Wata babbar mota ɗauke da yashi ta yi hatsari a kasuwar Mile 6 da ke Jalingo, jihar Taraba a ranar Asabar, inda ta yi sanadin mutuwar mutane da dama.
Majiyar tsaro Zagazola Makama ta bayyana cewa: “Hatsarin ya yi mummunan ɓarna, jama’a da dama sun jikkata yayin da wasu suka rasu.”
An bayyana cewa motar ta kufce ne sannan ya taya ta fashe, wanda hakan ya sa direba ya rasa iko da ita.
“Motar ta afko cikin kasuwar ba zato ba tsammani ta tattake mutane,” in ji wani ɗan kasuwa mai suna Musa Ibrahim.
Jami’an tsaro sun kama direban yayin da ake ci gaba da bincike.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp