ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Atiku Ga ‘Yan Inugu: Za Mu Samar Muku Da Romon Dimokraɗiyya Idan Kuka Zaɓe Mu

by Musa Muhammad
3 years ago
Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya yi kira ga jama’ar Jihar Inugu da su zaɓi PDP a zaɓen shugaban ƙasa da za a yi domin su ma su sha romon dimokiraɗiyya daga wajen Gwamnatin Tarayya.

Atiku ya faɗi haka ne a ranar Talata a lokacin taron yaƙin neman zaɓen PDP da aka yi a Inugu.

Ɗan takarar ya ce zaɓen PDP shi zai ƙara kusantar da jihar ga fadar shugaban ƙasa domin a tafi tare da ita.

ADVERTISEMENT

Ya bayyana jin daɗi kan ɗimbin mutanen da suka fito suka halarci taron, ya ce wannan na nufin da ma can Jihar Inugu jiha ce ta jam’iyyar PDP.

“Ni ne zan zama matakalar da wani ɗan ƙabilar Ibo zai taka ya kai ga zama shugaban ƙasa a nan gaba,” inji shi.

LABARAI MASU NASABA

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

  • Da ɗumi-ɗuminsa: Buhari Ya Kara Wa’adin Amfani Da Tsohuwar Naira 200 Da Kwana 60

 

Atiku ya ƙara da cewa: “Ina so ku ci gaba da ba PDP goyon baya domin kuwa gwamnatin da za ta kafa mulkin shugaban ƙasa a nan gaba ta Ibo ce a ƙarƙashin jagorancin Ibo.

“Ina ba ku shawara da ko yaushe ku riƙa tashi ana yin tafiya tare da ku domin ku ma ku sha romon dimokiraɗiyya,” in ji shi.

Sai dai an lura da cewa Gwamna Ifeanyi Ugwuanyi na Jihar Inugu bai halarci taron ba.

Ugwuanyi, wanda yana daga cikin gwamnonin nan biyar da suka yi tawaye suka ƙi bin Atiku, wato ‘yan gungun G-5, an ce ya tarbi Atiku ne a Gidan Gwamnati a matsayinsa na tsohon mataimakin shugaban ƙasa kawai.

Dakta Iyorcha Ayu, wanda shi ne Shugaban jami’ar PDP na ƙasa, a nasa jawabin ya bayyana Inugu da cewa jihar PDP ce tun fil’azal.

Ya ce: “Inugu sai PDP; kuma PDP sai Inugu.”

“PDP na cikin jinin ku, kuma na tabbatar da cewa a ranakun zaɓe, wato ranar 25 ga Fabrairu da ranar 11 ga Maris, daga nan za ku zaɓi PDP daga sama har ƙas, kuma daga ƙasa har zuwa sama.”

Bugu da ƙari, ya shawarce su da kada su kuskura su saurari wata jam’iyyar; ya ce: “Rayuwar ku na wajen PDP”.

Kuma ya ce, “Ba sai na tsaya yi maku wani dogon wa’azi ba domin kun riga kun dawo wajen mu.”

Atiku na ci gaba da yaƙin neman zaɓe a sassan ƙasar nan.

  • https://leadership.ng/atiku-in-jigawa-promises-to-invest-in-agriculture-commerce/
Atiku
Musa Muhammad
+ postsBio
  • Musa Muhammad
    https://hausa.leadership.ng/author/musa-muhammad/
    “Babu Gaskiya A Takardar Da Ke Alaƙanta Gwamnatin Zamfara Da ’Yan Bindiga”
  • Musa Muhammad
    https://hausa.leadership.ng/author/musa-muhammad/
    Ina Rokon Allah Ya Sa Na Kammala Sana’ar Fim Cikin Mutunci – Jarumi Sadik
  • Musa Muhammad
    https://hausa.leadership.ng/author/musa-muhammad/
    2023: Atiku Ya Sha Alwashin Ƙara Wa Jihohi Da Ƙananan Hukumomi Ƙarfin Iko
  • Musa Muhammad
    https://hausa.leadership.ng/author/musa-muhammad/
    Ambaliyar Ruwa: Gwamnati Ta Fara Kai Agajin Tan 12,000 Na Abinci Jigawa Da Anambra

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje
Manyan Labarai

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100
Siyasa

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Next Post
Kamfanin Lantarki Na Kaduna Ya Yi Tir Da Kai Wa Ma’aikatansa Farmaki

Kamfanin Lantarki Na Kaduna Ya Yi Tir Da Kai Wa Ma'aikatansa Farmaki

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.