• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babban Taron LEADERSHIP Karo Na 14 Zai Gudana Ranar Talata

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Babban Taron LEADERSHIP Karo Na 14 Zai Gudana Ranar Talata
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Idan Allah ya kaimu ranar Talata 31 ga watan Janairun 2023, Kamfanin LEADER-SHIP zai gudanar da babban taronsa wanda ya saba gudanarwa a duk shekara.

Taron karo na 14 da zai gudana a Babbar Cbiyar Taro ta Duniya da ke Abuja.

  • A Sake Lale Kan Mayar Da Tubabbun ‘Yan Boko Haram Jihohinsu Na Asali
  • Majalisa Ta Tabbatar Da Arase A Matsayin Sabon Shugaban Hukumar Kula Da ‘Yansanda

Ana sa ran Tsohon Firaministan Kenya, Raila Amolo Odinga zai kasance babban bako mai jawabi inda zai gabatar da makala mai taken “sahihin zabe da tattalin arziki a yanayin sauyi”.

Har ila yau, mai martaba Etsu Nupe kuma shugaban majalisar sarakunan Jihar Neja, Alhaji Yahaya Abubakar shi ne zai kasance uban taro a ranar.

Wasu manyan masu rike da mukamai za su raka sarkin zuwa dakin taron na LEADERSHIP da kuma bayar da lambar yabo.

Labarai Masu Nasaba

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

Babban taron na LEADERSHIP dai, zai kuma kunshi gabatar da lambobin yabo ga wasu fitattun ‘yan Nijeriya da kungiyoyi da suka nuna bajinta wajen kawo ci ga-ban kasa da na al’umma daban-daban.

Idan dai ba a manta ba, Kamfanin LEADERSHIP ya sanar da karrama wasu masha-huran mutane a shekarar 2021, wadanda suka hada da shugaban Bankin Afredim, Farfesa Benedict Oramah da shugaban hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi, (NDLEA) Birgediya Mohammed Buba Marwa (mai ritaya) da kuma Olu-watobilobi Ayomide Amusan, wadanda suka lashe kyautar zama gwarazan kam-fanin a shekarar 2021.

A taron na bana, Gwamnan Jihar Kaduna, Nasiru el-Rufa’I yana daya daga cikin gwarazan gwamnoni wanda zai samu karramawa bisa kyakkyawan shugabancinsa, musamman kokarin da ya yi na kawo canji a Jihar Kaduna ta han-yar bunkasa tattalin arziki, samar da ababen more rayuwa da ba a taba ganin irinsa ba da kuma gyara ma’aikatun gwamnati da cibiyoyin hukuma a jihar.

Haka shi ma Gwamna Abiodun ya samu nasarar lashe kyautar zama gwarzon gwamnan na shekara, saboda himmarsa wajen samar da ababen more rayuwa da kuma ci gaban da ya samu na fadada martabar kasuwanci a jiharsa.

Shi ma Gwamna Ifeayi Ugwanyi ya lashe lambar yabo ta gwarzon gwamnan she-karar 2022, saboda dora jiharsa kan turbar samun ‘yancin gashin kai da kuma samar da ci gaba a bangaren ababen more rayuwa a fadin jiharsa, duk da kalu-balen tsaro da jihar ke fuskanta.

Wadanda suka kasance gwarazan shugabannin ma’aikatun gwamnati da kamfan-in LEADERSHIP zai karrama sun hada da shugaban hukumar tara haraji ta kasa (FIRS), Muhammad Mamman Nami da Darakta Janar na Asusun Horaswa na (ITF), Joseph Ari, da kuma Shugaban Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa (NIS), Isa Jere Idris.

Bankin LOTUS shi ne ya lashe gwarzon bankin shekara na LEADERSHIP, saboda sabbin abubuwan da ya kawo na kare martabar masu hannun jari.

Har ila yau, za a karrama, Fasto Solomon Folorunsho a matsayin gwarzon kyau-tata rayuwar al’umma, saboda irin gudummar da gidauniyarsa ta bai wa jama’a duk da karancin kudaden da ake fuskanta.

A bangaren gwarzuwar shugaban banki kuma, Manajan Daraktan Bankin Fidelity, Misis Nneke Onyealu-Ikpe, ce ta lashe bisa jajircewarta wajen tallafa wa kananun ‘yan kasuwa da kudade a rassa daban-daban. Yayin da Manajan Daraktan Mojec International Holding, Misis Chantelle Abdul ta kasance gwarzuwar ‘yar kasuwa ta shekara.

Hukumar NSCDC ita ce ta lashe kyautar gwarzuwar hukumar gwamnati ta she-karar 2022, bisa gagarumin ci gaba da hukumar ta samu a cikin shekara daya.

Sauran wadanda za a karrama sun hada da gwarzon kamfanin shekara wanda za a bai wa BUA, bisa zama kamfanin da ke da mafi kyawon hannun jari a wannan shekarar, yayin da MTN kuma ya lashe gwarzon kamfanin sadarwa na shekara bisa kwarewarsa wajen sadarwa.

Mama Pride, daya daga cikin shinkafar gida wanda ta yi saurin karbuwa ita ce ta lashe gwarzuwar kayan kamfani na shekara.

Bugu da kari, Kamfanin LEADERSHIP zai bayar da kyautar gwarzon sashen mai da gas da ke amfani da kayan cikin gida ga Babban Sakataren hukumar kula da ci ga-ban abububuwan da ake samarwa a Nijeriya, Mista Simbi Wabote.

A wannan shekarar, mawakin nan mai wakar Turanci na bangaren kade-kade da wake-waken Afro Pop RnB-hop, Kiss Daniel shi ne ya lashe gwarzon dan nishadi.

Tawagar ‘yan kwallo mata na ‘yan kasa da shekaru 17 ta Nijeriya ita ce ta lashe lambar yabon gwarzuwar tawagar ‘yan wasa, bisa yadda ta wakilci kasar a gasar FIFA, inda ta ci wa Nijeriya lambar yabo a gasar Olympic ta lokacin zafi da aka gudanar a Rio de Janeiro ta kasar, yayin da wani yaro dan shekara 13 dan aji hudu a matakin firamare  mai hazaka daga Jihar Borno, Musa Sani, wanda ya zana fa-salin gadar sama ta Maiduguri ta hanyar amfani da laka, ya lashe kyautar LEAD-ERSHI ta gwarzon matashi na shekara.

Za a fara gudanar da babban taron ne dai da hantsin ranar Talata zuwa azuhur.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: LEADERSHIPTaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

Naja’atu: Cikon Banci Ce A Wurinmu, Tun Da Muka Kore Ta Take Ta Sambatu – APC   

Next Post

An Kama Wani Da Ake Zargi Da Hannu A Harin Jirgin Kasan Kaduna Zuwa Abuja

Related

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

11 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

13 hours ago
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

15 hours ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

16 hours ago
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Manyan Labarai

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

16 hours ago
Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu
Manyan Labarai

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

21 hours ago
Next Post
An Kama Wani Da Ake Zargi Da Hannu A Harin Jirgin Kasan Kaduna Zuwa Abuja

An Kama Wani Da Ake Zargi Da Hannu A Harin Jirgin Kasan Kaduna Zuwa Abuja

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.