• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babbar Kasa Ita Ce Mai Jagorantar Sauran Kasashe Wajen Tabbatar Da Zaman Lafiya A Duniya

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Babbar Kasa Ita Ce Mai Jagorantar Sauran Kasashe Wajen Tabbatar Da Zaman Lafiya A Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A baya-bayan nan ana ta samu karuwar rikici tsakanin bangarorin Isra’ila da Falasdinu, lamarin da ke haifar da asarar rayuka da jikkata da tsaiko ga harkokin ibada. Rikici tsakanin bangarorin biyu abu ne da yaki ci yaki cinyewa, wanda ke haifar da damuwa a yankin gabas ta tsakiya da ma duniya baki daya.

A matsayinta na kasa mai burin ganin dunkulewar duniya cikin zaman lafiya da ci gaba, kasar Sin ta bakin firaministanta Qin Gang, ta ce za ta samar da yanayin da ya dace na ganin an samu sulhu tsakanin bangarorin biyu.

  • Kasar Sin Ta Soki Amurka Bisa Kakabawa Wasu Kamfanoninta Takunkumi Dangane Da Batun Maganin Fentanyl

Tabbas, lokaci ya yi da ya kamata a ce an samu mai shiga tsakani mai adalci, domin lalubo mafita da kawo karshen wannan daddaden rikici.

Da yake tattaunwa jiya Litinin ta wayar tarho da takwarorinsa na Falasdinu Riad Maliki da na Isra’ila Eli Cohen, Qin Gang ya ce a shirye kasarsa take ta tallafawa tattaunawar wanzar da zaman lafiya tsakanin bangarorin tare da samar da damar cimma nasarar hakan.

Hakika burin Sin shi ne ganin an samar da zaman lafiya da hadin gwiwa da hakuri da girmama juna tsakanin kasa da kasa da al’ummunsu. Dole a samu bambance bambance tsakanin bangarori daban daban, amma kai zuciya nesa da hakuri da wadannan bambance-bambance, shi zai kai ga samun tabbatuwar zama lafiya a duniya da ma samun ci gaba.

Labarai Masu Nasaba

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Kasar Sin misali ce, domin ta kasance kasa mai kabilu da mabiya addinai daban-daban, amma abun ban sha’awa shi ne, yadda wadannan al’ummomi suka amince da yanayinsu kuma suke hakuri da juna, sannan suke morar zaman lafiya mai inganci.

Kasancewar na fito daga kasa mai mabanbantan kabilu da addinai, na kan yi matukar sha’awar yadda al’ummomin Sin ke zaune lafiya da juna ba tare da tsangwama ba. Don haka a ganina, babu kasar da ta fi dacewa wajen jagorantar sulhu tsakanin Falasdinu da Isra’ila, kamar kasar Sin.

Kamar yadda Sin ta taka muhimmiyar rawa wajen dawo da dangantakar da ta yi tsami tsakanin Saudiyya da Iran, ina da yakinin za ta cimma nasara wajen shawo kan rikicin wadannan bangarori dake zaman makwabtan juna. Kuma a matsayin wadda ta tabbatar da zaman lafiya a cikin gida, na yi imanin idan har aka bata dama, Sin za ta iya gabatar da dabaru da matakai na shawo kan wannan rikici da yaki ci yaki cinyewa.

Lokaci ya yi da ya kamata sauran kasashen duniya su goyawa Sin baya kan wannan buri nata, a maimaikon bangaranci da rura wutar rikicin.

Matsayin babbar kasar da ta san ya kamata, shi ne jagorantar sauran kasashe wajen samar da zaman lafiya da ci gaba mai dorewa, kuma wannan, shi ne matsayin kasar Sin a duniya. (Faeza Mustapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Rarara Ya Bukaci Kotu Ta Yi Watsi Da Karar Da Ake Masa

Next Post

Kotu Ta Yi Watsi Da Bukatar APC Kan Kalubalantar Ingancin Zaben Abba Gida-gida

Related

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang
Daga Birnin Sin

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

7 hours ago
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka
Daga Birnin Sin

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

8 hours ago
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya
Daga Birnin Sin

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

9 hours ago
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14
Daga Birnin Sin

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

10 hours ago
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing
Daga Birnin Sin

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

11 hours ago
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar
Daga Birnin Sin

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

13 hours ago
Next Post
Kotu Ta Yi Watsi Da Bukatar APC Kan Kalubalantar Ingancin Zaben Abba Gida-gida

Kotu Ta Yi Watsi Da Bukatar APC Kan Kalubalantar Ingancin Zaben Abba Gida-gida

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

September 18, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.