ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, November 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babbar Kasa Mai Farar Aniya: Shin Har Yanzu Akwai Masu Son Lalata Dangantakar Sin Da Afrika?

by CGTN Hausa and Sulaiman
12 months ago
Sin

Sin babbar kasa mai tasowa, mai karfin tattalin arziki na biyu a duniya, kuma babbar abokiyar huldar kasashen Afrika, na ci gaba da nunawa duniya cewa, ita din mai neman ci gaban duniya ce, haka kuma kawa ce abin dogora a ko da yaushe.

 

Ba abun mamaki ba ne yadda na fara da yabon kasar Sin, saboda har kullum kasar na ci gaba da kasancewa a bar yabo da koyi.

ADVERTISEMENT
  • Shawarar BRI Na Samar Da Wani Yanayi Mai Yakini Ga Tattalin Arzikin Duniya
  • Alternative Bank Shi Ne Mafi Inganci Da Baya Amfani Da Kuɗin Ruwa Da Zuwa Da Fasaha A 2024

A ranar Lahadin da ta gabata, kasar ta kaddamar da manufar dauke haraji na kaso 100 bisa 100 kan wasu hajojin dake shiga kasar daga kasashen Afrika masu karancin wadata dake da huldar diplomasiyya da ita.

 

LABARAI MASU NASABA

Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

Shin daga cikin kasashe masu kiran kansu manya ko ke shafawa kasar Sin bakin fenti a wajen kasashen Afrika, suna cewa tana kokarin dana musu tarkon bashi da sauran karairayi, akwai wadda ta yi wa kasashen Afrika irin wannan tagomashi? Kasar Sin ce babbar kasa mai tasowa ta farko, kuma ta farko cikin kasashe masu karfin tattalin arziki da ta dauki irin wannan mataki.

 

Hakan da ta yi, ya sake bayyanawa duniya kyakkyawar niyyar kasar Sin ta ganin kasashe masu karancin kudin shiga sun samu damar fitar da kayayyakinsu zuwa kasarta domin cin gajiyar babbar kasuwarta tare da samun wadata da ci gaba. Har ila yau, ta sake tabbatar da manufarta ta sake fadada bude kofa ga kasashen waje domin su ci gajiyar gogewarta da ci gabanta.

 

Kamar yadda na saba fada, ci gaban kasar Sin ci gaba ne ga sauran kasashe ba kalubale ba. Kuma kasar ba ta kyashin ci gaban sauran kasashe, sabanin yadda wasu ke yi mata bita da kulli da kokarin ganin ta durkushe. Yayin da take samun ci gaba ta hanyar kirkire-kirkiren fasahohi da aiwatar da sabbin dabaru, kasashe masu son ci gaba da kaunar zaman lafiya, na iya hada gwiwa da ita domin raya kansu. Don haka duk mai son ganin durkushewar kasar Sin, to ba da ci gabanta kadai yake adawa ba, har da na kasashe masu tasowa da ma sauran kasashen duniya ba ki daya. (Fa’iza Muhammad Mustapha)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95
Daga Birnin Sin

Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

November 16, 2025
Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku
Daga Birnin Sin

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

November 16, 2025
Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

November 16, 2025
Next Post
Gwamnatin Za Ta Samar Wa Matasa Miliyan 20 Guraben Aiki A Ƙarkashin Shirin NIYEEDEP 

Gwamnatin Za Ta Samar Wa Matasa Miliyan 20 Guraben Aiki A Ƙarkashin Shirin NIYEEDEP 

LABARAI MASU NASABA

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

November 16, 2025
Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

November 16, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

November 16, 2025
Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

November 16, 2025
An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

November 16, 2025
Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

November 16, 2025
Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
DSS

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.