Babban Hafsan Sojin kasa (COAS), Laftanar Janar Taoreed Lagbaja, ya nemi sojojin Nijeriya da su rubanya kokarinsu na yi wa kasa hidima musamman a yaki da rashin tsaro.
Ya amince cewa, sojojin suna aiki cikin “mawuyacin yanayi mai matukar kalubale” amma akwai bukatar kara jajircewar.
- An Kaddamar Taron Tattaunawa Game Da Raya Bangaren Al’adun Sin
- Lookman Ya Zura Kwallo Uku Rigis Yayin Da Atalanta Ta Lashe Kofin Europa League
Lagbaja ya yi wannan kiran ne a ranar Alhamis yayin da yake jawabi ga sojojin yayin ziyarar aiki da ya kai a runduna ta 35 da ke Barikin Alamala, Abeokuta, a Jihar Ogun.
Lagbaja ya tabbatar wa dakarun cewa, hedikwatar rundunar tsaro ta kasa, ta himmatu wajen shawo kan kalubalen da sojojin ke fuskanta cikin gaggawa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp