• English
  • Business News
Friday, July 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Minista Kyari, Gwamna Nasir Sun Kaddamar da Shirin Noma Na KADAGE A Kebbi

by Umar Faruk
1 year ago
in Labarai
0
Minista Kyari, Gwamna Nasir Sun Kaddamar da Shirin Noma Na KADAGE A Kebbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mai girma ministan noma da samar da abinci, Sanata Abubakar Kyari da gwamna Nasir Idris sun kaddamar da shirin bunkasa noma mai taken KADAGE a Karamar Hukumar Suru da ke Jihar Kebbi.

A shirin an raba famfunan ruwa masu amfani da hasken rana da injinan wutar lantarki ga manoma a karkashin shirin bunkasa noma da ci gaban mai taken KADAGE.

  • Kafofin Yada Labarai Na Yamma Bayin Kudi Ne
  • Tsaro: Gwamnatin Zamfara Ta Haramta Wa Sarakuna Bada Izinin Hakar Ma’adanai

A cewar ministan, Shugaba Bola Tinubu, ya himmatu wajen inganta harkar noma da kuma samar da wadataccen abinci a kasar nan daidai da ajanda takwas na shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu.

“Shugaba Tinubu ya sanya batun samar da abinci na daya a cikin ajandarsa takwas ta hanyar inganta noma a kasar nan.

“Dukkan shirye-shiryen da ke cikin ajandar na da alaka da noma, kamar samar da arziki da kawar da fatara da bunkasa tattalin arziki.

Labarai Masu Nasaba

Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal

Kotu Ta Yanke Wa Ɗan TikTok Tsulange Hukuncin Ɗauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci

“Shugaban kasa ya damu da yadda manoma za su iya samun kayan aikin noma kuma a yanzu ya fara wani tsari na hanzarta samar da irin wadannan kayan amfanin gona ga manoma,” in ji shi.

Sanata Kyari, ya sanar da taron cewa Gwamna Nasir Idris ya kai ziyara a ofishinsa da ke Abuja domin tattauna hanyoyin inganta noma a jihar.

“Ta hanyar ayyukan Gwamna Idris, ya ‘tattaki zance’ ta hanyar sayo da raba famfunan ruwa masu amfani da hasken rana guda 6,000 da sauran kayan aiki don bunkasa noman ban ruwa a jihar,” in ji shi.

Ministan ya lura cewa noman a duk shekara zai bunkasa noman amfanin gona, da kara samar da ayyukan yi, da rage fatara, da rage hauhawar farashin abinci da kuma kara hada kai.

“Wadannan manufofi ne da aka bayyana a cikin Shirin Sabunta Fata na Shugaba Tinubu. Jihar Kebbi na daya daga cikin jihohin da aka zaba domin noman rani,” inji shi.

Ya yaba wa gwamnan bisa goyon bayan da ya bayar bisa ga kiran da shugaba Tinubu ya yi na hada hannu tsakanin gwamnatin tarayya da na jihohi domin tabbatar da samar da kayayyakin noma ga manoma domin a samu nasarar samar da isasshen abinci.

Da yake raba kayan amfanin gonan, gwamnan jihar Kebbi, Dakta Nasir Idris, ya ce gwamnatinsa za ta raba famfunan ruwa masu amfani da hasken rana guda 12,000, inda za a fara raba 6,000 ga manoma domin su kara yawan amfanin gona.

“Gwamnatin jihar za ta sayo raka’a 20,000 na famfunan iskar Gas (CNG) masu amfani da ruwan famfo a matsayin tallafi ga fanfuna masu amfani da hasken rana domin kara yawan manoman da za su amfana a jihar,” in ji shi.

Dokta Nasir ya gargadi wadanda suka amfana da kada su sayar da kayayyakin, inda ya ce gwamnati za ta dauki matakin ladabtarwa a kan duk wanda aka samu yana sayar da famfon da aka bashi don aikin bunkasa noma a jihar, in ji shi.

“Na rantse da Allah duk wani jami’in gwamnati da ke da hannu wajen rabon kayayyakin da aka samu da hannu wajen karkatar da su, za a kama shi kuma a hukunta shi.

