• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Asirin Amurka A Fannin Tada “Yakin Hakkin Dan Adam” A Duniya

byCGTN Hausa and Sulaiman
12 months ago
Amurka

Zuwa yau 9 ga watan Oktoba aka cika wata daya da gudanar da taro na 57 na kwamitin kare hakkin dan Adam na Majalisar Dinkin Duniya, inda kasashe sama da 100 suka bayyana goyon bayansu ga kasar Sin ta hanyoyin gabatar da jawabi tare ko daya bayan daya, wajen jaddada cewa, harkokin Xinjiang, da Hong Kong, da Xizang(Tibet), harkokin cikin gida ne na kasar Sin, kuma bai kamata Amurka ta yi shisshigi a ciki ba. Al’amarin da ya shaida cewa, yunkurin Amurka da sauran wasu kasashe ‘yan kalilan na yammacin duniya na siyasantar da batun hakkin dan Adam, ba zai samu nasara ba.

 

Amurka ta kawar da ido daga matsalolin da ita kanta take fuskanta ta fannin kare hakkin Adam, kuma tana fakewa da batun hakkin dan Adam wajen matsawa sauran kasashe lamba, gami da nuna fin karfi a duniya.

  • Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Mara Baya Ga Kasashen Yankin Manyan Tafkunan Afirka Don Karfafa Hadin Gwiwa
  • Xi Jinping Ya Karfafawa Kungiyar Red Cross Ta Sin Gwiwar Karfafa Ayyukan Jin Kai

Domin tsoma baki cikin harkokin cikin gidan sauran kasashe, abu na farko da Amurka ta kan yi, shi ne kirkiro “laifin da ya shafi hakkin dan Adam”. Bari mu dauki kasar Venezuela a matsayin misali. A ’yan shekarun nan, bisa hujjar wai Venezuela ta aikata laifi a fannin kare hakkin dan Adam, Amurka ta fadada kakaba mata takunkumin tattalin arziki, al’amarin da ya haifar wa Venezuela matsalolin tattalin arziki da jin kai da kuma ci gaba.

 

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Baya ga gwamnati da kafafen yada labarai, wani muhimmin abu da ya taka muhimmiyar rawa a cikin “yakin hakkin dan Adam” da Amurka ta tayar a sauran kasashe, shi ne NGO, wato kungiyoyin da ba na gwamnati ba. Wasu kungiyoyin da ba na gwamnati ba a Amurka, wadanda suka fake da sunan kare “demokuradiyya” da “hakkin dan Adam”, sun yi yunkurin rura wutar rikicin kawo baraka, da kulla makiricin tada rikicin siyasa, da shirga karya da sauransu a sassan kasa da kasa.

 

A Majalisar Dinkin Duniya kuwa, Amurka ta kan bada shawarar zartas da kudurorin kasa iri-iri ta hanyar fakewa da batun hakkin Adam, inda ta kan nuna yatsa ga wasu kasashe masu tasowa, da matsa musu lamba a fannin siyasa, kana ta kan yi yunkurin kawo cikas ga wasu batutuwan gaggawa da suka shafi jin kai.

 

Akasarin kasashe masu tsayawa kan adalci da gaskiya sun riga sun fahimci wayon Amurka, wato yunkurin da take na yin shisshigi cikin harkokin cikin gidan kasar Sin da na sauran kasashe masu tasowa, ta hanyar amfani da batun hakkin dan Adam. Muryoyin kasashe sama da 100 sun shaida cewa, yunkurin da Amurka da sauran wasu kasashe ’yan kalilan suka yi, ba zai yi nasara ba. (Murtala Zhang)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko
Daga Birnin Sin

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan
Daga Birnin Sin

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana
Daga Birnin Sin

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Next Post
Dorewar Bunkasuwar Tattalin Arzikin Sin Ta Karawa Duniya Kwarin Gwiwa

Dorewar Bunkasuwar Tattalin Arzikin Sin Ta Karawa Duniya Kwarin Gwiwa

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version