• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Zan yi Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ba, Cewar Dikko Radda

by El-Zaharadeen Umar
2 years ago
in Labarai
0
Ba Zan yi Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ba, Cewar Dikko Radda
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umar Radda ya bayyana cewa gwamnatinsa ba za ta taba yin sulhu ko sasanci da ‘yan bindiga ba. 

Raddaa ya yi wannan ikirarin ne a lokacin taron addu’o’i na musamman da gwamnati jihar Katsina ta shirya domin samun saukin matsalar tsaro da ake fama da ita a jihar tuntuni.

  • An Kammala Harhada Tushen Sashe Na SMR A Sin
  • Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka Na Kara Haifar Da Da Mai Ido

Ya yi karin haske da cewa zai iya sauraren dan bindigar da ya ajiye makaminsa ya yadda ya rungumi zaman lafiya kuma ya zauna cikin al’umma to za a mayae da shi kuma za a saurare shi.

“Duk dan bindigar da bai yadda da zaman lafiya ba, zamu sa kafar wando daya da shi, kuma ba zamu saurara masa ba,” in ji shi.

Ya ce za su duk mai yiwuwa wajen ganin sun yi maganin ‘yan ta’adda da suka hana jama’a zaman lafiya ta hanyar karfafa jami’an tsaro da ba su kayan aiki da duk wani taimako da suke bukata.

Labarai Masu Nasaba

An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki

Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

Sannan ya yi kira ga jama’a da su je kai tsaye gidan gwamnatin jihar Katsina domin ba da bayanan sirri da za su taimaka wajen maganin duk wanda ke da hannu a wannan ta’adanci.

Gwamnan na Katsina ya shiga jerin ayarin jami’an tsaro da ke Katsina domin yin farautar kauraye a cikin garin Katsina da suke kwancen waya a hannun jama’a har kwana biyu a jere.

Haka kuma gwamnan ya yi kira ga daukacin al’umma da su ci gaba da yin addu’o’i da kaskantar da kai wajen Allah domin samun nasarar matsalar tsaro da ake fama da ita.

Kazalika, ya bai wa jama’a hakuri a kan halin kuncin da aka shiga na rayuwa, inda ya ce yanzu shirye-shirye sun yi nisa domin raba abinci kyauta ga ma bukata.

“Za mu raba wannan abinci a dukkanin runfunan zabe da muke da su a fadin jihar Katsina domin sauÆ™aÆ™awa jama’a halin kuncin da ake ciki na rayuwa,” in ji gwamnan.

Gwamnan ya yi karin haske dangane da matsalar da ke faruwa tsakanin gwamnatin Nijeriya da kuma kasar Nijar da ta fuskanci juyin mulki, inda ya ce nan gaba kadan za a samu maslaha in Allah ya yarda.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KatsinaRaddaSulhu
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Kammala Harhada Tushen Sashe Na SMR A Sin

Next Post

Bukatar Taka-tsan-tsan A Kan Shirin Daukar Matakin Soja A Nijar

Related

An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki
Labarai

An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki

47 minutes ago
Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi
Labarai

Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

1 hour ago
Radda
Labarai

Murnar Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (2)

4 hours ago
Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 
Rahotonni

Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 

4 hours ago
Matatar Dangote Ta Dakatar Da Zuwa ÆŠaukar Man Fetur, Sai Dai Ka Saya Ta Kai Ma
Labarai

Matatar Dangote Ta Dakatar Da Zuwa ÆŠaukar Man Fetur, Sai Dai Ka Saya Ta Kai Ma

5 hours ago
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Harajin Kashi 4 Na Shigo Da Kaya Wanda Ya Janyo Cece-kuce

5 hours ago
Next Post
Gwamnatin Sojin Nijar Ta Yi Sabbin Nade-Nade

Bukatar Taka-tsan-tsan A Kan Shirin Daukar Matakin Soja A Nijar

LABARAI MASU NASABA

An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki

An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki

September 19, 2025
Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

September 19, 2025
Radda

Murnar Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (2)

September 19, 2025
Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 

Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 

September 19, 2025
Matatar Dangote Ta Dakatar Da Zuwa ÆŠaukar Man Fetur, Sai Dai Ka Saya Ta Kai Ma

Matatar Dangote Ta Dakatar Da Zuwa ÆŠaukar Man Fetur, Sai Dai Ka Saya Ta Kai Ma

September 19, 2025

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Harajin Kashi 4 Na Shigo Da Kaya Wanda Ya Janyo Cece-kuce

September 19, 2025
GORON JUMA’A 01-07-2025

GORON JUMA’A 19-09-2025

September 19, 2025
Radda

2027: Su Wane Ne Ke Tsoron Guguwar Makinde A Jam’iyyar  PDP

September 19, 2025
Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

September 19, 2025
Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

September 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.