• English
  • Business News
Sunday, June 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Ma Cikin Waɗanda Suka Yi Sulhu Da ‘Yan Bindiga – Gwamnatin Katsina

by Sadiq
4 months ago
in Manyan Labarai
0
Ba Ma Cikin Waɗanda Suka Yi Sulhu Da ‘Yan Bindiga – Gwamnatin Katsina
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Jihar Katsina, ta bayyana cewa ba ta da hannu a wani zaman sulhu da ake zargin an yi da ‘yan bindiga, duk da rahotannin da ke cewa an cimma yarjejeniyar sulhu da shugabannin ‘yan bindiga a Ƙaramar Hukumar Batsari.

Kakakin Gwamnati kuma Kwamishinan Yaɗa Labarai da Al’adu na Jihar Katsina, Dokta Bala Salisu ne, ya shaidawa Daily Trust cewa gwamnatin jihar ta tsaya kan matsayinta na ƙin yin sulhu da ‘yan bindiga.

  • Trump Zai Fuskanci Tirjiya A Duniya, Ba Soyayya Ba – Shehu Sani
  • Yaƙin Gaza: Falasɗinawa Sun Fara Neman ‘Yan Uwansu Da Suka Ɓace A Baraguzan Gine-gine

Duk da haka, ya ce gwamnati za ta karɓi duk wani da ya yanke shawarar ajiye makamansa.

“Ba mu da hannu a kowace yarjejeniya ta zaman lafiya.

“Matsayin gwamnati yana nan a bayyane: duk wanda ya bar tashin hankali kuma ya ajiye makamai za mu yi la’akari da shi.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Yusuf Ya Bada Hutu A Ranar Litinin Domin Addu’o’i Ga ‘Yan Wasan Kano 22

Gwamnatin Kano Ta Ba Iyalan Mamatan Wasanni Tallafin Naira Miliyan Ɗaya Kowane

“Amma ba za mu nemi ‘yan bindiga don yin sulhu ba,” in ji Dokta Salisu.

Rahotanni sun ce an yi wata ganawar zaman lafiya a ranar Lahadi a ƙauyen Kofa, kusa da garin Batsari, tare da jagorancin manyan jami’an soji, DSS, sarakunan gargajiya, da mazauna yankin.

Wani mazaunin yankin da ya halarci ganawar ya ce ‘yan bindigar sun yi alƙawarin daina kai wa al’umma hare-hare.

Sannan za su saki mutanen da suka yi garkuwa da su tare da miƙa makamai.

“Sun nemi a ba su damar shiga cikin al’umma lafiya, kuma wannan zaman an ce shi ne farkon sulhun,” in ji mazaunin.

An ce manyan shugabannin ‘yan bindiga kamar Lamu Saudo, Abdulhamid Dan Da, Umar Black, da Abu Radda sun miƙa makamansu tare da sakin waɗanda suka yi garkuwa da su a yayin taron.

Majiyoyin soji sun bayyana cewa ‘yan bindigar sun miƙa wuya ne sakamakon matsin lamba da hare-haren sojoji ke ci gaba da kai musu, wanda ya sa ba su da wani zaɓi illa neman zaman lafiya.

Kakakin Rundunar Sojojin ta 17, Laftanar Lawal, ya tabbatar da wannan lamari, inda ya bayyana cewa ci gaba da matsin lambar jami’an tsaro ne ya sa ‘yan bindigar suka miƙa wuya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamnatin KatsinaSulhuYan bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Trump Zai Fuskanci Tirjiya A Duniya, Ba Soyayya Ba – Shehu Sani

Next Post

Matatar Dangote Ta Bai Wa Ɗalibai 473 Tallafin Karatu

Related

Gwamnan kano
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Bada Hutu A Ranar Litinin Domin Addu’o’i Ga ‘Yan Wasan Kano 22

6 hours ago
Gwamnatin Kano Ta Ba Iyalan Mamatan Wasanni Tallafin Naira Miliyan Ɗaya Kowane
Manyan Labarai

Gwamnatin Kano Ta Ba Iyalan Mamatan Wasanni Tallafin Naira Miliyan Ɗaya Kowane

19 hours ago
Shugaba Tinubu Ya Aika Tawaga Zuwa Jihar Neja Kan Ambaliya Ruwa
Manyan Labarai

Shugaba Tinubu Ya Aika Tawaga Zuwa Jihar Neja Kan Ambaliya Ruwa

1 day ago
Mutane 21 Sun Mutu A Tawagar Ƴan Wasannin Kano A Hatsarin Mota
Manyan Labarai

Mutane 21 Sun Mutu A Tawagar Ƴan Wasannin Kano A Hatsarin Mota

1 day ago
Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Dokar Rage Farashin Mai Da Iskar Gas
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Dokar Rage Farashin Mai Da Iskar Gas

2 days ago
Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Tabbatar Da Zaɓen Ƙananan Hukumomin Kano
Manyan Labarai

Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Tabbatar Da Zaɓen Ƙananan Hukumomin Kano

2 days ago
Next Post
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Matatar Dangote Ta Bai Wa Ɗalibai 473 Tallafin Karatu

LABARAI MASU NASABA

bakin wake

Bam Ya Kashe Mutane 9 A Wata Tashar Motoci Da Ke Borno 

June 1, 2025
‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa

‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa

June 1, 2025
NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

June 1, 2025
SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (3)

SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (3)

June 1, 2025
Gwamnan kano

Gwamna Yusuf Ya Bada Hutu A Ranar Litinin Domin Addu’o’i Ga ‘Yan Wasan Kano 22

June 1, 2025
Gwamna Dikko Zai Sake Tsarin Babbar Kasuwar Jihar Katsina

Majalisar Dokokin Katsina Ta Ayyana Gwamna Radda A Matsayin Dan Takara Daya Tilo A 2027

June 1, 2025
An Karrama Dalibar Kaduna Da Ta Zo Ta Biyu A Gasar Karatun Alkur’ani Ta Duniya

An Karrama Dalibar Kaduna Da Ta Zo Ta Biyu A Gasar Karatun Alkur’ani Ta Duniya

June 1, 2025
Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

June 1, 2025
Alfanu Da Rashin Alfanun Tallata Shirin Aure Tun Kafin Lokacin Ya Zo

Alfanu Da Rashin Alfanun Tallata Shirin Aure Tun Kafin Lokacin Ya Zo

June 1, 2025
Yadda Za Ki Hada Funkasonki

Yadda Za Ki Hada Funkasonki

June 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.