Kungiyar kwallon kafa ta Atalanta za ta bukaci kusan Yuro miliyan 50 don siyar da dan wasanta na gefe, Ademola Lookman a wannan bazarar.
Zakarun gasar Seria A, Napoli na zawarcin dan wasan na Nijeriya tun bayan rawar da ya taka a ‘yan shekarun nan inda ya taimakawa Atalanta lashe gasar UEFA Europa League a karon farko a tarihinta.
- Matatar Dangote Za Ta Fara Dakon Man Fetur Da Dizal Kyauta A Fadin Nijeriya
- Wata Sabuwa: Malaman Jami’ar Tarayya A Kano Sun ƙi Amince Wa Da Zaɓen Sabon VC
LEADERSHIP ta samu rahoton cewa kocin Napoli Antonio Conte na fatan ganin tsohon dan wasan na Everton ya zama daya daga cikin yan wasansa da zai tunkari kakar wasan da ke tafe, amma kuma farashin da Atalanta da dorawa dan wasan mai shekaru 27 na iya dagula al’amura ga kulob din na Naples.
A cewar Football Italia, Napoli ta yi imanin cewa Yuro miliyan 50 ya yi yawa ga dan wasan da ya haura shekaru 25, inda ta ke fatan samun rangwame kafin ta yanke shawara ta karshe akan Lookman wanda ya zura kwallaye da dama, ya kuma taimaka aka zura, Napoli na duba yiwuwar musayar dan wasa da kuma tsabar kudi wajen daukar shi, amma kuma Atalanta din tafi bukatar kudinsa domin samun gwagwgwabar riba.
Dan wasan mai shekaru 27 ya zura kwallaye 20 sannan ya taimaka wajen zura bakwai daga wasanni 40 da ya buga a duk wasannin da ya buga a kakar wasan data gabata, Lookman ya ci kwallaye 17 kuma ya taimaka wajen zura 10 a kakar wasanni ta shekarar 2023/24.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp