• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Asirin Amurka A Fannin Tada “Yakin Hakkin Dan Adam” A Duniya

by CGTN Hausa and Sulaiman
9 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Asirin Amurka A Fannin Tada “Yakin Hakkin Dan Adam” A Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Zuwa yau 9 ga watan Oktoba aka cika wata daya da gudanar da taro na 57 na kwamitin kare hakkin dan Adam na Majalisar Dinkin Duniya, inda kasashe sama da 100 suka bayyana goyon bayansu ga kasar Sin ta hanyoyin gabatar da jawabi tare ko daya bayan daya, wajen jaddada cewa, harkokin Xinjiang, da Hong Kong, da Xizang(Tibet), harkokin cikin gida ne na kasar Sin, kuma bai kamata Amurka ta yi shisshigi a ciki ba. Al’amarin da ya shaida cewa, yunkurin Amurka da sauran wasu kasashe ‘yan kalilan na yammacin duniya na siyasantar da batun hakkin dan Adam, ba zai samu nasara ba.

 

Amurka ta kawar da ido daga matsalolin da ita kanta take fuskanta ta fannin kare hakkin Adam, kuma tana fakewa da batun hakkin dan Adam wajen matsawa sauran kasashe lamba, gami da nuna fin karfi a duniya.

  • Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Mara Baya Ga Kasashen Yankin Manyan Tafkunan Afirka Don Karfafa Hadin Gwiwa
  • Xi Jinping Ya Karfafawa Kungiyar Red Cross Ta Sin Gwiwar Karfafa Ayyukan Jin Kai

Domin tsoma baki cikin harkokin cikin gidan sauran kasashe, abu na farko da Amurka ta kan yi, shi ne kirkiro “laifin da ya shafi hakkin dan Adam”. Bari mu dauki kasar Venezuela a matsayin misali. A ’yan shekarun nan, bisa hujjar wai Venezuela ta aikata laifi a fannin kare hakkin dan Adam, Amurka ta fadada kakaba mata takunkumin tattalin arziki, al’amarin da ya haifar wa Venezuela matsalolin tattalin arziki da jin kai da kuma ci gaba.

 

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

Baya ga gwamnati da kafafen yada labarai, wani muhimmin abu da ya taka muhimmiyar rawa a cikin “yakin hakkin dan Adam” da Amurka ta tayar a sauran kasashe, shi ne NGO, wato kungiyoyin da ba na gwamnati ba. Wasu kungiyoyin da ba na gwamnati ba a Amurka, wadanda suka fake da sunan kare “demokuradiyya” da “hakkin dan Adam”, sun yi yunkurin rura wutar rikicin kawo baraka, da kulla makiricin tada rikicin siyasa, da shirga karya da sauransu a sassan kasa da kasa.

 

A Majalisar Dinkin Duniya kuwa, Amurka ta kan bada shawarar zartas da kudurorin kasa iri-iri ta hanyar fakewa da batun hakkin Adam, inda ta kan nuna yatsa ga wasu kasashe masu tasowa, da matsa musu lamba a fannin siyasa, kana ta kan yi yunkurin kawo cikas ga wasu batutuwan gaggawa da suka shafi jin kai.

 

Akasarin kasashe masu tsayawa kan adalci da gaskiya sun riga sun fahimci wayon Amurka, wato yunkurin da take na yin shisshigi cikin harkokin cikin gidan kasar Sin da na sauran kasashe masu tasowa, ta hanyar amfani da batun hakkin dan Adam. Muryoyin kasashe sama da 100 sun shaida cewa, yunkurin da Amurka da sauran wasu kasashe ’yan kalilan suka yi, ba zai yi nasara ba. (Murtala Zhang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

A Dawo Da Tsohon Farashin Man Fetur Cikin Gaggawa – NLC

Next Post

Dorewar Bunkasuwar Tattalin Arzikin Sin Ta Karawa Duniya Kwarin Gwiwa

Related

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

17 hours ago
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

17 hours ago
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana
Daga Birnin Sin

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

19 hours ago
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa
Daga Birnin Sin

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

20 hours ago
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata
Daga Birnin Sin

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

21 hours ago
Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su
Daga Birnin Sin

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

2 days ago
Next Post
Dorewar Bunkasuwar Tattalin Arzikin Sin Ta Karawa Duniya Kwarin Gwiwa

Dorewar Bunkasuwar Tattalin Arzikin Sin Ta Karawa Duniya Kwarin Gwiwa

LABARAI MASU NASABA

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

June 29, 2025
Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

June 29, 2025
Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

June 29, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

June 29, 2025
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

June 29, 2025
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.