• English
  • Business News
Saturday, September 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Ma Cikin Waɗanda Suka Yi Sulhu Da ‘Yan Bindiga – Gwamnatin Katsina

by Sadiq
8 months ago
in Manyan Labarai
0
Ba Ma Cikin Waɗanda Suka Yi Sulhu Da ‘Yan Bindiga – Gwamnatin Katsina
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Jihar Katsina, ta bayyana cewa ba ta da hannu a wani zaman sulhu da ake zargin an yi da ‘yan bindiga, duk da rahotannin da ke cewa an cimma yarjejeniyar sulhu da shugabannin ‘yan bindiga a Ƙaramar Hukumar Batsari.

Kakakin Gwamnati kuma Kwamishinan Yaɗa Labarai da Al’adu na Jihar Katsina, Dokta Bala Salisu ne, ya shaidawa Daily Trust cewa gwamnatin jihar ta tsaya kan matsayinta na ƙin yin sulhu da ‘yan bindiga.

  • Trump Zai Fuskanci Tirjiya A Duniya, Ba Soyayya Ba – Shehu Sani
  • Yaƙin Gaza: Falasɗinawa Sun Fara Neman ‘Yan Uwansu Da Suka Ɓace A Baraguzan Gine-gine

Duk da haka, ya ce gwamnati za ta karɓi duk wani da ya yanke shawarar ajiye makamansa.

“Ba mu da hannu a kowace yarjejeniya ta zaman lafiya.

“Matsayin gwamnati yana nan a bayyane: duk wanda ya bar tashin hankali kuma ya ajiye makamai za mu yi la’akari da shi.

Labarai Masu Nasaba

Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai

“Amma ba za mu nemi ‘yan bindiga don yin sulhu ba,” in ji Dokta Salisu.

Rahotanni sun ce an yi wata ganawar zaman lafiya a ranar Lahadi a ƙauyen Kofa, kusa da garin Batsari, tare da jagorancin manyan jami’an soji, DSS, sarakunan gargajiya, da mazauna yankin.

Wani mazaunin yankin da ya halarci ganawar ya ce ‘yan bindigar sun yi alƙawarin daina kai wa al’umma hare-hare.

Sannan za su saki mutanen da suka yi garkuwa da su tare da miƙa makamai.

“Sun nemi a ba su damar shiga cikin al’umma lafiya, kuma wannan zaman an ce shi ne farkon sulhun,” in ji mazaunin.

An ce manyan shugabannin ‘yan bindiga kamar Lamu Saudo, Abdulhamid Dan Da, Umar Black, da Abu Radda sun miƙa makamansu tare da sakin waɗanda suka yi garkuwa da su a yayin taron.

Majiyoyin soji sun bayyana cewa ‘yan bindigar sun miƙa wuya ne sakamakon matsin lamba da hare-haren sojoji ke ci gaba da kai musu, wanda ya sa ba su da wani zaɓi illa neman zaman lafiya.

Kakakin Rundunar Sojojin ta 17, Laftanar Lawal, ya tabbatar da wannan lamari, inda ya bayyana cewa ci gaba da matsin lambar jami’an tsaro ne ya sa ‘yan bindigar suka miƙa wuya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamnatin KatsinaSulhuYan bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Trump Zai Fuskanci Tirjiya A Duniya, Ba Soyayya Ba – Shehu Sani

Next Post

Matatar Dangote Ta Bai Wa Ɗalibai 473 Tallafin Karatu

Related

Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato
Manyan Labarai

Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

1 hour ago
NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai
Manyan Labarai

NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai

8 hours ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 2 Da Wasu 156 Kan Aikata Laifuka A Jigawa

23 hours ago
Sojoji Sun Kwato Makamai Da Babura, Sun Ceto Mutane 3 A Kaduna 
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Bindiga Ɗauke Da Makamai A Jihar Filato

1 day ago
Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Da ɗumi-ɗuminsa

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

1 day ago
Ministan Tsaro
Manyan Labarai

Dawowar Matsalar Tsaro: Ta Haifar Da Cece-kuce Kan Daukar Matakin Kare Kai

1 day ago
Next Post
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Matatar Dangote Ta Bai Wa Ɗalibai 473 Tallafin Karatu

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

September 6, 2025
Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

September 6, 2025
Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

September 6, 2025
Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

September 6, 2025
Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa

Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa

September 6, 2025
Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

September 6, 2025
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

Kungiyoyi Da Abokan Arziki Na Ci Gaba Da Taya Dantsoho Murna

September 6, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

September 6, 2025
Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

September 6, 2025

Ilimi Shi Ne Matakin Nasarar Rayuwar Duniya Da Lahira – Yerima Shettima

September 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.