• English
  • Business News
Wednesday, July 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Mu Da Alaƙa Da Duk Wata Talla Ta Zambatar Al’umma – Rundunar Soji 

by Muh'd Shafi'u Saleh
1 year ago
in Labarai
0
Ba Mu Da Alaƙa Da Duk Wata Talla Ta Zambatar Al’umma – Rundunar Soji 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar sojin Nijeriya ta 23 da ke Yola, ta gargadi jama’a game da wata sanarwar talla da ke yawo a kafofin sada-zumunta, kan wani taron bayar da agaji mai taken ‘A 3 Day Charity Exercise/10km Trek 2024’.

Rundunar ta ce, sanarwar ta yi ikirarin gudanar da bukin cika shekaru 25, na hidimar jin kai na kungiyar matan sojojin Nijeriya (NAOWA), da akace za’a gudanar da taron a ofishin jami’an soji da ke Yola daga ranar 8 zuwa 11 ga Fabrairu, 2024.

  • Rundunar Soji Ta Kudancin Sin Ta Gudanar Da Ayyukan Sintiri Na Dakarun Sojin Ruwa Da Na Sama A Tekun Kudancin Kasar
  • ‘Yansanda Sun Kama Dan Bindiga, Sun Ki Karbar Cin Hancin Miliyan 8 A Taraba

Cikin sanarwar da mukaddashin jami’in hulda da jama’a na rundunar sojin da ke Yola, Laftanar Princewill Odoemenam, ya aikewa manema labarai, ta ci gaba da cewa “tallar ana zargin wani mutum mai suna AB Gofai AFOBREF da ya sanya wa hannu, ya ce shi ne Kwamanda, tare da bayar da lambar waya (08123497002).

“Tallar ta bukaci jama’a da su biya kudin talla ta Firstmonie Wallet da Palmpay asusun mai lamba 8132843616, a karkashinsa ansa sunan asusu Captain Jacub BD” inji sanarwar.

Rundunar ta ce “ba tare da wata shakka ba, ba mu da alaka da wannan sanarwa, bamu san wani Kwamanda mai suna AB Gofai ba, kuma bamu da duk wata alaka da wani mutum da aka ce Captain Jacub BD a cikin Runduna ta 23.

Labarai Masu Nasaba

Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano

“Muna gargadin jama’a sosai game da biyan duk wani kudi ga asusun da aka ambata, bugu da kari, rundunar soji ta 23, ta jaddada cewa babu irin wannan shirin gudanar da biki kamar yadda aka bayyana a sama.

“Mun nisanta kan mu da wannan tallar na bogi, tare da shawartar jama’a da su yi taka-tsan-tsan da kaurace wa duk wata kiraye-kiraye na talla, ko daukar nauyin gudanar da wani taron karya da aka ambata a sama.

“Rundunar Sojin Nijeriya, ta dauki al’amuran zamba da mazambata da muhimmanci, tana karfafa wa jama’a gwiwa da su kai rahoton duk wani abin da suke zargi ga hukumomin da suka dace” inji Princewill.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan bindigar SokotoRundunar sojojin NijeriyaYan yahoo
ShareTweetSendShare
Previous Post

Matsalar Tsaron Nijeriya: Ku Faɗi Alkairi Ko Ku Yi Shiru!

Next Post

AFCON 2023: Hasashe Ya Nuna Nijeriya Ce Za Ta Lashe Gasar Cin Kofin Afirika Ta Bana

Related

Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari
Labarai

Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

3 hours ago
VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano
Labarai

VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano

4 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato
Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato

6 hours ago
Ƴansanda Sun Cafke Mutane Biyu Bisa Zargin Kashe Ɗan Ƙasar China
Labarai

Ƴansanda Sun Cafke Mutane Biyu Bisa Zargin Kashe Ɗan Ƙasar China

8 hours ago
Girman Kai Da Son Zuciya Ba Za Su Sa A Amince Ko Ba Da Hadin Kai Ba
Ra'ayi Riga

Girman Kai Da Son Zuciya Ba Za Su Sa A Amince Ko Ba Da Hadin Kai Ba

9 hours ago
Bayan Shekaru 6 A Hannun Boko Haram, Wasu Yara Biyu Sun Kuɓuta
Labarai

Bayan Shekaru 6 A Hannun Boko Haram, Wasu Yara Biyu Sun Kuɓuta

9 hours ago
Next Post
AFCON 2023: Hasashe Ya Nuna Nijeriya Ce Za Ta Lashe Gasar Cin Kofin Afirika Ta Bana

AFCON 2023: Hasashe Ya Nuna Nijeriya Ce Za Ta Lashe Gasar Cin Kofin Afirika Ta Bana

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-9

Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-9

July 15, 2025
Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

July 15, 2025
VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano

VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano

July 15, 2025
Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

July 15, 2025
An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing

An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing

July 15, 2025
Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%

Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%

July 15, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato

July 15, 2025
Shugaba Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Game Da Aikin Raya Birane 

Shugaba Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Game Da Aikin Raya Birane 

July 15, 2025
Ƴansanda Sun Cafke Mutane Biyu Bisa Zargin Kashe Ɗan Ƙasar China

Ƴansanda Sun Cafke Mutane Biyu Bisa Zargin Kashe Ɗan Ƙasar China

July 15, 2025
Taron Matasan Sin Da Afrika Kan Tsaro Zai Kirkiro Wata Sabuwar Mahanga Ta Magance Matsalolin Tsaro

Taron Matasan Sin Da Afrika Kan Tsaro Zai Kirkiro Wata Sabuwar Mahanga Ta Magance Matsalolin Tsaro

July 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.