• English
  • Business News
Saturday, September 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babbar Kasa Mai Farar Aniya: Shin Har Yanzu Akwai Masu Son Lalata Dangantakar Sin Da Afrika?

by CGTN Hausa and Sulaiman
10 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Babbar Kasa Mai Farar Aniya: Shin Har Yanzu Akwai Masu Son Lalata Dangantakar Sin Da Afrika?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sin babbar kasa mai tasowa, mai karfin tattalin arziki na biyu a duniya, kuma babbar abokiyar huldar kasashen Afrika, na ci gaba da nunawa duniya cewa, ita din mai neman ci gaban duniya ce, haka kuma kawa ce abin dogora a ko da yaushe.

 

Ba abun mamaki ba ne yadda na fara da yabon kasar Sin, saboda har kullum kasar na ci gaba da kasancewa a bar yabo da koyi.

  • Shawarar BRI Na Samar Da Wani Yanayi Mai Yakini Ga Tattalin Arzikin Duniya
  • Alternative Bank Shi Ne Mafi Inganci Da Baya Amfani Da Kuɗin Ruwa Da Zuwa Da Fasaha A 2024

A ranar Lahadin da ta gabata, kasar ta kaddamar da manufar dauke haraji na kaso 100 bisa 100 kan wasu hajojin dake shiga kasar daga kasashen Afrika masu karancin wadata dake da huldar diplomasiyya da ita.

 

Labarai Masu Nasaba

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

Shin daga cikin kasashe masu kiran kansu manya ko ke shafawa kasar Sin bakin fenti a wajen kasashen Afrika, suna cewa tana kokarin dana musu tarkon bashi da sauran karairayi, akwai wadda ta yi wa kasashen Afrika irin wannan tagomashi? Kasar Sin ce babbar kasa mai tasowa ta farko, kuma ta farko cikin kasashe masu karfin tattalin arziki da ta dauki irin wannan mataki.

 

Hakan da ta yi, ya sake bayyanawa duniya kyakkyawar niyyar kasar Sin ta ganin kasashe masu karancin kudin shiga sun samu damar fitar da kayayyakinsu zuwa kasarta domin cin gajiyar babbar kasuwarta tare da samun wadata da ci gaba. Har ila yau, ta sake tabbatar da manufarta ta sake fadada bude kofa ga kasashen waje domin su ci gajiyar gogewarta da ci gabanta.

 

Kamar yadda na saba fada, ci gaban kasar Sin ci gaba ne ga sauran kasashe ba kalubale ba. Kuma kasar ba ta kyashin ci gaban sauran kasashe, sabanin yadda wasu ke yi mata bita da kulli da kokarin ganin ta durkushe. Yayin da take samun ci gaba ta hanyar kirkire-kirkiren fasahohi da aiwatar da sabbin dabaru, kasashe masu son ci gaba da kaunar zaman lafiya, na iya hada gwiwa da ita domin raya kansu. Don haka duk mai son ganin durkushewar kasar Sin, to ba da ci gabanta kadai yake adawa ba, har da na kasashe masu tasowa da ma sauran kasashen duniya ba ki daya. (Fa’iza Muhammad Mustapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Ya Ce Sin Ta Dukafa Wajen Ganin Duniya Na Amfana Da Magungunan Gargajiya Yadda Ya Kamata

Next Post

Gwamnatin Za Ta Samar Wa Matasa Miliyan 20 Guraben Aiki A Ƙarkashin Shirin NIYEEDEP 

Related

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu
Daga Birnin Sin

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

7 hours ago
An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan
Daga Birnin Sin

An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

8 hours ago
Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

9 hours ago
Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka
Daga Birnin Sin

Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

10 hours ago
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata
Daga Birnin Sin

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

11 hours ago
Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”
Daga Birnin Sin

Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

12 hours ago
Next Post
Gwamnatin Za Ta Samar Wa Matasa Miliyan 20 Guraben Aiki A Ƙarkashin Shirin NIYEEDEP 

Gwamnatin Za Ta Samar Wa Matasa Miliyan 20 Guraben Aiki A Ƙarkashin Shirin NIYEEDEP 

LABARAI MASU NASABA

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

September 19, 2025
Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

September 19, 2025
An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

September 19, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

September 19, 2025
Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

September 19, 2025
Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

September 19, 2025
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

September 19, 2025
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

September 19, 2025
Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

September 19, 2025
Sin

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

September 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.