• English
  • Business News
Friday, June 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Arsenal Ta Nuna Sha’awar Daukar Osimhen Idan Ya Yanke Shawarar Barin Napoli

by Rabilu Sanusi Bena
2 years ago
in Wasanni
0
Arsenal Ta Nuna Sha’awar Daukar Osimhen Idan Ya Yanke Shawarar Barin Napoli
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An bai wa Arsenal damar sayen dan wasan gaba na Napoli Victor Osimhen a kasuwar musayar ‘yan wasa, amma hakan zai sa ta rasa daya daga cikin manyan ‘yan wasanta Gabriel Jeauy.

Hakan na zuwa ne yayin da ake ci gaba da alakanta Gunners da karfafa zabin ‘yan wasan gabanta tare da Victor Osimhen a kasuwar musayar ‘yan wasa. Biyo bayan kashe fam miliyan 200 da suka yi a kasuwar saye da sayar da ‘yan wasa ta bazara, har yanzu akwai bukatar kungiyar da ke Arewacin Landan ta samu ‘yan wasan da suka kware wajen cin kwallaye.

  • Manchester United Zata Sayar Da Kashi 25 Na Kungiyar Akan Yuro Biliyan 1.3
  • An Bude Baje Kolin Canton Karo Na 134 A Guangzhou

Duk da cewa suna matsayi na biyu kuma har yanzu ba doke su ba a gasar Premier ta bana ba Arsenal na neman ganin ta tabuka abin azo a gani a wannan kakar. Gabriel Jesus da Eddie Nketiah su ne yan wasa masu zura kwallaye da Arsenal ta dogara da shi amma kuma har yanzu kwallaye uku kawai suka jefa su duka biyun abin da ya sa koci Arteta ke ganin akwai bukatar samun wanda zai jefa ma kungiyar kwallaye.

An alakanta Iban Toney na Brentford da kuma Ollie Watkins na Aston Billa duk da cewa ya rattaba hannu kan wata sabuwar yarjejeniya a Billa Park.

Sai kuma Osimhen, wanda ya kasance zabi mafi tsada amma wanda zai iya samuwa nan ba da jimawa ba.

Labarai Masu Nasaba

Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi

An ci gaba da yayata rade-radin cewa dan wasan na Nijeriya zai rattaba hannu a wani sabon kwantiragi a Napoli,sai dai al’amura sun yi tsami tsakaninsa da masu rike da kofin na Italiya a ‘yan makonnin da suka gabata.

Abin da ya sa wakilin Osimhen ya yi barazanar daukar matakin shari’a a kan kulob din saboda bidiyon da aka yada a shafukan sada zumunta game da tauraron.

Hakan dai ya kara tayar da hankali kan batun ficewarsa daga kungiyar kuma mai yiyuwa ne Arsenal ta dauko shi idan ya yanke shawarar barin Italiya. Hakan na iya faruwa a cikin watan Janairu domin Napoli ta fara neman wanda zai maye gurbin Osimhem kuma yana iya zama Gabriel Jesus na Arsenal wanda ka iya zama wani bangare na yarjejeniyar musaya.

Jesus na iya taka rawar gani a Napoli idan aka yi la’akari da muhimmancin dan wasan na Brazil tun da ya koma kungiyar daga Manchester City a bazarar da ta wuce.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ArsenalHazardOsimhen
ShareTweetSendShare
Previous Post

CMG Da Kafofin Watsa Labaran Afirka Sun Fitar Da Shawarar Aiki Kan Ziri Daya Da Hanya Daya

Next Post

Manufar Kafa Kasashe Biyu Hanya Ce Daya Tilo Ta Warware Rikicin Palesdinu Da Isra’ila

Related

Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr
Wasanni

Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

1 day ago
Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi
Wasanni

Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi

2 days ago
Manchester United Za Ta Biya Fam Miliyan 60 Don Ɗaukar Mbeumo Daga Brentford
Wasanni

Manchester United Za Ta Biya Fam Miliyan 60 Don Ɗaukar Mbeumo Daga Brentford

3 days ago
Rashford Na Fatan Buga Ƙwallo Tare Da Lamine Yamal A Barcelona
Wasanni

Rashford Na Fatan Buga Ƙwallo Tare Da Lamine Yamal A Barcelona

4 days ago
Bernado Silba Ya Zama Sabon Kyaftin Din Manchester City 
Wasanni

Bernado Silba Ya Zama Sabon Kyaftin Din Manchester City 

5 days ago
Liverpool Za Ta Kece Raini Da Bournemouth, Arsena Za Ta Bakunci Man Utd A Wasan Mako Na Firimiya Ta Baɗi
Wasanni

Liverpool Za Ta Kece Raini Da Bournemouth, Arsena Za Ta Bakunci Man Utd A Wasan Mako Na Firimiya Ta Baɗi

5 days ago
Next Post
Manufar Kafa Kasashe Biyu Hanya Ce Daya Tilo Ta Warware Rikicin Palesdinu Da Isra’ila

Manufar Kafa Kasashe Biyu Hanya Ce Daya Tilo Ta Warware Rikicin Palesdinu Da Isra’ila

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada

June 26, 2025
Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

June 26, 2025
An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome

An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome

June 26, 2025
NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

June 26, 2025
Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Ba Da Gudunmuwa Ga Habakar Tattalin Arzikin Duniya

Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Ba Da Gudunmuwa Ga Habakar Tattalin Arzikin Duniya

June 26, 2025
Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

June 26, 2025
Afirka CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwa Kan Kiwon Lafiya Da Kasar Sin

Afirka CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwa Kan Kiwon Lafiya Da Kasar Sin

June 26, 2025
Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji

Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji

June 26, 2025
An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” A Italiya

An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” A Italiya

June 26, 2025
Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

June 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.