• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ayyukan Ba Da Agaji Abin Koyi Daga Kasar Sin A Girgizar Kasa A Jihar Xizang

by CGTN Hausa and Sulaiman
8 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Ayyukan Ba Da Agaji Abin Koyi Daga Kasar Sin A Girgizar Kasa A Jihar Xizang
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Da misalin karfe 9:05 na safe (agogon Beijing), ranar Talata 7 ga watan Janairun 2025, wani sashe na jihar Xizang mai cin gashin kansa dake kudu maso yammacin kasar Sin ya tsinci kansa cikin ibtila’in girgizar kasa mai karfin maki 6.8, inda lamarin ya shafi a kalla mutane 60,000.

Idan irin wannan ibtila’i ya afku, hankula su kan karkata a kan kasar da abin ya afku domin a ga yadda za ta yi wajen saukakawa al’ummomin da abin ya shafa halin da suka tsinci kansu a ciki.

  • Xi Ya Zanta Da Babban Jagoran Vietnam Da Shugaban Sri Lanka
  • Karramawa: Ma’aikatan Kano Sun Yaba Wa Jagorancin Gwamna Abba Na Tausayi

Da yake kasar Sin tana fifita jama’a a gaba da komai, tabbas ba ta dauki lamarin da wasa ba, nan take Shugaba Xi Jinping ya umarci hada karfi da karfe daga dukkan bangarori wajen kai dauki ga mutanen da ibtila’in ya afkawa, har ma ya aike da mataimakin firaministan kasar, Zhang Guoqing zuwa yankin domin ya jagoranci ayyukan agaji.

Masu ayyukan ceto sun zage damtse tare da gwada tsere a tsakaninsu da kurewar lokaci wajen kakkafa tantuna na sake tsugunar da mutane a yankin, wanda a lokacin an yi hasashen yanayinsa na sanyi ya tsananta sosai.

Kazalika, masu ayyukan sa-kai daban-daban kowa ya nuna bajintar abin da zai iya gwargwadon hali. Daga cikinsu akwai wani mai shagon dafa taliya daga jihar Ningxia ta kabilar Hui mai cin gashin kansa, Wang Shengyun wanda ya yo tafiyar sama da kilomita 3,000 tare da abokansa zuwa yankin da abin ya shafa domin ba da agaji.

Labarai Masu Nasaba

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Wang Shengyun da abokansa sun taimaka wa al’ummar kauyen Gabu, da abincin da suka rika dafawa da kansu a kullum, irin su taliya, naman shanu da kayan marmari kamar su tuffa da kudinsu ya kai kimanin kudin Sin yuan 219,000, kwatankwacin dalar Amurka 30,000.

Jami’an ’yan sanda daga hukumar kula da shige da fice ta kasar Sin da ke yankin Xigaze a kalla 200 suka rika ceto mutanen da suka makale a baraguzai, tare da dabbobinsu da sauran kayayyakinsu masu amfani a kauyukan Yubai, Gabu da Zacun da ke birnin Changsuo. Saboda yawan aikin da suke yi da kyar suka rika samun hutu. Wani babban jami’i daga ofishinsu na Nyima ya ce, idan aiki ya yawaita a wani kauye ko jami’an can sun gaji ainun, su kan kwashi jami’ai daga yankunan da aikin ke da sauki zuwa can.

Wasu mazauna kauyukan da abin ya faru dai, sun tabbatar da cewa sun samu dauki daga ’yan sanda cikin minti 30 kacal da afkuwar ibtila’in.

Ma’aikatar kudi da ta ba da agajin gaggawa ta kasar Sin sun fitar da kudin Sin yuan miliyan 100, kwatankwacin dalar Amurka miliyan 13.9 don tallafa wa ayyukan agaji a jihar ta Xizang.

Haka nan, domin sake mayar da al’ummomin da abin ya shafa cikin hayyacinsu, ma’aikatar kudi ta kasar Sin ta sake kebe kudin Sin yuan miliyan 80 kwatankwacin dalar Amurka miliyan 11, domin farfadi da aikin gona a jihar ta Xizang. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Da Ɗumi-ɗumi: Sojoji Sun Haramta Amfani Da Jirage Marasa Matuƙa A Arewa Maso Gabas

Next Post

An Samu Kyakkyawan Sakamako A Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Sauran Kasashe A 2024

Related

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya
Daga Birnin Sin

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

5 hours ago
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya
Daga Birnin Sin

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

6 hours ago
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin
Daga Birnin Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

7 hours ago
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin
Daga Birnin Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

8 hours ago
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka
Daga Birnin Sin

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

9 hours ago
Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154
Daga Birnin Sin

Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

10 hours ago
Next Post
An Samu Kyakkyawan Sakamako A Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Sauran Kasashe A 2024

An Samu Kyakkyawan Sakamako A Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Sauran Kasashe A 2024

LABARAI MASU NASABA

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

September 12, 2025
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

September 12, 2025
Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

September 12, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

September 12, 2025
Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

September 12, 2025
Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

September 12, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.