“Na umarci dukkan shugabannin hukumomin tsaro da suka hada da kungiyoyin ‘yan banga da su sanya ido a kan yadda ake raba kayayyakin tare da daukar matakin da ya dace kan masu karya doka,” in ji shi.

Ya kuma kara da bayyyana cewa magabacinsa, Sen. Atiku Bagudu, ya yi iya kokarinsa wajen sanya jihar a taswirar duniya a matsayin sa na kan gaba wajen noman shinkafa a kasar nan.

Gwamnan ya bada tabbacin cewa zai karfafa aikin da aka samu tare da inganta noman noman.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KebbiNoma
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kafofin Yada Labarai Na Yamma Bayin Kudi Ne

Next Post

Ba Zan Yarda Da Cin Hanci Da Rashawa A Gwamnatin Zamfara ba – Gwamna Dauda

Related

Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal
Labarai

Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal

10 hours ago
Kotu Ta Yanke Wa Ɗan TikTok Tsulange Hukuncin Ɗauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci
Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Ɗan TikTok Tsulange Hukuncin Ɗauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci

11 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 1,191, Sun Ceto 543 Cikin Watanni Uku
Tsaro

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 1,191, Sun Ceto 543 Cikin Watanni Uku

12 hours ago
Dutsen Da Amurka Ta Jefa Ya Fado Kasa
Ra'ayi Riga

Dutsen Da Amurka Ta Jefa Ya Fado Kasa

12 hours ago
Kamfanin Simintin Dangote Ya Tallafa Wa Manoma 50 A Benue
Labarai

Kamfanin Simintin Dangote Ya Tallafa Wa Manoma 50 A Benue

13 hours ago
Gwamnatin Yobe Ta Rufe Kasuwanni Uku Saboda Fargabar Hare-haren Boko Haram
Manyan Labarai

Gwamnatin Yobe Ta Rufe Kasuwanni Uku Saboda Fargabar Hare-haren Boko Haram

15 hours ago
Next Post
Ba Zan Yarda Da Cin Hanci Da Rashawa A Gwamnatin Zamfara ba – Gwamna Dauda

Ba Zan Yarda Da Cin Hanci Da Rashawa A Gwamnatin Zamfara ba - Gwamna Dauda

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Kara Rungumar Nau’o’in Makamashi Marasa Gurbata Muhalli

Sin Na Kara Rungumar Nau’o’in Makamashi Marasa Gurbata Muhalli

July 3, 2025
Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC

Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC

July 3, 2025
Mai Tsaron Ragar Nijeriya, Peter Rufai Ya Rasu

Mai Tsaron Ragar Nijeriya, Peter Rufai Ya Rasu

July 3, 2025
Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 

Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 

July 3, 2025
Ƴan PDP Na Fice Wa Na Barin Jam’iyyar Ga Wike Da Ƴan Koransa –  Dele Momodu

Ƴan PDP Na Fice Wa Na Barin Jam’iyyar Ga Wike Da Ƴan Koransa –  Dele Momodu

July 3, 2025
Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattaunawa Kan Zaman Lafiya Na Duniya Karo Na 13

Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattaunawa Kan Zaman Lafiya Na Duniya Karo Na 13

July 3, 2025
Kuriar Jin Raayoyin Jamaa Na CGTN Ta Shaida Yadda Akasarin Jamaa Ke Ganin Baiken Kudurin Dokar Bunkasa Amurka

Kuriar Jin Raayoyin Jamaa Na CGTN Ta Shaida Yadda Akasarin Jamaa Ke Ganin Baiken Kudurin Dokar Bunkasa Amurka

July 3, 2025
Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal

Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal

July 3, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Labaran Sinawa Na Yakin Kin Harin Sojojin Japan Bisa Fifikonta Na Yayata Labarai A Duniya

CMG Za Ta Gabatar Da Labaran Sinawa Na Yakin Kin Harin Sojojin Japan Bisa Fifikonta Na Yayata Labarai A Duniya

July 3, 2025
Kotu Ta Yanke Wa Ɗan TikTok Tsulange Hukuncin Ɗauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci

Kotu Ta Yanke Wa Ɗan TikTok Tsulange Hukuncin Ɗauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci

July 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.