ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, November 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Mu Amince Da Ware Mutum Uku Kacal Su Dauki Rahotannin Gwamnan Kebbi Ba – ‘Yan Jarida

by Umar Faruk
2 years ago
'Yan jarida

LABARAI MASU NASABA

Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci

Jan Aikin Da Ke Gaban Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya

Kungiyar ‘Yan Jarida ta Nijeriya (NUJ), bangaren wakilan gidajen jaridun kasar nan da ke a Jihar Kebbi, sun yi watsi da zaben mambobinta guda uku kacal da za su rika daukar rahotannin Gwamna Nasir Idris a gidan gwamnati da ke Birnin Kebbi.
Hakan na kunshe ne a wata takardar sanarwa da aka raba wa manema labarai da shugabancin kungiyar tasu ta jihar mai dauke da sa hannun shugaban kungiyar Alhaji El-Yukub Usman da sakatarenta Ibrahim Bello a Birnin Kebbi.
  • Ana Kokarin Rantsar Da ‘Yan APC 16 A Majalisar Filato Ta Barauniyar Hanya – Gwamnatin Jihar
Wannan kin amincewa ya biyo bayan wani taron tattaunawa da aka yi a Birnin Kebbi ranar Talata tsakanin mukaddashin Babban sakataren gidan gwamnati, Alhaji Ibrahim Saraki;  mukaddashin Babban sakatare na hidindimun gwamna, Alhaji Sagir Mahe, da mai ba da shawara na musamman kan harkokin yada labarai ga Gwamna Nasir Idris, Malam Yahaya Sarki.
Sauran wadanda suka halarci taron tattaunawar sun hada da, Alhaji Aliyu Bandado, mai bai wa gwamna Idris shawara kan sabbin kafafen yada labarai kuma MC ga Gwamna, Alhaji Faruk Bello-Birnin Kebbi.
A ganawar tasu, sun cimma matsayar cewa gwamnan ya ba da umarnin cewa ba ya son ganin sama da mambobin ‘yan jarida uku da za su rika daukar labarun fadar gwamnatinsa.
Da yake mayar da martani kan wannan, Shugaban kungiyar, Alhaji El-Yakubu Usman-Dabai, ya bayyana wannan matakin a matsayin ‘mara amfani’ ga bangaren inganta ayyukan gwamnatin Kebbi, da kuma aikin jarida.
“A halin yanzu  muna da mambobi sama da 18, Kuma kowani wakili suna da salon daukar labari daban-daban na cikin gida, masu wakiltar kafafen yada labarai daban-daban a ciki da wajen Nijeriya, bai dace ba da rashin da’a a ba da dama ga mambobi uku kacal.
“Ka da jami’an gwamnati su manta da cewa, muna da wakilan talabijin da rediyo da jaridu da kafafen yada labarai na yanar gizo wadanda salon gidajensu ya bambanta da juna.
“Lokacin da kuka dauki jaridu don yin ayyukanku, kuna tauye wa sauran ‘yan jarida hakkinsu na tsarin mulki na sanar da al’ummar Kebbi game da ayyukan alheri da gwamnan yake yi.
“Muna da mutanen da ke zaune a wurare masu nisa da ke dogaro da rediyo da talabijin kawai don samun bayanai game da manufofin gwamnatinsu da shirye-shiryen gwamnatinsu a jihar,” in ji shi.
Usman-Dabai ya bukaci jami’an da abin ya shafa da su janye matakin da suka dauka, kasancewar ‘yan jarida abokan aikinsu ne.
ADVERTISEMENT
ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci
Manyan Labarai

Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci

November 14, 2025
Jan Aikin Da Ke Gaban Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya
Manyan Labarai

Jan Aikin Da Ke Gaban Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya

November 14, 2025
Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4
Manyan Labarai

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

November 13, 2025
Next Post
Bai Kamata Jama’a Su Tsorata Da Bullar Zazzabin Lassa A Adamawa Ba – Kwamishinan Lafiya

Bai Kamata Jama'a Su Tsorata Da Bullar Zazzabin Lassa A Adamawa Ba - Kwamishinan Lafiya

LABARAI MASU NASABA

Abin Da Ya Sa NPA Ta Yi Hadaka Da ‘Snake Island Port’ -Dakta Dantsoho

Abin Da Ya Sa NPA Ta Yi Hadaka Da ‘Snake Island Port’ -Dakta Dantsoho

November 14, 2025
Shugaban NPA Ya Bukaci A Yi Hadaka Domin Cin Gajiyar Albarkatun Fannin Sufurin Afirka

Shugaban NPA Ya Bukaci A Yi Hadaka Domin Cin Gajiyar Albarkatun Fannin Sufurin Afirka

November 14, 2025
Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci

Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci

November 14, 2025
Jan Aikin Da Ke Gaban Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya

Jan Aikin Da Ke Gaban Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya

November 14, 2025
Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

November 13, 2025
Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

November 13, 2025
Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

November 13, 2025
Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

November 13, 2025
Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

November 13, 2025
An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

November 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.