• English
  • Business News
Monday, November 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ayyukan Ba Da Agaji Abin Koyi Daga Kasar Sin A Girgizar Kasa A Jihar Xizang

by CGTN Hausa and Sulaiman
10 months ago
Agaji

Da misalin karfe 9:05 na safe (agogon Beijing), ranar Talata 7 ga watan Janairun 2025, wani sashe na jihar Xizang mai cin gashin kansa dake kudu maso yammacin kasar Sin ya tsinci kansa cikin ibtila’in girgizar kasa mai karfin maki 6.8, inda lamarin ya shafi a kalla mutane 60,000.

Idan irin wannan ibtila’i ya afku, hankula su kan karkata a kan kasar da abin ya afku domin a ga yadda za ta yi wajen saukakawa al’ummomin da abin ya shafa halin da suka tsinci kansu a ciki.

  • Xi Ya Zanta Da Babban Jagoran Vietnam Da Shugaban Sri Lanka
  • Karramawa: Ma’aikatan Kano Sun Yaba Wa Jagorancin Gwamna Abba Na Tausayi

Da yake kasar Sin tana fifita jama’a a gaba da komai, tabbas ba ta dauki lamarin da wasa ba, nan take Shugaba Xi Jinping ya umarci hada karfi da karfe daga dukkan bangarori wajen kai dauki ga mutanen da ibtila’in ya afkawa, har ma ya aike da mataimakin firaministan kasar, Zhang Guoqing zuwa yankin domin ya jagoranci ayyukan agaji.

Masu ayyukan ceto sun zage damtse tare da gwada tsere a tsakaninsu da kurewar lokaci wajen kakkafa tantuna na sake tsugunar da mutane a yankin, wanda a lokacin an yi hasashen yanayinsa na sanyi ya tsananta sosai.

Kazalika, masu ayyukan sa-kai daban-daban kowa ya nuna bajintar abin da zai iya gwargwadon hali. Daga cikinsu akwai wani mai shagon dafa taliya daga jihar Ningxia ta kabilar Hui mai cin gashin kansa, Wang Shengyun wanda ya yo tafiyar sama da kilomita 3,000 tare da abokansa zuwa yankin da abin ya shafa domin ba da agaji.

LABARAI MASU NASABA

Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

Wang Shengyun da abokansa sun taimaka wa al’ummar kauyen Gabu, da abincin da suka rika dafawa da kansu a kullum, irin su taliya, naman shanu da kayan marmari kamar su tuffa da kudinsu ya kai kimanin kudin Sin yuan 219,000, kwatankwacin dalar Amurka 30,000.

Jami’an ’yan sanda daga hukumar kula da shige da fice ta kasar Sin da ke yankin Xigaze a kalla 200 suka rika ceto mutanen da suka makale a baraguzai, tare da dabbobinsu da sauran kayayyakinsu masu amfani a kauyukan Yubai, Gabu da Zacun da ke birnin Changsuo. Saboda yawan aikin da suke yi da kyar suka rika samun hutu. Wani babban jami’i daga ofishinsu na Nyima ya ce, idan aiki ya yawaita a wani kauye ko jami’an can sun gaji ainun, su kan kwashi jami’ai daga yankunan da aikin ke da sauki zuwa can.

Wasu mazauna kauyukan da abin ya faru dai, sun tabbatar da cewa sun samu dauki daga ’yan sanda cikin minti 30 kacal da afkuwar ibtila’in.

Ma’aikatar kudi da ta ba da agajin gaggawa ta kasar Sin sun fitar da kudin Sin yuan miliyan 100, kwatankwacin dalar Amurka miliyan 13.9 don tallafa wa ayyukan agaji a jihar ta Xizang.

Haka nan, domin sake mayar da al’ummomin da abin ya shafa cikin hayyacinsu, ma’aikatar kudi ta kasar Sin ta sake kebe kudin Sin yuan miliyan 80 kwatankwacin dalar Amurka miliyan 11, domin farfadi da aikin gona a jihar ta Xizang. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar
Daga Birnin Sin

Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

November 2, 2025
Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik
Daga Birnin Sin

Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

November 2, 2025
Taron APEC Na 2026 Da Za A Shirya A Kasar Sin Zai Bude Sabon Babin Na Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik
Daga Birnin Sin

Taron APEC Na 2026 Da Za A Shirya A Kasar Sin Zai Bude Sabon Babin Na Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

November 2, 2025
Next Post
An Samu Kyakkyawan Sakamako A Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Sauran Kasashe A 2024

An Samu Kyakkyawan Sakamako A Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Sauran Kasashe A 2024

LABARAI MASU NASABA

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

November 2, 2025
Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

November 2, 2025
Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

November 2, 2025
Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

November 2, 2025
Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

November 2, 2025
Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

November 2, 2025
Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

November 2, 2025
Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

November 2, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su

November 2, 2025
Gidauniyar IRM Da KADCHMA Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna

Gidauniyar IRM Da KADCHMA Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna

November 2, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.