ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Minista Kyari, Gwamna Nasir Sun Kaddamar da Shirin Noma Na KADAGE A Kebbi

by Umar Faruk
2 years ago
Noma

Mai girma ministan noma da samar da abinci, Sanata Abubakar Kyari da gwamna Nasir Idris sun kaddamar da shirin bunkasa noma mai taken KADAGE a Karamar Hukumar Suru da ke Jihar Kebbi.

A shirin an raba famfunan ruwa masu amfani da hasken rana da injinan wutar lantarki ga manoma a karkashin shirin bunkasa noma da ci gaban mai taken KADAGE.

  • Kafofin Yada Labarai Na Yamma Bayin Kudi Ne
  • Tsaro: Gwamnatin Zamfara Ta Haramta Wa Sarakuna Bada Izinin Hakar Ma’adanai

A cewar ministan, Shugaba Bola Tinubu, ya himmatu wajen inganta harkar noma da kuma samar da wadataccen abinci a kasar nan daidai da ajanda takwas na shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu.

ADVERTISEMENT

“Shugaba Tinubu ya sanya batun samar da abinci na daya a cikin ajandarsa takwas ta hanyar inganta noma a kasar nan.

“Dukkan shirye-shiryen da ke cikin ajandar na da alaka da noma, kamar samar da arziki da kawar da fatara da bunkasa tattalin arziki.

LABARAI MASU NASABA

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

“Shugaban kasa ya damu da yadda manoma za su iya samun kayan aikin noma kuma a yanzu ya fara wani tsari na hanzarta samar da irin wadannan kayan amfanin gona ga manoma,” in ji shi.

Sanata Kyari, ya sanar da taron cewa Gwamna Nasir Idris ya kai ziyara a ofishinsa da ke Abuja domin tattauna hanyoyin inganta noma a jihar.

“Ta hanyar ayyukan Gwamna Idris, ya ‘tattaki zance’ ta hanyar sayo da raba famfunan ruwa masu amfani da hasken rana guda 6,000 da sauran kayan aiki don bunkasa noman ban ruwa a jihar,” in ji shi.

Ministan ya lura cewa noman a duk shekara zai bunkasa noman amfanin gona, da kara samar da ayyukan yi, da rage fatara, da rage hauhawar farashin abinci da kuma kara hada kai.

“Wadannan manufofi ne da aka bayyana a cikin Shirin Sabunta Fata na Shugaba Tinubu. Jihar Kebbi na daya daga cikin jihohin da aka zaba domin noman rani,” inji shi.

Ya yaba wa gwamnan bisa goyon bayan da ya bayar bisa ga kiran da shugaba Tinubu ya yi na hada hannu tsakanin gwamnatin tarayya da na jihohi domin tabbatar da samar da kayayyakin noma ga manoma domin a samu nasarar samar da isasshen abinci.

Da yake raba kayan amfanin gonan, gwamnan jihar Kebbi, Dakta Nasir Idris, ya ce gwamnatinsa za ta raba famfunan ruwa masu amfani da hasken rana guda 12,000, inda za a fara raba 6,000 ga manoma domin su kara yawan amfanin gona.

“Gwamnatin jihar za ta sayo raka’a 20,000 na famfunan iskar Gas (CNG) masu amfani da ruwan famfo a matsayin tallafi ga fanfuna masu amfani da hasken rana domin kara yawan manoman da za su amfana a jihar,” in ji shi.

Dokta Nasir ya gargadi wadanda suka amfana da kada su sayar da kayayyakin, inda ya ce gwamnati za ta dauki matakin ladabtarwa a kan duk wanda aka samu yana sayar da famfon da aka bashi don aikin bunkasa noma a jihar, in ji shi.

“Na rantse da Allah duk wani jami’in gwamnati da ke da hannu wajen rabon kayayyakin da aka samu da hannu wajen karkatar da su, za a kama shi kuma a hukunta shi.

“Na umarci dukkan shugabannin hukumomin tsaro da suka hada da kungiyoyin ‘yan banga da su sanya ido a kan yadda ake raba kayayyakin tare da daukar matakin da ya dace kan masu karya doka,” in ji shi.

Ya kuma kara da bayyyana cewa magabacinsa, Sen. Atiku Bagudu, ya yi iya kokarinsa wajen sanya jihar a taswirar duniya a matsayin sa na kan gaba wajen noman shinkafa a kasar nan.

Gwamnan ya bada tabbacin cewa zai karfafa aikin da aka samu tare da inganta noman noman.

Noma
Umar Faruk
+ postsBio
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk-2/
    Nijeriya Da Jamhuriyar Benin Za Su Sassauta Tsanantawa A Kan Iyakokinsu Ga ‘Yan Kasuwa
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk-2/
    Hajjin Bana: Shettima Zai Kaddamar Da Jirgin Farko Na Maniyyata 430 A Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk-2/
    Jami’an Tsaro sun Ceto Mata Biyu da aka Yi Garkuwa da Su A Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk-2/
    Majalisar Dokokin Kebbi Ta Dakatar Da Dan Majalisa Mai Wakiltar Birnin Kebbi Ta Arewa

MASU ALAKA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Next Post
Ba Zan Yarda Da Cin Hanci Da Rashawa A Gwamnatin Zamfara ba – Gwamna Dauda

Ba Zan Yarda Da Cin Hanci Da Rashawa A Gwamnatin Zamfara ba - Gwamna Dauda

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.