• English
  • Business News
Friday, October 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Zan Yarda Da Cin Hanci Da Rashawa A Gwamnatin Zamfara ba – Gwamna Dauda

by Hussein Yero
2 years ago
Zamfara

Gwamna Dauda Lawal na Jihar Zamfara, ya ce gwamnatinsa ba za ta amince da duk wani nau’in cin hanci da rashawa ko rashin tausayi daga mambobin majalisarsa ba da ma’aikatan gwamnati a jihar ba.

A ranar Alhamis ne, gwamnan ya jagoranci zaman majalisar zartarwa na musamman a zauren majalisar da ke gidan gwamnatin jihar a Gusau.

  • Minista Kyari, Gwamna Nasir Sun Kaddamar da Shirin Noma Na KADAGE A Kebbi
  • Jimillar Kayayyakin Yau Da Kullum Da Aka Sayar A Sin A Shekarar 2023 Ta Zarce Yuan Triliyan 47

Babban mataimaki na musamman ga gwamna Dauda kan yada labarai, Sulaiman Bala Idris ne, ya bayyana haka a takardar da ya sanya ga manema labarai a Gusau.

A cewarsa Gwamna Dauda Lawal ya bukaci dukkan masu manyan mukamai da kwamishinoni da Shugabanin Kananan hukumomin da masu ba da shawara na musamman da ma’aikata su fahimci manufarsa tare da yin gyare-gyaren da suka dace.

“Dole ne mu kawo canjin da ake bukata domin ciyar da jihar gaba; dole ne mu yi abubuwa daban na kyawawan halaye.

LABARAI MASU NASABA

Nnamdi Kanu Ya Sake Bayyana A Kotu Ba Tare Da Lauya Ba, Zai Kare Kansa Da Kansa

Ƙungiyoyin Ma’aikatan Jihar Kaduna Sun Yabawa Gwamna Sani Kan Amincewa Da Sabon Albashin  Ma’aikata

“Ba al’ummar jihar ta zabe mu ba don kawai mu maye gurbin fuskoki da halayen wadanda suka gabace mu ba. An zabe mu ne don mu canza yadda ake gudanar da harkokin gwamnati, hanyar da za ta sa mu ci gaban al’umma.”

Gwamnan ya kara nanata wa majalisar zartarwar, cewa ba mun kawo kh ba ne cikin gwamnati don neman kudi.

“Game da haka, ina fada muku duk a yau, ba zan yarda da duk wani aiki na cin hanci da rashawa da rashin tausayi daga kowane mukami ko ma’aikacin gwamnati ba. Na sha cewa ban zo nan don neman kudi ba, kuma duk wanda ke da burin arzuta kan sa gara ya canza shawara ko kuma ya yi murabus daga gwamnati cikin mutunci.

“Kamar yadda na fada a baya, mun zabi kowannen ku ne bisa halayenku. Muna sa ran za ku yi sadaukarwa don canza jiharmu.

“Ba za mu iya cimma wani abu mai yawa ba idan ba mu sake duba ma’aikatan gwamnati da na ma’aikatanmu ba. Ina da niyyar gabatar da kuma sanya ma’aikatan gwamnati abin koyi da zai zama silar ci gaban jiharmu.

“Ina kira ga shugaban ma’aikatan gwamnatin jiha da su gaggauta samar da wata shawara mai amfani kan yadda za a sake fasalin ma’aikatan gwamnati tare da aiwatar da shi zuwa matakin inganci.

“Yayin da nake gyare-gyare a hidimar, ina da niyyar inganta ma’aikatanmu. na shirya horar da ma’aikatanmu na gida da waje.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Nnamdi Kanu Ya Sake Bayyana A Kotu Ba Tare Da Lauya Ba, Zai Kare Kansa Da Kansa
Manyan Labarai

Nnamdi Kanu Ya Sake Bayyana A Kotu Ba Tare Da Lauya Ba, Zai Kare Kansa Da Kansa

October 24, 2025
Uba Sani Ya Amince Da Biyan Naira Biliyan ₦2.3 Ga Tsofaffin Ma’aikata Da Iyalansu
Labarai

Ƙungiyoyin Ma’aikatan Jihar Kaduna Sun Yabawa Gwamna Sani Kan Amincewa Da Sabon Albashin  Ma’aikata

October 24, 2025
Ƙarfin Niyyar Manzon Allah (SAW) Da Matakinsa Na Aƙlul A’ala
Manyan Labarai

Ƙarfin Niyyar Manzon Allah (SAW) Da Matakinsa Na Aƙlul A’ala

October 24, 2025
Next Post
Abdilahi Ismail Abdilahi: Furucin Xi Jinping Ya Burge Ni Matuka

Abdilahi Ismail Abdilahi: Furucin Xi Jinping Ya Burge Ni Matuka

LABARAI MASU NASABA

Nnamdi Kanu Ya Sake Bayyana A Kotu Ba Tare Da Lauya Ba, Zai Kare Kansa Da Kansa

Nnamdi Kanu Ya Sake Bayyana A Kotu Ba Tare Da Lauya Ba, Zai Kare Kansa Da Kansa

October 24, 2025
Uba Sani Ya Amince Da Biyan Naira Biliyan ₦2.3 Ga Tsofaffin Ma’aikata Da Iyalansu

Ƙungiyoyin Ma’aikatan Jihar Kaduna Sun Yabawa Gwamna Sani Kan Amincewa Da Sabon Albashin  Ma’aikata

October 24, 2025
Ƙarfin Niyyar Manzon Allah (SAW) Da Matakinsa Na Aƙlul A’ala

Ƙarfin Niyyar Manzon Allah (SAW) Da Matakinsa Na Aƙlul A’ala

October 24, 2025
Gobara Ta Tafka Ɓarna A Kasuwar Shuwaki, Ta Ƙona Fiye da Rumfuna 500 A Kano

Gobara Ta Tafka Ɓarna A Kasuwar Shuwaki, Ta Ƙona Fiye da Rumfuna 500 A Kano

October 24, 2025
Gwarzuwar Shekarar 2025 Sanata Oluremi Tinubu

Gwarzuwar Shekarar 2025 Sanata Oluremi Tinubu

October 24, 2025
Dauda Lawal Gwarzon Gwamnan 2025: Ceto Zamfara Domin Ci Gaba

Dauda Lawal Gwarzon Gwamnan 2025: Ceto Zamfara Domin Ci Gaba

October 24, 2025
Buƙatar Daƙile Badaƙalar Amfani Da Takardun Karatun Bogi A Nijeriya

Buƙatar Daƙile Badaƙalar Amfani Da Takardun Karatun Bogi A Nijeriya

October 24, 2025
Fahimtar Sabon Tunani: Samar Da Wadata Ga Dukkan Jama’a Ta Daidaita Gibin Dake Tsakanin Hamshakai Da Matalauta

Fahimtar Sabon Tunani: Samar Da Wadata Ga Dukkan Jama’a Ta Daidaita Gibin Dake Tsakanin Hamshakai Da Matalauta

October 23, 2025
Shugaban Senegal: Kasar Sin Ta Zama Abin Koyi Ga Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Senegal: Kasar Sin Ta Zama Abin Koyi Ga Kasashe Masu Tasowa

October 23, 2025
Sojoji Sun Kashe Mayakan Boko Haram 6, Sun Kama Wasu A Borno

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 50, Sun Daƙile Hare-Hare A Borno

October 23, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.