ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 20, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Taron Matasan Sin Da Afrika Kan Tsaro Zai Kirkiro Wata Sabuwar Mahanga Ta Magance Matsalolin Tsaro

by CGTN Hausa and Sulaiman
11 months ago
Sin

A yau Talata 15 ga wata, ma’aikatar tsaron kasar Sin ta bude taron shugabannin matasa irinsa na farko na dandalin tattaunawar zaman lafiya da tsaro na Sin da Afrika, wanda zai gudana har zuwa ranar 19 ga wata.

Manufar taron wanda zai samu halartar manya da matsakaitan hafsoshin soja kusan 90 daga kasashen Afirka fiye da 40, ita ce kara cimma matsaya, da karfafa hadin kai a fannin zaman lafiya da tsaro, da ba da gudummawa ga gina al’umma mai kyakkyawar makoma ta Sin da Afirka.

  • Bayan Shekaru 6 A Hannun Boko Haram, Wasu Yara Biyu Sun Kuɓuta
  • Girman Kai Da Son Zuciya Ba Za Su Sa A Amince Ko Ba Da Hadin Kai Ba

Tsaro wani muhimmin ginshiki ne na ci gaba da tabbatar da walwalar al’umma. Kafin al’umma ta samu walwala ko wadata, ko bunkasar tattalin arziki, sai ta samu tsaro da kwanciyar hankali. Haka kuma duk wani arziki da kasa ke tinkaho da shi, to ba za ta iya cin gajiyarsa ba muddin tana fama da matsaloli na tsaro.

ADVERTISEMENT

Ba makawa koma bayan tattalin arziki da mawuyacin halin da kasashen Afrika ke fama da su na da alaka mai zurfi da tabarbarewar tsaro da yaki ci yaki cinyewa.

Hakika tunanin kasar Sin abu ne mai matukar burgewa domin ta kan mayar da hankali ne ga neman mafita mai dorewa. Kamar yadda muka sani, matasa, su ne kashin bayan ci gaban kowace al’umma, haka kuma su ne masu tafiya da zamani da ganin irin abubuwan dake faruwa a cikin al’umma. Baya ga haka, su ne za su fi fahimtar yadda bata-gari ke tunani.

LABARAI MASU NASABA

Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin

Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza

Gayyato matasan Afrika da Sin ta yi, yana da muhimmanci ga warware matsalar da kasashensu suke fama da su, kasancewarsu na da kaso mai yawa cikin al’umma, kuma akasari su ne suka fi jin radadin tashe-tashen hankula da yake-yake, don haka yin watsi da ra’ayoyinsu, ba zai taba kawo mafita ga halin rashin tsaro ba. Amma sanya matasa cikin manufofi da dabarun tsaro da na raya kasa, zai kai ga warware tushen matsalolin.

Bugu da kari, tunaninsu ya bambanta da na wadanda suka gabace su, don haka za su iya kirkiro sabbin dabarun samar da mafita da za su kore wadanda aka dade ana amfani da su.

Tabbas ba su dama na tattaunawa da Sin ta yi, ya samar da wata mahanga ta daban, wadda muke sa ran za ta taimaka wajen sauya alkiblar yaki da matsalolin tsaro da za su kawo mafita. Bugu da kari, bisa la’akari da zuwansu, za su koyi darrusa daga kasa mai gogewa kamar Sin, wadda duk da yawan al’ummarta, tabbatar da tsaronsu bai taba gagararta ba.

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Na Kira Da A Ingiza Matakan Siyasa A Kasar Libya
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa
  • Sulaiman
    NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho
  • Sulaiman
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware
  • Sulaiman
    Yadda Gwamnatin Kano Ta Samu Nasarar Kashi 80 A Fannin Aikin Noma

MASU ALAKA

Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin

June 19, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza

June 19, 2026
Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS
Daga Birnin Sin

Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS

June 19, 2026
Next Post
Ƴansanda Sun Cafke Mutane Biyu Bisa Zargin Kashe Ɗan Ƙasar China

Ƴansanda Sun Cafke Mutane Biyu Bisa Zargin Kashe Ɗan Ƙasar China

LABARAI MASU NASABA

2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa

2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa

June 20, 2026
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Abinci

Yadda Gwamnatin Kano Ta Samu Nasarar Kashi 80 A Fannin Aikin Noma

June 19, 2026
Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

June 19, 2026
Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin

Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin

June 19, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

June 19, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza

Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza

June 19, 2026
Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS

Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS

June 19, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.