• English
  • Business News
Thursday, August 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Mu Amince Da Ware Mutum Uku Kacal Su Dauki Rahotannin Gwamnan Kebbi Ba – ‘Yan Jarida

by Umar Faruk
1 year ago
in Labarai, Kananan Labarai
0
Ba Mu Amince Da Ware Mutum Uku Kacal Su Dauki Rahotannin Gwamnan Kebbi Ba – ‘Yan Jarida
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Bauchi Ta Amince Da N32,000 A Matsayin Mafi Karancin Kuɗin Fansho

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ya Kawo Wa Afirka Fatan Warware Matsalar Karancin Wutar Lantarki

Kungiyar ‘Yan Jarida ta Nijeriya (NUJ), bangaren wakilan gidajen jaridun kasar nan da ke a Jihar Kebbi, sun yi watsi da zaben mambobinta guda uku kacal da za su rika daukar rahotannin Gwamna Nasir Idris a gidan gwamnati da ke Birnin Kebbi.
Hakan na kunshe ne a wata takardar sanarwa da aka raba wa manema labarai da shugabancin kungiyar tasu ta jihar mai dauke da sa hannun shugaban kungiyar Alhaji El-Yukub Usman da sakatarenta Ibrahim Bello a Birnin Kebbi.
  • Ana Kokarin Rantsar Da ‘Yan APC 16 A Majalisar Filato Ta Barauniyar Hanya – Gwamnatin Jihar
Wannan kin amincewa ya biyo bayan wani taron tattaunawa da aka yi a Birnin Kebbi ranar Talata tsakanin mukaddashin Babban sakataren gidan gwamnati, Alhaji Ibrahim Saraki;  mukaddashin Babban sakatare na hidindimun gwamna, Alhaji Sagir Mahe, da mai ba da shawara na musamman kan harkokin yada labarai ga Gwamna Nasir Idris, Malam Yahaya Sarki.
Sauran wadanda suka halarci taron tattaunawar sun hada da, Alhaji Aliyu Bandado, mai bai wa gwamna Idris shawara kan sabbin kafafen yada labarai kuma MC ga Gwamna, Alhaji Faruk Bello-Birnin Kebbi.
A ganawar tasu, sun cimma matsayar cewa gwamnan ya ba da umarnin cewa ba ya son ganin sama da mambobin ‘yan jarida uku da za su rika daukar labarun fadar gwamnatinsa.
Da yake mayar da martani kan wannan, Shugaban kungiyar, Alhaji El-Yakubu Usman-Dabai, ya bayyana wannan matakin a matsayin ‘mara amfani’ ga bangaren inganta ayyukan gwamnatin Kebbi, da kuma aikin jarida.
“A halin yanzu  muna da mambobi sama da 18, Kuma kowani wakili suna da salon daukar labari daban-daban na cikin gida, masu wakiltar kafafen yada labarai daban-daban a ciki da wajen Nijeriya, bai dace ba da rashin da’a a ba da dama ga mambobi uku kacal.
“Ka da jami’an gwamnati su manta da cewa, muna da wakilan talabijin da rediyo da jaridu da kafafen yada labarai na yanar gizo wadanda salon gidajensu ya bambanta da juna.
“Lokacin da kuka dauki jaridu don yin ayyukanku, kuna tauye wa sauran ‘yan jarida hakkinsu na tsarin mulki na sanar da al’ummar Kebbi game da ayyukan alheri da gwamnan yake yi.
“Muna da mutanen da ke zaune a wurare masu nisa da ke dogaro da rediyo da talabijin kawai don samun bayanai game da manufofin gwamnatinsu da shirye-shiryen gwamnatinsu a jihar,” in ji shi.
Usman-Dabai ya bukaci jami’an da abin ya shafa da su janye matakin da suka dauka, kasancewar ‘yan jarida abokan aikinsu ne.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan JaridaAikiFadar GwamnatiGwamnaKebbiNUJ
ShareTweetSendShare
Previous Post

EFCC Ta Cafke Motoci 21 Makare Da Abincin Da Aka Yi Fasa-kwauri Zuwa Kasashe Makwabta

