce Daya Tilo Ta Warware Rikicin Palesdinu Da Isra’ila

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

May 14, 2025
Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

May 14, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

May 14, 2025
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

May 14, 2025
Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

May 14, 2025
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.