• English
  • Business News
Saturday, August 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babbar Kasa Ita Ce Mai Jagorantar Sauran Kasashe Wajen Tabbatar Da Zaman Lafiya A Duniya

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Babbar Kasa Ita Ce Mai Jagorantar Sauran Kasashe Wajen Tabbatar Da Zaman Lafiya A Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A baya-bayan nan ana ta samu karuwar rikici tsakanin bangarorin Isra’ila da Falasdinu, lamarin da ke haifar da asarar rayuka da jikkata da tsaiko ga harkokin ibada. Rikici tsakanin bangarorin biyu abu ne da yaki ci yaki cinyewa, wanda ke haifar da damuwa a yankin gabas ta tsakiya da ma duniya baki daya.

A matsayinta na kasa mai burin ganin dunkulewar duniya cikin zaman lafiya da ci gaba, kasar Sin ta bakin firaministanta Qin Gang, ta ce za ta samar da yanayin da ya dace na ganin an samu sulhu tsakanin bangarorin biyu.

  • Kasar Sin Ta Soki Amurka Bisa Kakabawa Wasu Kamfanoninta Takunkumi Dangane Da Batun Maganin Fentanyl

Tabbas, lokaci ya yi da ya kamata a ce an samu mai shiga tsakani mai adalci, domin lalubo mafita da kawo karshen wannan daddaden rikici.

Da yake tattaunwa jiya Litinin ta wayar tarho da takwarorinsa na Falasdinu Riad Maliki da na Isra’ila Eli Cohen, Qin Gang ya ce a shirye kasarsa take ta tallafawa tattaunawar wanzar da zaman lafiya tsakanin bangarorin tare da samar da damar cimma nasarar hakan.

Hakika burin Sin shi ne ganin an samar da zaman lafiya da hadin gwiwa da hakuri da girmama juna tsakanin kasa da kasa da al’ummunsu. Dole a samu bambance bambance tsakanin bangarori daban daban, amma kai zuciya nesa da hakuri da wadannan bambance-bambance, shi zai kai ga samun tabbatuwar zama lafiya a duniya da ma samun ci gaba.

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

Kasar Sin misali ce, domin ta kasance kasa mai kabilu da mabiya addinai daban-daban, amma abun ban sha’awa shi ne, yadda wadannan al’ummomi suka amince da yanayinsu kuma suke hakuri da juna, sannan suke morar zaman lafiya mai inganci.

Kasancewar na fito daga kasa mai mabanbantan kabilu da addinai, na kan yi matukar sha’awar yadda al’ummomin Sin ke zaune lafiya da juna ba tare da tsangwama ba. Don haka a ganina, babu kasar da ta fi dacewa wajen jagorantar sulhu tsakanin Falasdinu da Isra’ila, kamar kasar Sin.

Kamar yadda Sin ta taka muhimmiyar rawa wajen dawo da dangantakar da ta yi tsami tsakanin Saudiyya da Iran, ina da yakinin za ta cimma nasara wajen shawo kan rikicin wadannan bangarori dake zaman makwabtan juna. Kuma a matsayin wadda ta tabbatar da zaman lafiya a cikin gida, na yi imanin idan har aka bata dama, Sin za ta iya gabatar da dabaru da matakai na shawo kan wannan rikici da yaki ci yaki cinyewa.

Lokaci ya yi da ya kamata sauran kasashen duniya su goyawa Sin baya kan wannan buri nata, a maimaikon bangaranci da rura wutar rikicin.

Matsayin babbar kasar da ta san ya kamata, shi ne jagorantar sauran kasashe wajen samar da zaman lafiya da ci gaba mai dorewa, kuma wannan, shi ne matsayin kasar Sin a duniya. (Faeza Mustapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Rarara Ya Bukaci Kotu Ta Yi Watsi Da Karar Da Ake Masa

Next Post

Kotu Ta Yi Watsi Da Bukatar APC Kan Kalubalantar Ingancin Zaben Abba Gida-gida

Related

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

14 hours ago
Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

15 hours ago
Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana
Daga Birnin Sin

Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

16 hours ago
Ministan Tsaron Kasar Sin Ya Nanata Shan Damarar PLA A Kan Sake Hadewar Kasar
Daga Birnin Sin

Ministan Tsaron Kasar Sin Ya Nanata Shan Damarar PLA A Kan Sake Hadewar Kasar

17 hours ago
An Bude Atisayen “Hadin Gwiwa Na Teku Na 2025″ Tsakanin Sin Da Rasha
Daga Birnin Sin

An Bude Atisayen “Hadin Gwiwa Na Teku Na 2025″ Tsakanin Sin Da Rasha

18 hours ago
Zhao Leji Ya Yi Jawabi A Babban Taron Shugabannin Majalisun Kasa Da Kasa Karo Na 6
Daga Birnin Sin

Zhao Leji Ya Yi Jawabi A Babban Taron Shugabannin Majalisun Kasa Da Kasa Karo Na 6

19 hours ago
Next Post
Kotu Ta Yi Watsi Da Bukatar APC Kan Kalubalantar Ingancin Zaben Abba Gida-gida

Kotu Ta Yi Watsi Da Bukatar APC Kan Kalubalantar Ingancin Zaben Abba Gida-gida

LABARAI MASU NASABA

Sabon Shugaban Matatar Dangote Ya Bayyana Shirin Faɗaɗa Ayyukanta

Sabon Shugaban Matatar Dangote Ya Bayyana Shirin Faɗaɗa Ayyukanta

August 2, 2025
Manyan Ƙalubale Takwas Da Ke Shafar Farashin Tumatir

Manyan Ƙalubale Takwas Da Ke Shafar Farashin Tumatir

August 2, 2025
Kwamitin Tantance Makarantun Gaba da Sakandire Na Bogi Ya Yi Wa Yankin Funtua Dirar Mikiya

Kwamitin Tantance Makarantun Gaba da Sakandire Na Bogi Ya Yi Wa Yankin Funtua Dirar Mikiya

August 2, 2025
Yarjejeniyar Dala Biliyan Ɗaya Da Ƙasar Brazil Za Ta Haɓaka Fannin Noma A Nijeriya —Tinubu

Yarjejeniyar Dala Biliyan Ɗaya Da Ƙasar Brazil Za Ta Haɓaka Fannin Noma A Nijeriya —Tinubu

August 2, 2025
ADC Za Ta Kayar Da Tinubu A 2027 – Dino Melaye

ADC Za Ta Kayar Da Tinubu A 2027 – Dino Melaye

August 2, 2025
Ƴansanda Sun Ƙwato Mota Da Aka Sace, Gami Da Cafke Dillalan Ƙwayoyi A Jigawa

Ƴansanda Sun Ƙwato Mota Da Aka Sace, Gami Da Cafke Dillalan Ƙwayoyi A Jigawa

August 2, 2025
Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa

Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa

August 1, 2025
Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

August 1, 2025
2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

August 1, 2025
Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

August 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.