• English
  • Business News
Monday, June 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babbar Kasa Ita Ce Mai Jagorantar Sauran Kasashe Wajen Tabbatar Da Zaman Lafiya A Duniya

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Babbar Kasa Ita Ce Mai Jagorantar Sauran Kasashe Wajen Tabbatar Da Zaman Lafiya A Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A baya-bayan nan ana ta samu karuwar rikici tsakanin bangarorin Isra’ila da Falasdinu, lamarin da ke haifar da asarar rayuka da jikkata da tsaiko ga harkokin ibada. Rikici tsakanin bangarorin biyu abu ne da yaki ci yaki cinyewa, wanda ke haifar da damuwa a yankin gabas ta tsakiya da ma duniya baki daya.

A matsayinta na kasa mai burin ganin dunkulewar duniya cikin zaman lafiya da ci gaba, kasar Sin ta bakin firaministanta Qin Gang, ta ce za ta samar da yanayin da ya dace na ganin an samu sulhu tsakanin bangarorin biyu.

  • Kasar Sin Ta Soki Amurka Bisa Kakabawa Wasu Kamfanoninta Takunkumi Dangane Da Batun Maganin Fentanyl

Tabbas, lokaci ya yi da ya kamata a ce an samu mai shiga tsakani mai adalci, domin lalubo mafita da kawo karshen wannan daddaden rikici.

Da yake tattaunwa jiya Litinin ta wayar tarho da takwarorinsa na Falasdinu Riad Maliki da na Isra’ila Eli Cohen, Qin Gang ya ce a shirye kasarsa take ta tallafawa tattaunawar wanzar da zaman lafiya tsakanin bangarorin tare da samar da damar cimma nasarar hakan.

Hakika burin Sin shi ne ganin an samar da zaman lafiya da hadin gwiwa da hakuri da girmama juna tsakanin kasa da kasa da al’ummunsu. Dole a samu bambance bambance tsakanin bangarori daban daban, amma kai zuciya nesa da hakuri da wadannan bambance-bambance, shi zai kai ga samun tabbatuwar zama lafiya a duniya da ma samun ci gaba.

Labarai Masu Nasaba

Za A Gudanar Da Taron Davos Na Yanayin Zafi Na Bana A Birnin Tianjin

Me Ya Sa Kamfanonin Kasa Da Kasa Ke Da Imanin Gudanar Da Harkokinsu A Kasar Sin?

Kasar Sin misali ce, domin ta kasance kasa mai kabilu da mabiya addinai daban-daban, amma abun ban sha’awa shi ne, yadda wadannan al’ummomi suka amince da yanayinsu kuma suke hakuri da juna, sannan suke morar zaman lafiya mai inganci.

Kasancewar na fito daga kasa mai mabanbantan kabilu da addinai, na kan yi matukar sha’awar yadda al’ummomin Sin ke zaune lafiya da juna ba tare da tsangwama ba. Don haka a ganina, babu kasar da ta fi dacewa wajen jagorantar sulhu tsakanin Falasdinu da Isra’ila, kamar kasar Sin.

Kamar yadda Sin ta taka muhimmiyar rawa wajen dawo da dangantakar da ta yi tsami tsakanin Saudiyya da Iran, ina da yakinin za ta cimma nasara wajen shawo kan rikicin wadannan bangarori dake zaman makwabtan juna. Kuma a matsayin wadda ta tabbatar da zaman lafiya a cikin gida, na yi imanin idan har aka bata dama, Sin za ta iya gabatar da dabaru da matakai na shawo kan wannan rikici da yaki ci yaki cinyewa.

Lokaci ya yi da ya kamata sauran kasashen duniya su goyawa Sin baya kan wannan buri nata, a maimaikon bangaranci da rura wutar rikicin.

Matsayin babbar kasar da ta san ya kamata, shi ne jagorantar sauran kasashe wajen samar da zaman lafiya da ci gaba mai dorewa, kuma wannan, shi ne matsayin kasar Sin a duniya. (Faeza Mustapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Rarara Ya Bukaci Kotu Ta Yi Watsi Da Karar Da Ake Masa

Next Post

Kotu Ta Yi Watsi Da Bukatar APC Kan Kalubalantar Ingancin Zaben Abba Gida-gida

Related

Za A Gudanar Da Taron Davos Na Yanayin Zafi Na Bana A Birnin Tianjin
Daga Birnin Sin

Za A Gudanar Da Taron Davos Na Yanayin Zafi Na Bana A Birnin Tianjin

4 hours ago
Me Ya Sa Kamfanonin Kasa Da Kasa Ke Da Imanin Gudanar Da Harkokinsu A Kasar Sin?
Daga Birnin Sin

Me Ya Sa Kamfanonin Kasa Da Kasa Ke Da Imanin Gudanar Da Harkokinsu A Kasar Sin?

6 hours ago
Gwamnatin Hong Kong Ta Gudanar Da Bikin Cika Shekaru Biyar Da Kafuwar Dokar Tsaron Kasa Ta Yankin
Daga Birnin Sin

Gwamnatin Hong Kong Ta Gudanar Da Bikin Cika Shekaru Biyar Da Kafuwar Dokar Tsaron Kasa Ta Yankin

8 hours ago
Sin Ta Yi Matukar Allah Wadai Da Hare-Haren Da Amurka Ta Kaiwa Iran
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Matukar Allah Wadai Da Hare-Haren Da Amurka Ta Kaiwa Iran

9 hours ago
CMG Ya Ja Hankulan Baki A Dandalin Tattaunawar Tattalin Arziki Na Kasa Da Kasa Na St. Petersburg Karo Na 28 
Daga Birnin Sin

CMG Ya Ja Hankulan Baki A Dandalin Tattaunawar Tattalin Arziki Na Kasa Da Kasa Na St. Petersburg Karo Na 28 

1 day ago
Yankin Taiwan Ya Yi Taron Bikin Bauta Na Kakan Gargajiyar Sin Fuxi
Daga Birnin Sin

Yankin Taiwan Ya Yi Taron Bikin Bauta Na Kakan Gargajiyar Sin Fuxi

1 day ago
Next Post
Kotu Ta Yi Watsi Da Bukatar APC Kan Kalubalantar Ingancin Zaben Abba Gida-gida

Kotu Ta Yi Watsi Da Bukatar APC Kan Kalubalantar Ingancin Zaben Abba Gida-gida

LABARAI MASU NASABA

2027: Wajibi Ne A Saka Sakamakon Zaɓe A Na’ura – Farfesa Jega

2027: Wajibi Ne A Saka Sakamakon Zaɓe A Na’ura – Farfesa Jega

June 22, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

June 22, 2025
Za A Gudanar Da Taron Davos Na Yanayin Zafi Na Bana A Birnin Tianjin

Za A Gudanar Da Taron Davos Na Yanayin Zafi Na Bana A Birnin Tianjin

June 22, 2025
Mun Gano Wurare 52 Da Ake Aikata Laifuka A Kano – Janar Mai Adda’u

Mun Gano Wurare 52 Da Ake Aikata Laifuka A Kano – Janar Mai Adda’u

June 22, 2025
Me Ya Sa Kamfanonin Kasa Da Kasa Ke Da Imanin Gudanar Da Harkokinsu A Kasar Sin?

Me Ya Sa Kamfanonin Kasa Da Kasa Ke Da Imanin Gudanar Da Harkokinsu A Kasar Sin?

June 22, 2025
Rashford Na Fatan Buga Ƙwallo Tare Da Lamine Yamal A Barcelona

Rashford Na Fatan Buga Ƙwallo Tare Da Lamine Yamal A Barcelona

June 22, 2025
Tinubu Ya Yi Allah-Wadai Da Harin Bam A Borno, Ya Yi Alhinin Fashewar Wani A Kano

Tinubu Ya Yi Allah-Wadai Da Harin Bam A Borno, Ya Yi Alhinin Fashewar Wani A Kano

June 22, 2025
Gwamnatin Hong Kong Ta Gudanar Da Bikin Cika Shekaru Biyar Da Kafuwar Dokar Tsaron Kasa Ta Yankin

Gwamnatin Hong Kong Ta Gudanar Da Bikin Cika Shekaru Biyar Da Kafuwar Dokar Tsaron Kasa Ta Yankin

June 22, 2025
Barayin Wayar Lantarki Sun Addabi A’lummar Jihar Kebbi

Barayin Wayar Lantarki Sun Addabi A’lummar Jihar Kebbi

June 22, 2025
Sin Ta Yi Matukar Allah Wadai Da Hare-Haren Da Amurka Ta Kaiwa Iran

Sin Ta Yi Matukar Allah Wadai Da Hare-Haren Da Amurka Ta Kaiwa Iran

June 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.