ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shawarar BRI Na Samar Da Wani Yanayi Mai Yakini Ga Tattalin Arzikin Duniya

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
BRI

Abokaina, ko kun taba kai ziyara a tashar jiragen ruwa ta Lekki dake Legas, Najeriya? Wata sabuwar tashar zamani ce, da Najeriya da Sin, da sauran bangarorin kasa da kasa, suka gina a hadin gwiwarsu, wadda ta kasance tashar jiragen ruwa mafi girma ta Najeriya. Ban da haka, bisa matsayinta na tasha mai kunshe da mafi yawan fasahohin zamani a yammacin Afirka, tashar jiragen ruwa ta Lekki na taka rawar gani a fagen zamanantarwa da ci gaban tattalin arzikin Najeriya, da na sauran kasashe makwabtanta. Sai dai idan an tantance dalilan da suka haifar da tashar, za a ga akwai tallafin da aka samu daga shawarar Ziri Daya da Hanya Daya (BRI) da kasar Sin ta kaddamar.

 

Akwai dimbin abokai da suka yi mana tambaya kan ma’anar taken shawarar “Ziri Daya da Hanya Daya”. Hakika wannan suna yana da alaka da muhimman tsoffin hanyoyin ciniki da suka hada kasar Sin da sauran kasashe a tarihi, wato Hanyar Siliki, da Hanyar Siliki dake Kan Teku. Dalilin da ya sa aka ba wata sabuwar shawara sunan wasu tsoffin hanyoyi, shi ne domin muhimmiyar rawar da tsoffin hanyoyin suka taka ta fuskar raya tattalin arzikin duniya, inda a maimakon dogaro kan karfin makamai, da kaddamar da yaki, aka yi amfani da ayarin rakuma, da jiragen ruwan dakon kaya, wajen karfafa cudanyar ciniki, da al’adu, tare da tabbatar da ci gaban tattalin arzikin kasashe daban daban.

ADVERTISEMENT
  • CMG Ya Gabatar Da Alamar Bayyana Kyakyyawar Fata Ta Sabuwar Shekara Bisa Kalandar Gargajiya Ta Kasar Sin

Shawarar BRI ta gaji ruhin tsoffin hanyoyin ciniki da aka kafa a tarihi, inda ta samar da damammaki na samun ci gaba ga duniya, abin da ya sa ta samun karbuwa sosai. Idan muka dauki nahiyar Afirka a matsayin misali, tun bayan da kasar Sin ta kaddamar da shawarar BRI a shekarar 2013, har zuwa yanzu, kasashe 52 dake nahiyar Afirka da kwamitin kungiyar kasashen Afirka ta AU, dukkansu sun kulla yarjeniyoyi na hadin gwiwa tare da kasar Sin, a karkashin shawarar. Ta haka, an samu dimbin sakamako masu gamsarwa, inda a fannin ciniki aka samu ci gaba sosai, ko a shekarar bara kadai ma, yawan cinikin da kasar Sin ta yi tare da kusan rabin kasashen dake nahiyar Afirka ya karu da fiye da kaso 10%. Bayan haka, kasar Sin ta zama kasar da ta zuba mafi yawan jari ga kasashen Afirka, kana a cikin shekaru 3 da suka wuce, kamfanoninta suka samar da guraben aikin yi fiye da miliyan 1 da dubu dari ga kasashen Afirka. Haka zalika, an gina dimbin kayayyakin more rayuwa a kasashen Afirka, bisa hadin gwiwa da kasar Sin.

 

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Sai dai ta yaya za a iya tabbatar da cewa, BRI za ta ci gaba da haifar da alfanu ga dukkan bangarori masu ruwa da tsaki? A jiya Litinin, an gudanar da taron karawa juna sani kan aikin aiwatar da BRI karo na 4 a birnin Beijing na kasar Sin, inda shugaban kasar Xi Jinping ya bayyana tsarin da za a bi wajen ci gaba da aiwatar da shawarar BRI a nan gaba. Cikin jawabinsa, ya yi bayanai masu muhimmanci, kamar su “kokarin gina al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai-daya” da “tsayawa kan manufar tattaunawa tare da kasashe daban daban, da yin aiki bisa hadin kai tare da su, gami da raba damar cin moriya tare da su”, da dai makamantansu. Abin lura shi ne, wannan taro na manyan jami’an kasar Sin ne, maimakon na kasa da kasa, don haka, maganar da shugaba Xi ya fada, ba da umarni ne ga jami’an Sin, maimaikon tallar wata manufar Sin ga kasashe daban daban. Amma duk da haka, shugaban na kasar Sin bai taba nuna son kai ba ko kadan. Kafin ya ambaci batun kare moriyar kasar Sin, ya jaddada bukatar samar da karin alfanu ga kasashen da suke cikin shawarar BRI.

 

A ganina, zamanin da muke ciki ya baiwa BRI karin muhimmanci. Saboda a halin yanzu, an fi nuna ra’ayi na son kai a duniyarmu, inda dimbin kasashe ke son daukar matakan radin kai, da bata huldar ciniki, da kin dunkulewar tattalin arzikin duniya. Sai dai duk da haka, BRI na ci gaba da samar da wani yanayi mai yakini a duniya, inda take kokarin tabbatar da samun zaman lafiya, da hadin kai, da kare moriyar bangarori daban daban, da neman samun ci gaba tare. (Bello Wang)

BRI
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
BRI
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa
  • Sulaiman
    Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

MASU ALAKA

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa
Daga Birnin Sin

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”
Daga Birnin Sin

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Next Post
Sin Ta Gabatarwa MDD Sanarwar Tabbatar Da Shatar Yankinta Na Teku a Tsibirin Huangyan Da Taswirarsa

Sin Ta Gabatarwa MDD Sanarwar Tabbatar Da Shatar Yankinta Na Teku a Tsibirin Huangyan Da Taswirarsa

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.