• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ayyukan Ba Da Agaji Abin Koyi Daga Kasar Sin A Girgizar Kasa A Jihar Xizang

by CGTN Hausa and Sulaiman
7 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Ayyukan Ba Da Agaji Abin Koyi Daga Kasar Sin A Girgizar Kasa A Jihar Xizang
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Da misalin karfe 9:05 na safe (agogon Beijing), ranar Talata 7 ga watan Janairun 2025, wani sashe na jihar Xizang mai cin gashin kansa dake kudu maso yammacin kasar Sin ya tsinci kansa cikin ibtila’in girgizar kasa mai karfin maki 6.8, inda lamarin ya shafi a kalla mutane 60,000.

Idan irin wannan ibtila’i ya afku, hankula su kan karkata a kan kasar da abin ya afku domin a ga yadda za ta yi wajen saukakawa al’ummomin da abin ya shafa halin da suka tsinci kansu a ciki.

  • Xi Ya Zanta Da Babban Jagoran Vietnam Da Shugaban Sri Lanka
  • Karramawa: Ma’aikatan Kano Sun Yaba Wa Jagorancin Gwamna Abba Na Tausayi

Da yake kasar Sin tana fifita jama’a a gaba da komai, tabbas ba ta dauki lamarin da wasa ba, nan take Shugaba Xi Jinping ya umarci hada karfi da karfe daga dukkan bangarori wajen kai dauki ga mutanen da ibtila’in ya afkawa, har ma ya aike da mataimakin firaministan kasar, Zhang Guoqing zuwa yankin domin ya jagoranci ayyukan agaji.

Masu ayyukan ceto sun zage damtse tare da gwada tsere a tsakaninsu da kurewar lokaci wajen kakkafa tantuna na sake tsugunar da mutane a yankin, wanda a lokacin an yi hasashen yanayinsa na sanyi ya tsananta sosai.

Kazalika, masu ayyukan sa-kai daban-daban kowa ya nuna bajintar abin da zai iya gwargwadon hali. Daga cikinsu akwai wani mai shagon dafa taliya daga jihar Ningxia ta kabilar Hui mai cin gashin kansa, Wang Shengyun wanda ya yo tafiyar sama da kilomita 3,000 tare da abokansa zuwa yankin da abin ya shafa domin ba da agaji.

Labarai Masu Nasaba

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Wang Shengyun da abokansa sun taimaka wa al’ummar kauyen Gabu, da abincin da suka rika dafawa da kansu a kullum, irin su taliya, naman shanu da kayan marmari kamar su tuffa da kudinsu ya kai kimanin kudin Sin yuan 219,000, kwatankwacin dalar Amurka 30,000.

Jami’an ’yan sanda daga hukumar kula da shige da fice ta kasar Sin da ke yankin Xigaze a kalla 200 suka rika ceto mutanen da suka makale a baraguzai, tare da dabbobinsu da sauran kayayyakinsu masu amfani a kauyukan Yubai, Gabu da Zacun da ke birnin Changsuo. Saboda yawan aikin da suke yi da kyar suka rika samun hutu. Wani babban jami’i daga ofishinsu na Nyima ya ce, idan aiki ya yawaita a wani kauye ko jami’an can sun gaji ainun, su kan kwashi jami’ai daga yankunan da aikin ke da sauki zuwa can.

Wasu mazauna kauyukan da abin ya faru dai, sun tabbatar da cewa sun samu dauki daga ’yan sanda cikin minti 30 kacal da afkuwar ibtila’in.

Ma’aikatar kudi da ta ba da agajin gaggawa ta kasar Sin sun fitar da kudin Sin yuan miliyan 100, kwatankwacin dalar Amurka miliyan 13.9 don tallafa wa ayyukan agaji a jihar ta Xizang.

Haka nan, domin sake mayar da al’ummomin da abin ya shafa cikin hayyacinsu, ma’aikatar kudi ta kasar Sin ta sake kebe kudin Sin yuan miliyan 80 kwatankwacin dalar Amurka miliyan 11, domin farfadi da aikin gona a jihar ta Xizang. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Da Ɗumi-ɗumi: Sojoji Sun Haramta Amfani Da Jirage Marasa Matuƙa A Arewa Maso Gabas

Next Post

An Samu Kyakkyawan Sakamako A Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Sauran Kasashe A 2024

Related

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama
Daga Birnin Sin

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

17 hours ago
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14
Daga Birnin Sin

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

18 hours ago
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12
Daga Birnin Sin

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

19 hours ago
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana
Daga Birnin Sin

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

20 hours ago
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

21 hours ago
Manyan Jami’an JKS Sun Ziyarci Jami’ai Da Mazauna Birnin Lhasa
Daga Birnin Sin

Manyan Jami’an JKS Sun Ziyarci Jami’ai Da Mazauna Birnin Lhasa

22 hours ago
Next Post
An Samu Kyakkyawan Sakamako A Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Sauran Kasashe A 2024

An Samu Kyakkyawan Sakamako A Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Sauran Kasashe A 2024

LABARAI MASU NASABA

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

August 23, 2025
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

August 23, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

August 23, 2025
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

August 23, 2025
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

August 23, 2025
Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

August 23, 2025
Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

August 23, 2025
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga

Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Kama Waɗanda Suka Kashe Masallata A Malumfashi 

August 23, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

August 23, 2025
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.