• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Zan Yarda Da Cin Hanci Da Rashawa A Gwamnatin Zamfara ba – Gwamna Dauda

byHussein Yero
2 years ago
Zamfara

Gwamna Dauda Lawal na Jihar Zamfara, ya ce gwamnatinsa ba za ta amince da duk wani nau’in cin hanci da rashawa ko rashin tausayi daga mambobin majalisarsa ba da ma’aikatan gwamnati a jihar ba.

A ranar Alhamis ne, gwamnan ya jagoranci zaman majalisar zartarwa na musamman a zauren majalisar da ke gidan gwamnatin jihar a Gusau.

  • Minista Kyari, Gwamna Nasir Sun Kaddamar da Shirin Noma Na KADAGE A Kebbi
  • Jimillar Kayayyakin Yau Da Kullum Da Aka Sayar A Sin A Shekarar 2023 Ta Zarce Yuan Triliyan 47

Babban mataimaki na musamman ga gwamna Dauda kan yada labarai, Sulaiman Bala Idris ne, ya bayyana haka a takardar da ya sanya ga manema labarai a Gusau.

A cewarsa Gwamna Dauda Lawal ya bukaci dukkan masu manyan mukamai da kwamishinoni da Shugabanin Kananan hukumomin da masu ba da shawara na musamman da ma’aikata su fahimci manufarsa tare da yin gyare-gyaren da suka dace.

“Dole ne mu kawo canjin da ake bukata domin ciyar da jihar gaba; dole ne mu yi abubuwa daban na kyawawan halaye.

LABARAI MASU NASABA

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

“Ba al’ummar jihar ta zabe mu ba don kawai mu maye gurbin fuskoki da halayen wadanda suka gabace mu ba. An zabe mu ne don mu canza yadda ake gudanar da harkokin gwamnati, hanyar da za ta sa mu ci gaban al’umma.”

Gwamnan ya kara nanata wa majalisar zartarwar, cewa ba mun kawo kh ba ne cikin gwamnati don neman kudi.

“Game da haka, ina fada muku duk a yau, ba zan yarda da duk wani aiki na cin hanci da rashawa da rashin tausayi daga kowane mukami ko ma’aikacin gwamnati ba. Na sha cewa ban zo nan don neman kudi ba, kuma duk wanda ke da burin arzuta kan sa gara ya canza shawara ko kuma ya yi murabus daga gwamnati cikin mutunci.

“Kamar yadda na fada a baya, mun zabi kowannen ku ne bisa halayenku. Muna sa ran za ku yi sadaukarwa don canza jiharmu.

“Ba za mu iya cimma wani abu mai yawa ba idan ba mu sake duba ma’aikatan gwamnati da na ma’aikatanmu ba. Ina da niyyar gabatar da kuma sanya ma’aikatan gwamnati abin koyi da zai zama silar ci gaban jiharmu.

“Ina kira ga shugaban ma’aikatan gwamnatin jiha da su gaggauta samar da wata shawara mai amfani kan yadda za a sake fasalin ma’aikatan gwamnati tare da aiwatar da shi zuwa matakin inganci.

“Yayin da nake gyare-gyare a hidimar, ina da niyyar inganta ma’aikatanmu. na shirya horar da ma’aikatanmu na gida da waje.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Next Post
Abdilahi Ismail Abdilahi: Furucin Xi Jinping Ya Burge Ni Matuka

Abdilahi Ismail Abdilahi: Furucin Xi Jinping Ya Burge Ni Matuka

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version