• English
  • Business News
Wednesday, October 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Atiku Ga ‘Yan Inugu: Za Mu Samar Muku Da Romon Dimokraɗiyya Idan Kuka Zaɓe Mu

by Musa Muhammad
3 years ago
Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya yi kira ga jama’ar Jihar Inugu da su zaɓi PDP a zaɓen shugaban ƙasa da za a yi domin su ma su sha romon dimokiraɗiyya daga wajen Gwamnatin Tarayya.

Atiku ya faɗi haka ne a ranar Talata a lokacin taron yaƙin neman zaɓen PDP da aka yi a Inugu.

Ɗan takarar ya ce zaɓen PDP shi zai ƙara kusantar da jihar ga fadar shugaban ƙasa domin a tafi tare da ita.

Ya bayyana jin daɗi kan ɗimbin mutanen da suka fito suka halarci taron, ya ce wannan na nufin da ma can Jihar Inugu jiha ce ta jam’iyyar PDP.

“Ni ne zan zama matakalar da wani ɗan ƙabilar Ibo zai taka ya kai ga zama shugaban ƙasa a nan gaba,” inji shi.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP

2027: Babu Ɗan Siyasar Da Zai Iya Ƙalubalantar Tinubu — Fadar Shugaban Ƙasa

  • Da ɗumi-ɗuminsa: Buhari Ya Kara Wa’adin Amfani Da Tsohuwar Naira 200 Da Kwana 60

 

Atiku ya ƙara da cewa: “Ina so ku ci gaba da ba PDP goyon baya domin kuwa gwamnatin da za ta kafa mulkin shugaban ƙasa a nan gaba ta Ibo ce a ƙarƙashin jagorancin Ibo.

“Ina ba ku shawara da ko yaushe ku riƙa tashi ana yin tafiya tare da ku domin ku ma ku sha romon dimokiraɗiyya,” in ji shi.

Sai dai an lura da cewa Gwamna Ifeanyi Ugwuanyi na Jihar Inugu bai halarci taron ba.

Ugwuanyi, wanda yana daga cikin gwamnonin nan biyar da suka yi tawaye suka ƙi bin Atiku, wato ‘yan gungun G-5, an ce ya tarbi Atiku ne a Gidan Gwamnati a matsayinsa na tsohon mataimakin shugaban ƙasa kawai.

Dakta Iyorcha Ayu, wanda shi ne Shugaban jami’ar PDP na ƙasa, a nasa jawabin ya bayyana Inugu da cewa jihar PDP ce tun fil’azal.

Ya ce: “Inugu sai PDP; kuma PDP sai Inugu.”

“PDP na cikin jinin ku, kuma na tabbatar da cewa a ranakun zaɓe, wato ranar 25 ga Fabrairu da ranar 11 ga Maris, daga nan za ku zaɓi PDP daga sama har ƙas, kuma daga ƙasa har zuwa sama.”

Bugu da ƙari, ya shawarce su da kada su kuskura su saurari wata jam’iyyar; ya ce: “Rayuwar ku na wajen PDP”.

Kuma ya ce, “Ba sai na tsaya yi maku wani dogon wa’azi ba domin kun riga kun dawo wajen mu.”

Atiku na ci gaba da yaƙin neman zaɓe a sassan ƙasar nan.

  • https://leadership.ng/atiku-in-jigawa-promises-to-invest-in-agriculture-commerce/
ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP

October 15, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

2027: Babu Ɗan Siyasar Da Zai Iya Ƙalubalantar Tinubu — Fadar Shugaban Ƙasa

October 15, 2025
Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima
Manyan Labarai

Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

October 15, 2025
Next Post
Kamfanin Lantarki Na Kaduna Ya Yi Tir Da Kai Wa Ma’aikatansa Farmaki

Kamfanin Lantarki Na Kaduna Ya Yi Tir Da Kai Wa Ma'aikatansa Farmaki

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Yi Juyin Mulki A Ƙasar Madagascar

Sojoji Sun Yi Juyin Mulki A Ƙasar Madagascar

October 15, 2025
Shugaban Zaunannen Kwamitin Majalisar Wakilan Jama’ar Sin Ya Gana Da Mukaddashin Shugaban Majalisar Dattawan Kasar Liberia

Shugaban Zaunannen Kwamitin Majalisar Wakilan Jama’ar Sin Ya Gana Da Mukaddashin Shugaban Majalisar Dattawan Kasar Liberia

October 15, 2025
Gwamnan Kaduna Ya Taya Al’Amin Murnar Nasarar Lashe Gasar Ƙirƙirar Fasaha Ta Duniya A Ƙasar Birtaniya 

Gwamnan Kaduna Ya Taya Al’Amin Murnar Nasarar Lashe Gasar Ƙirƙirar Fasaha Ta Duniya A Ƙasar Birtaniya 

October 15, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Ladan Bosso Ya Ajiye Aikin Horar Da Barau Fc 

Da Ɗumi-ɗumi: Ladan Bosso Ya Ajiye Aikin Horar Da Barau Fc 

October 15, 2025
An Bude Bikin Baje Kolin Kasuwanci Na Kasa Da Kasa Na 138 A Guangzhou

An Bude Bikin Baje Kolin Kasuwanci Na Kasa Da Kasa Na 138 A Guangzhou

October 15, 2025
sallah

Da Ɗumi-ɗumi: Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ya Ƙara Raguwa Zuwa Kashi 18.02%

October 15, 2025
Mujallar “Qiushi” Za Ta Wallafa Muhimmiyar Kasidar Shugaba Xi Jinping Kan Muhimman Shawarwari Hudu Da Ya Gabatar

Mujallar “Qiushi” Za Ta Wallafa Muhimmiyar Kasidar Shugaba Xi Jinping Kan Muhimman Shawarwari Hudu Da Ya Gabatar

October 15, 2025
Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Ta’adda A Dajin Taraba

Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Ta’adda A Dajin Taraba

October 15, 2025
Xi Jinping Ya Taya Patrick Herminie Murnar Lashe Zaben Shugaban Kasar Seychelles

Xi Jinping Ya Taya Patrick Herminie Murnar Lashe Zaben Shugaban Kasar Seychelles

October 15, 2025
Yajin Aikin: Ɗalibai Sun Bai Wa ASUU Da Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwana 7 Su Warware Rikicinsu

Yajin Aikin: Ɗalibai Sun Bai Wa ASUU Da Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwana 7 Su Warware Rikicinsu

October 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.