• English
  • Business News
Sunday, August 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Zan Yarda Da Cin Hanci Da Rashawa A Gwamnatin Zamfara ba – Gwamna Dauda

by Hussein Yero
2 years ago
in Labarai
0
Ba Zan Yarda Da Cin Hanci Da Rashawa A Gwamnatin Zamfara ba – Gwamna Dauda
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Dauda Lawal na Jihar Zamfara, ya ce gwamnatinsa ba za ta amince da duk wani nau’in cin hanci da rashawa ko rashin tausayi daga mambobin majalisarsa ba da ma’aikatan gwamnati a jihar ba.

A ranar Alhamis ne, gwamnan ya jagoranci zaman majalisar zartarwa na musamman a zauren majalisar da ke gidan gwamnatin jihar a Gusau.

  • Minista Kyari, Gwamna Nasir Sun Kaddamar da Shirin Noma Na KADAGE A Kebbi
  • Jimillar Kayayyakin Yau Da Kullum Da Aka Sayar A Sin A Shekarar 2023 Ta Zarce Yuan Triliyan 47

Babban mataimaki na musamman ga gwamna Dauda kan yada labarai, Sulaiman Bala Idris ne, ya bayyana haka a takardar da ya sanya ga manema labarai a Gusau.

A cewarsa Gwamna Dauda Lawal ya bukaci dukkan masu manyan mukamai da kwamishinoni da Shugabanin Kananan hukumomin da masu ba da shawara na musamman da ma’aikata su fahimci manufarsa tare da yin gyare-gyaren da suka dace.

“Dole ne mu kawo canjin da ake bukata domin ciyar da jihar gaba; dole ne mu yi abubuwa daban na kyawawan halaye.

Labarai Masu Nasaba

Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi

“Ba al’ummar jihar ta zabe mu ba don kawai mu maye gurbin fuskoki da halayen wadanda suka gabace mu ba. An zabe mu ne don mu canza yadda ake gudanar da harkokin gwamnati, hanyar da za ta sa mu ci gaban al’umma.”

Gwamnan ya kara nanata wa majalisar zartarwar, cewa ba mun kawo kh ba ne cikin gwamnati don neman kudi.

“Game da haka, ina fada muku duk a yau, ba zan yarda da duk wani aiki na cin hanci da rashawa da rashin tausayi daga kowane mukami ko ma’aikacin gwamnati ba. Na sha cewa ban zo nan don neman kudi ba, kuma duk wanda ke da burin arzuta kan sa gara ya canza shawara ko kuma ya yi murabus daga gwamnati cikin mutunci.

“Kamar yadda na fada a baya, mun zabi kowannen ku ne bisa halayenku. Muna sa ran za ku yi sadaukarwa don canza jiharmu.

“Ba za mu iya cimma wani abu mai yawa ba idan ba mu sake duba ma’aikatan gwamnati da na ma’aikatanmu ba. Ina da niyyar gabatar da kuma sanya ma’aikatan gwamnati abin koyi da zai zama silar ci gaban jiharmu.

“Ina kira ga shugaban ma’aikatan gwamnatin jiha da su gaggauta samar da wata shawara mai amfani kan yadda za a sake fasalin ma’aikatan gwamnati tare da aiwatar da shi zuwa matakin inganci.

“Yayin da nake gyare-gyare a hidimar, ina da niyyar inganta ma’aikatanmu. na shirya horar da ma’aikatanmu na gida da waje.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Cin HanciRashawaZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Minista Kyari, Gwamna Nasir Sun Kaddamar da Shirin Noma Na KADAGE A Kebbi

Next Post

Abdilahi Ismail Abdilahi: Furucin Xi Jinping Ya Burge Ni Matuka

Related

Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina
Labarai

Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

1 hour ago
Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi
Labarai

Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi

2 hours ago
Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21
Labarai

Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21

4 hours ago
Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM
Labarai

ADC Ta Yi Allah-wadai Da Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM A Neja

9 hours ago
Gwamnatin Katsina Ta Gabatar Da Matsayarta A Taron Jin Ra’ayiyin Jama’a
Labarai

Gwamnatin Katsina Ta Gabatar Da Matsayarta A Taron Jin Ra’ayiyin Jama’a

10 hours ago
Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare
Manyan Labarai

Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare

11 hours ago
Next Post
Abdilahi Ismail Abdilahi: Furucin Xi Jinping Ya Burge Ni Matuka

Abdilahi Ismail Abdilahi: Furucin Xi Jinping Ya Burge Ni Matuka

LABARAI MASU NASABA

Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

August 3, 2025
Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi

Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi

August 3, 2025
Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu?

Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu?

August 3, 2025
Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21

Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21

August 3, 2025
An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu

An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu

August 3, 2025
Rikici Ya Ɓarke A Zaɓen Ribas, Ƴan PDP Sun Fito A Matsayin Ƴan Takarar APC

Rikici Ya Ɓarke A Zaɓen Ribas, Ƴan PDP Sun Fito A Matsayin Ƴan Takarar APC

August 3, 2025
Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin

Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin

August 3, 2025
Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar

Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar

August 3, 2025
Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

August 3, 2025
Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa

Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa

August 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.