ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shawarar BRI Na Samar Da Wani Yanayi Mai Yakini Ga Tattalin Arzikin Duniya

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
BRI

Abokaina, ko kun taba kai ziyara a tashar jiragen ruwa ta Lekki dake Legas, Najeriya? Wata sabuwar tashar zamani ce, da Najeriya da Sin, da sauran bangarorin kasa da kasa, suka gina a hadin gwiwarsu, wadda ta kasance tashar jiragen ruwa mafi girma ta Najeriya. Ban da haka, bisa matsayinta na tasha mai kunshe da mafi yawan fasahohin zamani a yammacin Afirka, tashar jiragen ruwa ta Lekki na taka rawar gani a fagen zamanantarwa da ci gaban tattalin arzikin Najeriya, da na sauran kasashe makwabtanta. Sai dai idan an tantance dalilan da suka haifar da tashar, za a ga akwai tallafin da aka samu daga shawarar Ziri Daya da Hanya Daya (BRI) da kasar Sin ta kaddamar.

 

Akwai dimbin abokai da suka yi mana tambaya kan ma’anar taken shawarar “Ziri Daya da Hanya Daya”. Hakika wannan suna yana da alaka da muhimman tsoffin hanyoyin ciniki da suka hada kasar Sin da sauran kasashe a tarihi, wato Hanyar Siliki, da Hanyar Siliki dake Kan Teku. Dalilin da ya sa aka ba wata sabuwar shawara sunan wasu tsoffin hanyoyi, shi ne domin muhimmiyar rawar da tsoffin hanyoyin suka taka ta fuskar raya tattalin arzikin duniya, inda a maimakon dogaro kan karfin makamai, da kaddamar da yaki, aka yi amfani da ayarin rakuma, da jiragen ruwan dakon kaya, wajen karfafa cudanyar ciniki, da al’adu, tare da tabbatar da ci gaban tattalin arzikin kasashe daban daban.

ADVERTISEMENT
  • CMG Ya Gabatar Da Alamar Bayyana Kyakyyawar Fata Ta Sabuwar Shekara Bisa Kalandar Gargajiya Ta Kasar Sin

Shawarar BRI ta gaji ruhin tsoffin hanyoyin ciniki da aka kafa a tarihi, inda ta samar da damammaki na samun ci gaba ga duniya, abin da ya sa ta samun karbuwa sosai. Idan muka dauki nahiyar Afirka a matsayin misali, tun bayan da kasar Sin ta kaddamar da shawarar BRI a shekarar 2013, har zuwa yanzu, kasashe 52 dake nahiyar Afirka da kwamitin kungiyar kasashen Afirka ta AU, dukkansu sun kulla yarjeniyoyi na hadin gwiwa tare da kasar Sin, a karkashin shawarar. Ta haka, an samu dimbin sakamako masu gamsarwa, inda a fannin ciniki aka samu ci gaba sosai, ko a shekarar bara kadai ma, yawan cinikin da kasar Sin ta yi tare da kusan rabin kasashen dake nahiyar Afirka ya karu da fiye da kaso 10%. Bayan haka, kasar Sin ta zama kasar da ta zuba mafi yawan jari ga kasashen Afirka, kana a cikin shekaru 3 da suka wuce, kamfanoninta suka samar da guraben aikin yi fiye da miliyan 1 da dubu dari ga kasashen Afirka. Haka zalika, an gina dimbin kayayyakin more rayuwa a kasashen Afirka, bisa hadin gwiwa da kasar Sin.

 

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Sai dai ta yaya za a iya tabbatar da cewa, BRI za ta ci gaba da haifar da alfanu ga dukkan bangarori masu ruwa da tsaki? A jiya Litinin, an gudanar da taron karawa juna sani kan aikin aiwatar da BRI karo na 4 a birnin Beijing na kasar Sin, inda shugaban kasar Xi Jinping ya bayyana tsarin da za a bi wajen ci gaba da aiwatar da shawarar BRI a nan gaba. Cikin jawabinsa, ya yi bayanai masu muhimmanci, kamar su “kokarin gina al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai-daya” da “tsayawa kan manufar tattaunawa tare da kasashe daban daban, da yin aiki bisa hadin kai tare da su, gami da raba damar cin moriya tare da su”, da dai makamantansu. Abin lura shi ne, wannan taro na manyan jami’an kasar Sin ne, maimakon na kasa da kasa, don haka, maganar da shugaba Xi ya fada, ba da umarni ne ga jami’an Sin, maimaikon tallar wata manufar Sin ga kasashe daban daban. Amma duk da haka, shugaban na kasar Sin bai taba nuna son kai ba ko kadan. Kafin ya ambaci batun kare moriyar kasar Sin, ya jaddada bukatar samar da karin alfanu ga kasashen da suke cikin shawarar BRI.

 

A ganina, zamanin da muke ciki ya baiwa BRI karin muhimmanci. Saboda a halin yanzu, an fi nuna ra’ayi na son kai a duniyarmu, inda dimbin kasashe ke son daukar matakan radin kai, da bata huldar ciniki, da kin dunkulewar tattalin arzikin duniya. Sai dai duk da haka, BRI na ci gaba da samar da wani yanayi mai yakini a duniya, inda take kokarin tabbatar da samun zaman lafiya, da hadin kai, da kare moriyar bangarori daban daban, da neman samun ci gaba tare. (Bello Wang)

BRI
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya
BRI
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

MASU ALAKA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Daga Birnin Sin

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
Daga Birnin Sin

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
Daga Birnin Sin

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Next Post
Sin Ta Gabatarwa MDD Sanarwar Tabbatar Da Shatar Yankinta Na Teku a Tsibirin Huangyan Da Taswirarsa

Sin Ta Gabatarwa MDD Sanarwar Tabbatar Da Shatar Yankinta Na Teku a Tsibirin Huangyan Da Taswirarsa

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.