• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babban Taron LEADERSHIP Karo Na 14 Zai Gudana Ranar Talata

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Babban Taron LEADERSHIP Karo Na 14 Zai Gudana Ranar Talata
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Idan Allah ya kaimu ranar Talata 31 ga watan Janairun 2023, Kamfanin LEADER-SHIP zai gudanar da babban taronsa wanda ya saba gudanarwa a duk shekara.

Taron karo na 14 da zai gudana a Babbar Cbiyar Taro ta Duniya da ke Abuja.

  • A Sake Lale Kan Mayar Da Tubabbun ‘Yan Boko Haram Jihohinsu Na Asali
  • Majalisa Ta Tabbatar Da Arase A Matsayin Sabon Shugaban Hukumar Kula Da ‘Yansanda

Ana sa ran Tsohon Firaministan Kenya, Raila Amolo Odinga zai kasance babban bako mai jawabi inda zai gabatar da makala mai taken “sahihin zabe da tattalin arziki a yanayin sauyi”.

Har ila yau, mai martaba Etsu Nupe kuma shugaban majalisar sarakunan Jihar Neja, Alhaji Yahaya Abubakar shi ne zai kasance uban taro a ranar.

Wasu manyan masu rike da mukamai za su raka sarkin zuwa dakin taron na LEADERSHIP da kuma bayar da lambar yabo.

Labarai Masu Nasaba

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

Babban taron na LEADERSHIP dai, zai kuma kunshi gabatar da lambobin yabo ga wasu fitattun ‘yan Nijeriya da kungiyoyi da suka nuna bajinta wajen kawo ci ga-ban kasa da na al’umma daban-daban.

Idan dai ba a manta ba, Kamfanin LEADERSHIP ya sanar da karrama wasu masha-huran mutane a shekarar 2021, wadanda suka hada da shugaban Bankin Afredim, Farfesa Benedict Oramah da shugaban hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi, (NDLEA) Birgediya Mohammed Buba Marwa (mai ritaya) da kuma Olu-watobilobi Ayomide Amusan, wadanda suka lashe kyautar zama gwarazan kam-fanin a shekarar 2021.

A taron na bana, Gwamnan Jihar Kaduna, Nasiru el-Rufa’I yana daya daga cikin gwarazan gwamnoni wanda zai samu karramawa bisa kyakkyawan shugabancinsa, musamman kokarin da ya yi na kawo canji a Jihar Kaduna ta han-yar bunkasa tattalin arziki, samar da ababen more rayuwa da ba a taba ganin irinsa ba da kuma gyara ma’aikatun gwamnati da cibiyoyin hukuma a jihar.

Haka shi ma Gwamna Abiodun ya samu nasarar lashe kyautar zama gwarzon gwamnan na shekara, saboda himmarsa wajen samar da ababen more rayuwa da kuma ci gaban da ya samu na fadada martabar kasuwanci a jiharsa.

Shi ma Gwamna Ifeayi Ugwanyi ya lashe lambar yabo ta gwarzon gwamnan she-karar 2022, saboda dora jiharsa kan turbar samun ‘yancin gashin kai da kuma samar da ci gaba a bangaren ababen more rayuwa a fadin jiharsa, duk da kalu-balen tsaro da jihar ke fuskanta.

Wadanda suka kasance gwarazan shugabannin ma’aikatun gwamnati da kamfan-in LEADERSHIP zai karrama sun hada da shugaban hukumar tara haraji ta kasa (FIRS), Muhammad Mamman Nami da Darakta Janar na Asusun Horaswa na (ITF), Joseph Ari, da kuma Shugaban Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa (NIS), Isa Jere Idris.

Bankin LOTUS shi ne ya lashe gwarzon bankin shekara na LEADERSHIP, saboda sabbin abubuwan da ya kawo na kare martabar masu hannun jari.

Har ila yau, za a karrama, Fasto Solomon Folorunsho a matsayin gwarzon kyau-tata rayuwar al’umma, saboda irin gudummar da gidauniyarsa ta bai wa jama’a duk da karancin kudaden da ake fuskanta.

A bangaren gwarzuwar shugaban banki kuma, Manajan Daraktan Bankin Fidelity, Misis Nneke Onyealu-Ikpe, ce ta lashe bisa jajircewarta wajen tallafa wa kananun ‘yan kasuwa da kudade a rassa daban-daban. Yayin da Manajan Daraktan Mojec International Holding, Misis Chantelle Abdul ta kasance gwarzuwar ‘yar kasuwa ta shekara.

Hukumar NSCDC ita ce ta lashe kyautar gwarzuwar hukumar gwamnati ta she-karar 2022, bisa gagarumin ci gaba da hukumar ta samu a cikin shekara daya.

Sauran wadanda za a karrama sun hada da gwarzon kamfanin shekara wanda za a bai wa BUA, bisa zama kamfanin da ke da mafi kyawon hannun jari a wannan shekarar, yayin da MTN kuma ya lashe gwarzon kamfanin sadarwa na shekara bisa kwarewarsa wajen sadarwa.

Mama Pride, daya daga cikin shinkafar gida wanda ta yi saurin karbuwa ita ce ta lashe gwarzuwar kayan kamfani na shekara.

Bugu da kari, Kamfanin LEADERSHIP zai bayar da kyautar gwarzon sashen mai da gas da ke amfani da kayan cikin gida ga Babban Sakataren hukumar kula da ci ga-ban abububuwan da ake samarwa a Nijeriya, Mista Simbi Wabote.

A wannan shekarar, mawakin nan mai wakar Turanci na bangaren kade-kade da wake-waken Afro Pop RnB-hop, Kiss Daniel shi ne ya lashe gwarzon dan nishadi.

Tawagar ‘yan kwallo mata na ‘yan kasa da shekaru 17 ta Nijeriya ita ce ta lashe lambar yabon gwarzuwar tawagar ‘yan wasa, bisa yadda ta wakilci kasar a gasar FIFA, inda ta ci wa Nijeriya lambar yabo a gasar Olympic ta lokacin zafi da aka gudanar a Rio de Janeiro ta kasar, yayin da wani yaro dan shekara 13 dan aji hudu a matakin firamare  mai hazaka daga Jihar Borno, Musa Sani, wanda ya zana fa-salin gadar sama ta Maiduguri ta hanyar amfani da laka, ya lashe kyautar LEAD-ERSHI ta gwarzon matashi na shekara.

Za a fara gudanar da babban taron ne dai da hantsin ranar Talata zuwa azuhur.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: LEADERSHIPTaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

Naja’atu: Cikon Banci Ce A Wurinmu, Tun Da Muka Kore Ta Take Ta Sambatu – APC   

Next Post

An Kama Wani Da Ake Zargi Da Hannu A Harin Jirgin Kasan Kaduna Zuwa Abuja

Related

JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

2 hours ago
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

7 hours ago
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte
Manyan Labarai

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

11 hours ago
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?
Manyan Labarai

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

12 hours ago
Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar
Manyan Labarai

Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

1 day ago
Wata Mata Ta Kashe Dan Hayar Da Ke Gidanta A Ondo
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban APC A Ondo, Sun Nemi N100m

1 day ago
Next Post
An Kama Wani Da Ake Zargi Da Hannu A Harin Jirgin Kasan Kaduna Zuwa Abuja

An Kama Wani Da Ake Zargi Da Hannu A Harin Jirgin Kasan Kaduna Zuwa Abuja

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

May 14, 2025
Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

May 14, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

May 14, 2025
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

May 14, 2025
Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

May 14, 2025
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.