Next Post

Bai Kamata Jama’a Su Tsorata Da Bullar Zazzabin Lassa A Adamawa Ba – Kwamishinan Lafiya

Related

Gwamnatin Bauchi Ta Amince Da N32,000 A Matsayin Mafi Karancin Kuɗin Fansho
Manyan Labarai

Gwamnatin Bauchi Ta Amince Da N32,000 A Matsayin Mafi Karancin Kuɗin Fansho

19 minutes ago
Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ya Kawo Wa Afirka Fatan Warware Matsalar Karancin Wutar Lantarki
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ya Kawo Wa Afirka Fatan Warware Matsalar Karancin Wutar Lantarki

33 minutes ago
Hukumar Shige Da Fice Ta Ƙara Kuɗin Fasfo Zuwa N100,000, N200,000
Manyan Labarai

Hukumar Shige Da Fice Ta Ƙara Kuɗin Fasfo Zuwa N100,000, N200,000

2 hours ago
Dangote Zai Gina Kamfanin Taki A Habasha Kan Dala Biliyan $2.5
Tattalin Arziki

Dangote Zai Gina Kamfanin Taki A Habasha Kan Dala Biliyan $2.5

3 hours ago
An Kama Matasa 2 Kan Nuna Makamai A Shafukan Sada Zumunta A Kano
Manyan Labarai

An Kama Matasa 2 Kan Nuna Makamai A Shafukan Sada Zumunta A Kano

5 hours ago
’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja
Labarai

’Yansanda Sun Ceto Mutane 16 Da Aka Sace A Edo

6 hours ago
Next Post
Bai Kamata Jama’a Su Tsorata Da Bullar Zazzabin Lassa A Adamawa Ba – Kwamishinan Lafiya

Bai Kamata Jama'a Su Tsorata Da Bullar Zazzabin Lassa A Adamawa Ba - Kwamishinan Lafiya

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Bauchi Ta Amince Da N32,000 A Matsayin Mafi Karancin Kuɗin Fansho

Gwamnatin Bauchi Ta Amince Da N32,000 A Matsayin Mafi Karancin Kuɗin Fansho

August 28, 2025
Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ya Kawo Wa Afirka Fatan Warware Matsalar Karancin Wutar Lantarki

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ya Kawo Wa Afirka Fatan Warware Matsalar Karancin Wutar Lantarki

August 28, 2025
Ƴansandan Libya Sun Kama Ƴan Nijeriya Biyu Kan Zargin Fashi

Ƴansandan Libya Sun Kama Ƴan Nijeriya Biyu Kan Zargin Fashi

August 28, 2025
Hukumar Shige Da Fice Ta Ƙara Kuɗin Fasfo Zuwa N100,000, N200,000

Hukumar Shige Da Fice Ta Ƙara Kuɗin Fasfo Zuwa N100,000, N200,000

August 28, 2025
Dangote Zai Gina Kamfanin Taki A Habasha Kan Dala Biliyan $2.5

Dangote Zai Gina Kamfanin Taki A Habasha Kan Dala Biliyan $2.5

August 28, 2025
Ba Zan Nemi Kujerar Siyasa A 2027 Ba — El-Rufai

Ba Zan Nemi Kujerar Siyasa A 2027 Ba — El-Rufai

August 28, 2025
An Kama Matasa 2 Kan Nuna Makamai A Shafukan Sada Zumunta A Kano

An Kama Matasa 2 Kan Nuna Makamai A Shafukan Sada Zumunta A Kano

August 28, 2025
’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

’Yansanda Sun Ceto Mutane 16 Da Aka Sace A Edo

August 28, 2025
Uwa Da ’Ya’yanta 3 Sun Rasu Bayan Gini Ya Rufta Musu A Zariya

Uwa Da ’Ya’yanta 3 Sun Rasu Bayan Gini Ya Rufta Musu A Zariya

August 28, 2025
ADC Tana Da Damar Kayar Da Tinubu A Zaɓen 2027 – Amaechi

ADC Tana Da Damar Kayar Da Tinubu A Zaɓen 2027 – Amaechi

August 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.