ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Atiku Ga ‘Yan Inugu: Za Mu Samar Muku Da Romon Dimokraɗiyya Idan Kuka Zaɓe Mu

by Musa Muhammad
3 years ago
Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya yi kira ga jama’ar Jihar Inugu da su zaɓi PDP a zaɓen shugaban ƙasa da za a yi domin su ma su sha romon dimokiraɗiyya daga wajen Gwamnatin Tarayya.

Atiku ya faɗi haka ne a ranar Talata a lokacin taron yaƙin neman zaɓen PDP da aka yi a Inugu.

Ɗan takarar ya ce zaɓen PDP shi zai ƙara kusantar da jihar ga fadar shugaban ƙasa domin a tafi tare da ita.

ADVERTISEMENT

Ya bayyana jin daɗi kan ɗimbin mutanen da suka fito suka halarci taron, ya ce wannan na nufin da ma can Jihar Inugu jiha ce ta jam’iyyar PDP.

“Ni ne zan zama matakalar da wani ɗan ƙabilar Ibo zai taka ya kai ga zama shugaban ƙasa a nan gaba,” inji shi.

LABARAI MASU NASABA

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

  • Da ɗumi-ɗuminsa: Buhari Ya Kara Wa’adin Amfani Da Tsohuwar Naira 200 Da Kwana 60

 

Atiku ya ƙara da cewa: “Ina so ku ci gaba da ba PDP goyon baya domin kuwa gwamnatin da za ta kafa mulkin shugaban ƙasa a nan gaba ta Ibo ce a ƙarƙashin jagorancin Ibo.

“Ina ba ku shawara da ko yaushe ku riƙa tashi ana yin tafiya tare da ku domin ku ma ku sha romon dimokiraɗiyya,” in ji shi.

Sai dai an lura da cewa Gwamna Ifeanyi Ugwuanyi na Jihar Inugu bai halarci taron ba.

Ugwuanyi, wanda yana daga cikin gwamnonin nan biyar da suka yi tawaye suka ƙi bin Atiku, wato ‘yan gungun G-5, an ce ya tarbi Atiku ne a Gidan Gwamnati a matsayinsa na tsohon mataimakin shugaban ƙasa kawai.

Dakta Iyorcha Ayu, wanda shi ne Shugaban jami’ar PDP na ƙasa, a nasa jawabin ya bayyana Inugu da cewa jihar PDP ce tun fil’azal.

Ya ce: “Inugu sai PDP; kuma PDP sai Inugu.”

“PDP na cikin jinin ku, kuma na tabbatar da cewa a ranakun zaɓe, wato ranar 25 ga Fabrairu da ranar 11 ga Maris, daga nan za ku zaɓi PDP daga sama har ƙas, kuma daga ƙasa har zuwa sama.”

Bugu da ƙari, ya shawarce su da kada su kuskura su saurari wata jam’iyyar; ya ce: “Rayuwar ku na wajen PDP”.

Kuma ya ce, “Ba sai na tsaya yi maku wani dogon wa’azi ba domin kun riga kun dawo wajen mu.”

Atiku na ci gaba da yaƙin neman zaɓe a sassan ƙasar nan.

  • https://leadership.ng/atiku-in-jigawa-promises-to-invest-in-agriculture-commerce/
Atiku
Musa Muhammad
+ postsBio
  • Musa Muhammad
    https://hausa.leadership.ng/author/musa-muhammad/
    “Babu Gaskiya A Takardar Da Ke Alaƙanta Gwamnatin Zamfara Da ’Yan Bindiga”
  • Musa Muhammad
    https://hausa.leadership.ng/author/musa-muhammad/
    Ina Rokon Allah Ya Sa Na Kammala Sana’ar Fim Cikin Mutunci – Jarumi Sadik
  • Musa Muhammad
    https://hausa.leadership.ng/author/musa-muhammad/
    2023: Atiku Ya Sha Alwashin Ƙara Wa Jihohi Da Ƙananan Hukumomi Ƙarfin Iko
  • Musa Muhammad
    https://hausa.leadership.ng/author/musa-muhammad/
    Ambaliyar Ruwa: Gwamnati Ta Fara Kai Agajin Tan 12,000 Na Abinci Jigawa Da Anambra

MASU ALAKA

2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa
Siyasa

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

June 22, 2026
Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
Siyasa

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

June 22, 2026
ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027
Siyasa

ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

June 21, 2026
Next Post
Kamfanin Lantarki Na Kaduna Ya Yi Tir Da Kai Wa Ma’aikatansa Farmaki

Kamfanin Lantarki Na Kaduna Ya Yi Tir Da Kai Wa Ma'aikatansa Farmaki

LABARAI MASU NASABA

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.