• English
  • Business News
Tuesday, September 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Auren Gata : Gwamnatin Jihar Kebbi Ta Aurar Da Mata 300

by Umar Faruk
2 years ago
in Labarai
0
Auren Gata : Gwamnatin Jihar Kebbi Ta Aurar Da Mata 300
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin jihar Kebbi karkashin jagorancin Gwamna Nasir Idris tare da hadin gwiwar gidauniyar Nafisa Nasir Charity Development Foundation (NANAS) sun aurar da mata 300 a garin Birnin Kebbi tare da shawartar ma’auratan da su kasance masu sada zumunci da son juna.

Bikin wanda ya gudana a fadar Mai Martaba Sarkin Gwandu, Gidauniyar NANAS ce ta shirya wanda matar Gwamnan, Hajiya Nafisa Nasir Idris ta kafa.

  • ‘Saurayin Da Muka Yi Alkawarin Aure Ya Fara Kula ‘Yan Mata Da Yawa, A Ba Ni Shawara’
  • Kwamoti B Laori Ya Kaddamar Da Zauren Taro a Borrong, Demsa

Kakakin majalisar dokokin jihar Rt. Hon. Muhammad Usman Ankwe, shine ya wakilci gwamna a wajen bikin daurin auren inda ya bayyana cewa, za’a gudanar da irin wannan daurin auren lokaci-lokaci domin taimakawa marasa galihu maza da mata.

Dakta Nasir Idris ya ce, gwamnatinsa ta bayar da jimillar Naira miliyan 21 a matsayin sadaki ga matan da aka daura wa aure 300 da suka fito daga kananan hukumomin jihar 21, inda kowace amarya za ta samu sadaki Naira 70,000.

Auren gata

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Kai Hare-hare 261, ‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 1,950 A Watan Agusta – NOA

An Kama Mutane 30 Da Zargin Laifin Aikin Dabanci A Yayin Zagayen Maulidi A Neja

Ya kara da cewa, gwamnatinsa ta kuma samar da kayan daki da kayan abinci ga dukkan ma’auratan domin karfafa wa aurensu .

Haka kuma Gwamnan ya Kara da bayyana cewa an daura auren ne bayan tattaunawa da malaman addinin Musulunci bisa tsarin da Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya yi, wanda ya baiwa mabiyansa izinin yin mubayi’ar aure don amfanin al’umma da kuma haifar da zuriya masu albarka.

Daga karshe ya shawarci ma’aurata da su mutunta dokokin aure, yana mai cewa dole ne ango ya kare hakki da hakkokin matarsa, haka kuma matan su kasance masu aminci da goyon bayan mazajensu.

Auren gata

A nata jawabin, Uwargidan Gwamnan Jihar, Hajiya Nafisa Nasir Idris wadda ita ce ta kafa NANAS FOUNDATION, ta bayyana matukar jin dadinta ga mijin nata da ya ba ta tallafin kayan daki da kayan masarufi wanda ya sanya aka yi gagarumin bikin aure.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Auren gataGwamnatin Kebbi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Batura Kirar Sin Sun Jawo Hankalin Kamfanoni Daga Duk Fadin Duniya

Next Post

CMG Ya Kaddamar Da Biki Kafin Liyafar Bikin Bazara A New York

Related

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kai Hare-hare 261, ‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 1,950 A Watan Agusta – NOA

7 hours ago
'yansanda
Labarai

An Kama Mutane 30 Da Zargin Laifin Aikin Dabanci A Yayin Zagayen Maulidi A Neja

8 hours ago
Gwamnatin Tarayya, NUPENG Da Ɗangote Sun Fara Tattaunawa Don Kawo Ƙarshen Yajin Aikin Ma’aikatan Mai
Labarai

Gwamnatin Tarayya, NUPENG Da Ɗangote Sun Fara Tattaunawa Don Kawo Ƙarshen Yajin Aikin Ma’aikatan Mai

9 hours ago
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Rahotonni

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

11 hours ago
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna
Manyan Labarai

Gwamna Uba Sani Ya Buƙaci Al’ummar Jihar Kaduna Da Su Yi Rijistar Katin Zaɓe 

12 hours ago
DSS Ta Ba Sowore Mako Ɗaya Ya Janye Maganarsa Kan Tinubu
Manyan Labarai

DSS Ta Ba Sowore Mako Ɗaya Ya Janye Maganarsa Kan Tinubu

14 hours ago
Next Post
CMG Ya Kaddamar Da Biki Kafin Liyafar Bikin Bazara A New York

CMG Ya Kaddamar Da Biki Kafin Liyafar Bikin Bazara A New York

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Zama Wurin Da Aka Fi Zaba Domin Warware Takaddamar Cinikayya Da Ta Shafi Kasa Da Kasa

Kasar Sin Ta Zama Wurin Da Aka Fi Zaba Domin Warware Takaddamar Cinikayya Da Ta Shafi Kasa Da Kasa

September 8, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Kai Hare-hare 261, ‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 1,950 A Watan Agusta – NOA

September 8, 2025
Kasar Sin Ta Bayar Da Gaggarumar Gudunmuwa Ga Wanzuwar Zaman Lafiya Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

Kasar Sin Ta Bayar Da Gaggarumar Gudunmuwa Ga Wanzuwar Zaman Lafiya Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

September 8, 2025
'yansanda

An Kama Mutane 30 Da Zargin Laifin Aikin Dabanci A Yayin Zagayen Maulidi A Neja

September 8, 2025
Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Cifit Karo Na 25

Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Cifit Karo Na 25

September 8, 2025
Gwamnatin Tarayya, NUPENG Da Ɗangote Sun Fara Tattaunawa Don Kawo Ƙarshen Yajin Aikin Ma’aikatan Mai

Gwamnatin Tarayya, NUPENG Da Ɗangote Sun Fara Tattaunawa Don Kawo Ƙarshen Yajin Aikin Ma’aikatan Mai

September 8, 2025
Sin Ta Gabatar Da Sabon Injin Aiki A Manyan Na’urori Mai Amfani Da Iskar Gas Kirar Gida

Sin Ta Gabatar Da Sabon Injin Aiki A Manyan Na’urori Mai Amfani Da Iskar Gas Kirar Gida

September 8, 2025
Auren gata

Jarin Da Sin Ta Zuba Kai Tsaye A Kasashe Cikin Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Ya Karu Da Kashi 22.9% A 2024

September 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

September 8, 2025
Adadin Kamfanonin AI A Sin Sun Haura 5,000

Adadin Kamfanonin AI A Sin Sun Haura 5,000

September 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.